ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Ake Rubibin Wike A Siyasar Nijeriya?

by Yusuf Shuaibu
4 years ago
Wike

Tun bayan kammala zaben fitar da gwani na takarar shugaban kasa a karkashin jam’iyyar PDP ake ta samun zaman doya da manja a tsakanin ‘ya’yan jam’iyyar PDP.

Wani sabon rikici ya kunno kai a kan zabin dan takarar mataimakin shugaban kasa a Jam’iyyar PDP.

  • Bincikenmu: An Dade Da Hana Karuwanci A Neja, Amma Abin Ya Dau Sabon Salo
  • Da Hannun Amurka A Kuskuren Kai Harin Sojin Nijeriya Na 2017 A Borno — Bincike

Akwai rahotanni da suke cewa Gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Wike, yana barazanar ficewa daga PDP bayan da Atiku Abubakar ya zabi Gwamnan Jihar Delta, Ifeanyi Okowa, a matsayin abokin takararsa a zaben shugaban kasa na 2023.

ADVERTISEMENT

Wadannan rahotannin ne ya sanya wasu ke ta kamun kafa a wajen Wike idan ya bar jam’iyyar PDP ya shiga jam’iyyarsu ganin irin tasirin da yake da shi a yankin kudu maso kudancin Nijeriya.

Wasu fitattu manyan jam’iyyar PDP sun fito suna kokarin cire wa dan takarar shugaban kasar zani a kasuwa, inda suke cewa bai kyauta ba da ya tsallake gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Wike, wajen zaben abokin takarasa, alama ce ta yankan shakku cewa za su kunna wata wutar rikici, wadda idan ba a yi wa tubkar-hanci ba za ta cinye jam’iyyar.

LABARAI MASU NASABA

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

A nasa bangaren, Gwamnan Jihar Benuwe, Samuel Ortom, a wata zantawa da ‘yan jarida ya ce sam-sam dan takarar shugaban kasar a karkashin jam’iyyar PDP, Atiku Ababukar, bai yi halacci ba da ya ki amincewa da Gwamna Wike a matsayin mataimakisa.

A hannu guda kuwa, wasu ‘yan takarar shugaban kasa da kusoshin wasu jam’iyyun hamayyar ke tururu zuwa wajen Wike, kuma ga dukkan alamu da nufin yin wuf da shi daga jam’iyyar PDP.

A kwanakin nan an ga dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP, Peter Obi ya kai wa Mista Wike ziyara.

An ga kuma dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya ziyarci gwamnann Ribas.

Haka kuma wasu gwamnonin APC sun gana da Wike.

Kafafen yada labarai dai da dama sun ruwaito cewa cikin gwamnonin sun hada da gwamnan Jihar Ekiti kuma shugaban kungiyar gwamnoni, Dakta Kayode Fayemi tare da gwamnan Legas da kuma na Ondo.

Sai dai babu wani abu da ya fito na dalili da kuma sakamakon tattaunawar tsakanin Wike da gwamnonin na APC, amma ba ya rasa nasaba da zaben 2023.

Baya ga wannan kuma, sai ga ‘yan tawayen APC wato su Yakubu Dogara da Tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Babachir Lawal sun kai wa Wike ziyara jim kadan bayan dawowarsa daga bulaguro a kasar waje.

Har Yakubu Dogara yake cewa Nijeriya na bukatar mutane irin su Wike don a gyarata.

A ranar Lahadi, 31 ga watan Yulin 2022, gwamnonin PDP sun kai wa Wike ziyara. Gwamnonin sun kai ziyarar ce kwana daya bayan da manyan ‘yan tawayen APC, suka Kai masa ziyara.

Gwamnonin da suka kai wa Wike ziyara, sun je ne tare da wasu tsoffin gwamnonin PDP, inda a ranar Lahadi suka gana da shi a asirce, a gidan Gwamnatin Jihar Ribas da ke Asokoro cikin garin Abuja.

Ba a san dai abin da suka tattauna ba. Amma kuma tabbas tattaunawar ba ta rasa nasaba da sabanin da ke kara tsanani tsakanin Wike da Atiku Abubakar.

Daga baya Wike ya ce Atiku ya yaudare shi, domin bayan kammala zaben, ya bi Wike har gida ya ba shi hakuri. Kuma ya ce shi zai dauka mataimakin takararsa.

Manyan PDP sun fara jin tsoron Wike tun bayan da gwamnonin APC uku daga kudu maso yamma suka kai masa ziyara.

Sai kuma ziyarar da Yakubu Dogara da Babachir Lawal suka kai masa a ranar Asabar.

Rahotanni dai da dama na nuna cewa Wike dai na cewa ba zai fita daga PDP ba, shi da jam’iyyar mutu-ka-raba.

Amma abun tambaya a nan wani irin tasiri Wike yake da shi haka har zama tamkar gwal?

Lallai wannan tambaya tana da amsa, idann aka duba irin tasirin da yake da shi a cikin harkokin siyasar Jihar Ribas da ma Nijeriya gaba daya za a ga cewa rasa irin Wike a cikin jam’iyya babban nakasu ne, domin yana da dimbin magoya baya, sannan yana iya amfani da kudinsa wajen gina jam’iyya da samun nasara a cikin siyasa.

Ya kasance wani bango da ake kallo a cikin harkokin siyasan kudancin Nijeriya da ke da tasiri wajen tsayawa kan akidarsa, wanda yake da wahalar taukwaruwa.

Tabbas Wike yana da matukar tasiri a cikin harkokin siyasar Nijeriya, musamman ma a cikin jam’iyyarsa ta PDP.

Wike
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu
Siyasa

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano
Siyasa

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa
Siyasa

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

June 22, 2026
Next Post
Atiku Ya Nada Dino Melaye Da Daniel Bwala A Matsayin Masu Magana da Yawunsa

2023: Wata Kungiya Zata Yi Gangamin Tara Wa Atiku Gudunmawar Biliyan 1 Na Kamfen

LABARAI MASU NASABA

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

June 25, 2026
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

June 25, 2026
Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.