ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bincikenmu: An Dade Da Hana Karuwanci A Neja, Amma Abin Ya Dau Sabon Salo

by Muhammad Awwal Umar
4 years ago
Karuwanci

Karuwanci na daya daga gurbatattun dabi’un da gwamnatin Neja ta haramta tun zuwan shari’ar musulunci lokacin gwamnatin Marigayi Injiniya Abdulkadir Kure, wanda ya kai gwamnatin wancan lokacin ta samar da hukuma ta musamman da za ta kula da harkokin addinin musulunci a karkashin hukuma mai kula da shari’a.

Babban aikin hukumar a lokacin shi ne, sulhu tsakanin ma’aurata, rabon gado da kulawa wajen bin dokokin shari’ar musulunci, musamman wajen tabbatar da hana shan giya da sayar da ita a bainar jama’a tare da rufe gidajen karuwai da wuraren ‘yan caca.

  • Gwamnatin Gombe Ta Kafa Kwamitin Sayarwa Da Raba Takin Zamani Don Saukaka Wa Manoma 
  • Ma’aikatar Tsaron Sin Ta Yi Bayani Game Da Matakan Soji Da Kasar Ta Dauka

Hukumar ta yi suna wajen aiki da jajirtattun rudunar HISBA, wanda suke aiki ba dare ba rana kamar yadda majalisar dokokin jihar ta tanada, wanda dokar kasa ta ba ta dama. Ko a wancan lokacin ana karuwanci amma a fakaice, dalilin tarwatsewar karuwan zuwa gidajen haya, inda suke haduwa da abokan huldarsu a wasu kebabbun wurare ba tare sanin gwamnati ba.

ADVERTISEMENT

Bayan wucewar gwamnatin, Injiya Abdulkadir Kure, gwamnatin Dakta Mu’azu Babangida Aliyu ta jaddada dokar hana karuwanci a jihar, amma sakamakon rashin bai wa hukumar goyon bayan da ta dace, ayyukan yaki da karuwancin ya yi sanyi, inda mafiwan karuwa suka ci gaba da tallata kawunansu a wasu manyan hanyoyi, musamman da yamma dan masu wucewa su rika daukarsu zuwa mafi akasari masaukan baki da wuraren hutuwa ba tare da an sanya masu idanu ba.

Wani lokacin kuma wasu kan labe da zawarci suna yawo a ma’aikatun gwamnati, inda su kan ziyarci wasu manyan ma’aikata da suka taka rawa a lokacin yakin neman zabe tare da ‘yan siyasa.

LABARAI MASU NASABA

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

Gwamnatin Ma’azu Aliyu duk da ba ta ba da damar ci gaba da sakar wa karuwai mara ba, amma ba ta tsanantawa kamar lokacin gwamnatin da ta gada ba, hakan kuma bai ba da damar bude gidajen karuwai ba.

Bayan tafiyar gwamnatin Dakta Mu’azu Aliyu, gwamnatin Alhaji Abubakar Sani Bello ba ta halasta karuwancin ba, amma kuma ita din ma ba ta yi abin da ya dace wajen karfafa gwiwar hukumar ba, kasancewar ma’aikatan Hisbar ba su samu kulawar da ta dace domin ci gaba da ayyukansu.

Kasancewar hukumar shari’ar tana da bangarori da dama da suka shafi bangaren shari’a mai kula da sulhunta ma’aurata, rabon gado da bangaren yaki da giya, ya sa kusan aikin fataucin karuwan ya koma hadin gwiwa tsakanin bangaren hana sha da sayar da giya da bangaren Hisba. ‘Yan Hisban na samun damar gudanar da aikin ne da tallafin bangaren yaki da sayar da giya.

A lokata da dama bangaren ne ke taimaka wa ‘yan Hisban idan za su fita gudanar da samame.

Domin bincike ya nuna kusan duk wuraren da ake sayar da kayan barasar matan masu zamansu suna yin tururuwa a wajen, wani lokacin ma har zawara da ‘yan mata kan fake a ire-iren wadannan wuraren.

