ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Ake Rubibin Wike A Siyasar Nijeriya?

by Yusuf Shuaibu
4 years ago
Wike

Tun bayan kammala zaben fitar da gwani na takarar shugaban kasa a karkashin jam’iyyar PDP ake ta samun zaman doya da manja a tsakanin ‘ya’yan jam’iyyar PDP.

Wani sabon rikici ya kunno kai a kan zabin dan takarar mataimakin shugaban kasa a Jam’iyyar PDP.

  • Bincikenmu: An Dade Da Hana Karuwanci A Neja, Amma Abin Ya Dau Sabon Salo
  • Da Hannun Amurka A Kuskuren Kai Harin Sojin Nijeriya Na 2017 A Borno — Bincike

Akwai rahotanni da suke cewa Gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Wike, yana barazanar ficewa daga PDP bayan da Atiku Abubakar ya zabi Gwamnan Jihar Delta, Ifeanyi Okowa, a matsayin abokin takararsa a zaben shugaban kasa na 2023.

ADVERTISEMENT

Wadannan rahotannin ne ya sanya wasu ke ta kamun kafa a wajen Wike idan ya bar jam’iyyar PDP ya shiga jam’iyyarsu ganin irin tasirin da yake da shi a yankin kudu maso kudancin Nijeriya.

Wasu fitattu manyan jam’iyyar PDP sun fito suna kokarin cire wa dan takarar shugaban kasar zani a kasuwa, inda suke cewa bai kyauta ba da ya tsallake gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Wike, wajen zaben abokin takarasa, alama ce ta yankan shakku cewa za su kunna wata wutar rikici, wadda idan ba a yi wa tubkar-hanci ba za ta cinye jam’iyyar.

LABARAI MASU NASABA

2027: Magoya Bayan Tinubu Sun Yi Watsi Da Sukar Takarar Musulmi-Musulmi Da Kwankwaso Ya Yi

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

A nasa bangaren, Gwamnan Jihar Benuwe, Samuel Ortom, a wata zantawa da ‘yan jarida ya ce sam-sam dan takarar shugaban kasar a karkashin jam’iyyar PDP, Atiku Ababukar, bai yi halacci ba da ya ki amincewa da Gwamna Wike a matsayin mataimakisa.

A hannu guda kuwa, wasu ‘yan takarar shugaban kasa da kusoshin wasu jam’iyyun hamayyar ke tururu zuwa wajen Wike, kuma ga dukkan alamu da nufin yin wuf da shi daga jam’iyyar PDP.

A kwanakin nan an ga dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP, Peter Obi ya kai wa Mista Wike ziyara.

An ga kuma dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya ziyarci gwamnann Ribas.

Haka kuma wasu gwamnonin APC sun gana da Wike.

Kafafen yada labarai dai da dama sun ruwaito cewa cikin gwamnonin sun hada da gwamnan Jihar Ekiti kuma shugaban kungiyar gwamnoni, Dakta Kayode Fayemi tare da gwamnan Legas da kuma na Ondo.

Sai dai babu wani abu da ya fito na dalili da kuma sakamakon tattaunawar tsakanin Wike da gwamnonin na APC, amma ba ya rasa nasaba da zaben 2023.

Baya ga wannan kuma, sai ga ‘yan tawayen APC wato su Yakubu Dogara da Tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Babachir Lawal sun kai wa Wike ziyara jim kadan bayan dawowarsa daga bulaguro a kasar waje.

Har Yakubu Dogara yake cewa Nijeriya na bukatar mutane irin su Wike don a gyarata.

A ranar Lahadi, 31 ga watan Yulin 2022, gwamnonin PDP sun kai wa Wike ziyara. Gwamnonin sun kai ziyarar ce kwana daya bayan da manyan ‘yan tawayen APC, suka Kai masa ziyara.

Gwamnonin da suka kai wa Wike ziyara, sun je ne tare da wasu tsoffin gwamnonin PDP, inda a ranar Lahadi suka gana da shi a asirce, a gidan Gwamnatin Jihar Ribas da ke Asokoro cikin garin Abuja.

Ba a san dai abin da suka tattauna ba. Amma kuma tabbas tattaunawar ba ta rasa nasaba da sabanin da ke kara tsanani tsakanin Wike da Atiku Abubakar.

Daga baya Wike ya ce Atiku ya yaudare shi, domin bayan kammala zaben, ya bi Wike har gida ya ba shi hakuri. Kuma ya ce shi zai dauka mataimakin takararsa.

Manyan PDP sun fara jin tsoron Wike tun bayan da gwamnonin APC uku daga kudu maso yamma suka kai masa ziyara.