Jami’an Hisbar idan sun samu nasarar kamensu kan bai wa ‘yan sanda ne domin mika su gaban alkala. Hakan bai sanya karuwan fakewa a inda suke tsammanin gwamnatin ba ta ganin su wajen ci gaba da mummunar sana’arsu.

Binciken wakilinmu ya gano cewa har yanzu karuwan kan tsaya gefen shataletalen Sabuwar Sakatariya kusa da kofar shiga garin Minna, wasu kuma kan koma hanyar bayan gari da ya tashi daga gidajen ‘yan majalisar dokokin jiha zuwa Mararrabar masaukin baki na Aloe-bera, kasancewar akwai sabbin masaukin baki a bangaren.

Wata da ta nemi a sakaya sunanta ta ce karuwancin kama daki tsohon yayi ne, domin a kan shirya da wasu manajojin masaukan baki ta hanyar ba su lambar waya, duk wanda ya samo abokin hulda yana da kaso na abin da za a biya kafin a yi zina da su.

Wani jami’in hukumar shari’a da ya nemi a sakaya sunansa, ya ce jami’an Hisbar ba cikakkun ma’aikata ba ne, ana biyan su alawus ne idan an dawo aiki, amma yanzu kusan shekaru uku kenan gwamnatin jiha ta kasa bai wa hukumar shari’a kudaden gudanar da aiki balle a samu damar gudanar da aikin yadda ya dace.

Ya ce, “Ina da tabbacin kwarewa a aikin nan, da gwamnatin jiha za ta sakar mana mara yadda ya dace ta hanyar ba mu kudaden aiki, duk wani salon karuwan nan da mun dakile shi, amma maganar kafa doka kan hana karuwanci a kan dalilan tsaro na nan daram tun ma kafin mu samu kanmu a wannan annobar ta rashin tsaro a wannan jihar.

“Kudin da ake ba mu a wannan bangaren da ya shafi biyan alawus na ‘yan Hisba da kudaden gudanar da aikin kamen a wata bai wuce dubu dari takwas zuwa miliyan daya ba, amma yanzu mun kai kusan shekaru uku gwamnati ba ta ba mu ba, kuma ba mu da wata hanyar samun kudin shiga da zai ba mu damar rike ‘yan Hisba dan gudanar da aikin.”

Koma dai mene ne, binciken da Jaridar LEADERSHIP Hausa ta gudanar kan karuwanci a Jihar Neja, ta gano cewa masu mummunar sana’ar suna amfani da wasu dubaru da salo ta hanyar fakewa da sunan neman abinci a dalilin rashin aiki da talauci.

A wasu lokutan ma har da matan auren da ke fakar idanun mazajensu, suna zuwa otel a tsakanin sallar Magriba zuwa Isha’i, wasu bayan isha’i zuwa karfe goma na dare bisa farashi dan kadan domin samun abin sanyawa aljihu.

Karuwanci
Muhammad Awwal Umar
+ postsBio
  • Muhammad Awwal Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-awwal-umar/
    Yadda Mayar Da Gonaki Fulotai Ke Tsananta Karancin Abinci
  • Muhammad Awwal Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-awwal-umar/
    Gwamnatoci Sun Fara Daukar Matakan Dakile Yunwa
  • Muhammad Awwal Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-awwal-umar/
    Neja Za Ta Gyara Makarantun Rugagen Fulani
  • Muhammad Awwal Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-awwal-umar/
    Ba Mu Hana Sulhu Da ‘Yan Ta’adda Ba, Amma A Bar Jami’an Tsaro Su Yi Aikinsu – Bosso

MASU ALAKA

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya
Rahotonni

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Rahotonni

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

July 11, 2026
Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

June 26, 2026
Next Post
Jihar Nasarawa Ta Fadakar Da Al’ummarta A Kan Cutar Hanta

Jihar Nasarawa Ta Fadakar Da Al’ummarta A Kan Cutar Hanta

LABARAI MASU NASABA

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.