Sai kuma ziyarar da Yakubu Dogara da Babachir Lawal suka kai masa a ranar Asabar.

Rahotanni dai da dama na nuna cewa Wike dai na cewa ba zai fita daga PDP ba, shi da jam’iyyar mutu-ka-raba.

Amma abun tambaya a nan wani irin tasiri Wike yake da shi haka har zama tamkar gwal?

Lallai wannan tambaya tana da amsa, idann aka duba irin tasirin da yake da shi a cikin harkokin siyasar Jihar Ribas da ma Nijeriya gaba daya za a ga cewa rasa irin Wike a cikin jam’iyya babban nakasu ne, domin yana da dimbin magoya baya, sannan yana iya amfani da kudinsa wajen gina jam’iyya da samun nasara a cikin siyasa.

Ya kasance wani bango da ake kallo a cikin harkokin siyasan kudancin Nijeriya da ke da tasiri wajen tsayawa kan akidarsa, wanda yake da wahalar taukwaruwa.

Tabbas Wike yana da matukar tasiri a cikin harkokin siyasar Nijeriya, musamman ma a cikin jam’iyyarsa ta PDP.

Wike
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Manufofin Tattalin Arzikin Gwamnatin Tinubu Sun Lalata Rayukan Al’ummar Nijeriya —ADC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

MASU ALAKA

Kwankwaso Zai Koma ADC Ranar Litinin
Manyan Labarai

2027: Magoya Bayan Tinubu Sun Yi Watsi Da Sukar Takarar Musulmi-Musulmi Da Kwankwaso Ya Yi

July 22, 2026
Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC
Labarai

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

July 21, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Siyasa

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Next Post
Atiku Ya Nada Dino Melaye Da Daniel Bwala A Matsayin Masu Magana da Yawunsa

2023: Wata Kungiya Zata Yi Gangamin Tara Wa Atiku Gudunmawar Biliyan 1 Na Kamfen

LABARAI MASU NASABA

Dauda Dauda Lawal Ya Sha Alwashin Farfaɗo Da Masana’antar Yadi Ta Zamfara

Dauda Dauda Lawal Ya Sha Alwashin Farfaɗo Da Masana’antar Yadi Ta Zamfara

July 26, 2026
Gwamna Uba Sani Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Kyauta Ga Manoma 150,000  A Kaduna

Gwamna Uba Sani Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Kyauta Ga Manoma 150,000 A Kaduna

July 26, 2026
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Birtaniya Ta Yaba Wa Tinubu Kan Sauye-sauyen Tattalin Arziki

July 25, 2026
Ofishin Jakadancin Sin A Nijeriya Ya Shirya Taron Murnar Cika Shekaru 99 Da Kafuwar Rundunar PLA Ta Sin

Ofishin Jakadancin Sin A Nijeriya Ya Shirya Taron Murnar Cika Shekaru 99 Da Kafuwar Rundunar PLA Ta Sin

July 25, 2026
Sabon Rahoton Bankin Duniya Ya Yaba Da Yadda Tattalin Arzkin Nijeriya Ke Bunkasa

Sabon Rahoton Bankin Duniya Ya Yaba Da Yadda Tattalin Arzkin Nijeriya Ke Bunkasa

July 25, 2026
Farfesa Dr. Otto Heinrich Herzog: Sin Tana Da Tsari Mai Kyau Na Aiwatar Da Dabarun Ci Gaba

Farfesa Dr. Otto Heinrich Herzog: Sin Tana Da Tsari Mai Kyau Na Aiwatar Da Dabarun Ci Gaba

July 25, 2026
Yadda Ake Faten Dankalin Turawa Da Kaza

Yadda Ake Faten Dankalin Turawa Da Kaza

July 25, 2026
An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Yiwu Ta Duniya –Yadda Xi Jinping Ke Kulawa Da Jagorantar Ci Gaban Yiwu”

An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Yiwu Ta Duniya –Yadda Xi Jinping Ke Kulawa Da Jagorantar Ci Gaban Yiwu”

July 25, 2026
Baya Ga “Sanyi Irin Na Sin”, Akwai Wasu Abubuwa Da Yawa Da Masu Yawon Bude Ido Na Turai Ke Sha’awa Kan Kasar

Baya Ga “Sanyi Irin Na Sin”, Akwai Wasu Abubuwa Da Yawa Da Masu Yawon Bude Ido Na Turai Ke Sha’awa Kan Kasar

July 25, 2026
Rodri Ya Amince da Tayin Komawa Real Madrid

Rodri Ya Amince da Tayin Komawa Real Madrid

July 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.