ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bincikenmu: An Dade Da Hana Karuwanci A Neja, Amma Abin Ya Dau Sabon Salo

by Muhammad Awwal Umar
4 years ago
Karuwanci

Karuwanci na daya daga gurbatattun dabi’un da gwamnatin Neja ta haramta tun zuwan shari’ar musulunci lokacin gwamnatin Marigayi Injiniya Abdulkadir Kure, wanda ya kai gwamnatin wancan lokacin ta samar da hukuma ta musamman da za ta kula da harkokin addinin musulunci a karkashin hukuma mai kula da shari’a.

Babban aikin hukumar a lokacin shi ne, sulhu tsakanin ma’aurata, rabon gado da kulawa wajen bin dokokin shari’ar musulunci, musamman wajen tabbatar da hana shan giya da sayar da ita a bainar jama’a tare da rufe gidajen karuwai da wuraren ‘yan caca.

  • Gwamnatin Gombe Ta Kafa Kwamitin Sayarwa Da Raba Takin Zamani Don Saukaka Wa Manoma 
  • Ma’aikatar Tsaron Sin Ta Yi Bayani Game Da Matakan Soji Da Kasar Ta Dauka

Hukumar ta yi suna wajen aiki da jajirtattun rudunar HISBA, wanda suke aiki ba dare ba rana kamar yadda majalisar dokokin jihar ta tanada, wanda dokar kasa ta ba ta dama. Ko a wancan lokacin ana karuwanci amma a fakaice, dalilin tarwatsewar karuwan zuwa gidajen haya, inda suke haduwa da abokan huldarsu a wasu kebabbun wurare ba tare sanin gwamnati ba.

ADVERTISEMENT

Bayan wucewar gwamnatin, Injiya Abdulkadir Kure, gwamnatin Dakta Mu’azu Babangida Aliyu ta jaddada dokar hana karuwanci a jihar, amma sakamakon rashin bai wa hukumar goyon bayan da ta dace, ayyukan yaki da karuwancin ya yi sanyi, inda mafiwan karuwa suka ci gaba da tallata kawunansu a wasu manyan hanyoyi, musamman da yamma dan masu wucewa su rika daukarsu zuwa mafi akasari masaukan baki da wuraren hutuwa ba tare da an sanya masu idanu ba.

Wani lokacin kuma wasu kan labe da zawarci suna yawo a ma’aikatun gwamnati, inda su kan ziyarci wasu manyan ma’aikata da suka taka rawa a lokacin yakin neman zabe tare da ‘yan siyasa.

LABARAI MASU NASABA

Ko Yakin Iran Zai Kawo Karshen Kawancen Amurka Da Kasashen Larabawa?

Yadda Sauya Shekar ‘Yan Siyasa Ta Sauya Fasalin Majalisar Dokokin Kasa

Gwamnatin Ma’azu Aliyu duk da ba ta ba da damar ci gaba da sakar wa karuwai mara ba, amma ba ta tsanantawa kamar lokacin gwamnatin da ta gada ba, hakan kuma bai ba da damar bude gidajen karuwai ba.

Bayan tafiyar gwamnatin Dakta Mu’azu Aliyu, gwamnatin Alhaji Abubakar Sani Bello ba ta halasta karuwancin ba, amma kuma ita din ma ba ta yi abin da ya dace wajen karfafa gwiwar hukumar ba, kasancewar ma’aikatan Hisbar ba su samu kulawar da ta dace domin ci gaba da ayyukansu.

Kasancewar hukumar shari’ar tana da bangarori da dama da suka shafi bangaren shari’a mai kula da sulhunta ma’aurata, rabon gado da bangaren yaki da giya, ya sa kusan aikin fataucin karuwan ya koma hadin gwiwa tsakanin bangaren hana sha da sayar da giya da bangaren Hisba. ‘Yan Hisban na samun damar gudanar da aikin ne da tallafin bangaren yaki da sayar da giya.

A lokata da dama bangaren ne ke taimaka wa ‘yan Hisban idan za su fita gudanar da samame.

Domin bincike ya nuna kusan duk wuraren da ake sayar da kayan barasar matan masu zamansu suna yin tururuwa a wajen, wani lokacin ma har zawara da ‘yan mata kan fake a ire-iren wadannan wuraren.

Jami’an Hisbar idan sun samu nasarar kamensu kan bai wa ‘yan sanda ne domin mika su gaban alkala. Hakan bai sanya karuwan fakewa a inda suke tsammanin gwamnatin ba ta ganin su wajen ci gaba da mummunar sana’arsu.

Binciken wakilinmu ya gano cewa har yanzu karuwan kan tsaya gefen shataletalen Sabuwar Sakatariya kusa da kofar shiga garin Minna, wasu kuma kan koma hanyar bayan gari da ya tashi daga gidajen ‘yan majalisar dokokin jiha zuwa Mararrabar masaukin baki na Aloe-bera, kasancewar akwai sabbin masaukin baki a bangaren.

Wata da ta nemi a sakaya sunanta ta ce karuwancin kama daki tsohon yayi ne, domin a kan shirya da wasu manajojin masaukan baki ta hanyar ba su lambar waya, duk wanda ya samo abokin hulda yana da kaso na abin da za a biya kafin a yi zina da su.

Wani jami’in hukumar shari’a da ya nemi a sakaya sunansa, ya ce jami’an Hisbar ba cikakkun ma’aikata ba ne, ana biyan su alawus ne idan an dawo aiki, amma yanzu kusan shekaru uku kenan gwamnatin jiha ta kasa bai wa hukumar shari’a kudaden gudanar da aiki balle a samu damar gudanar da aikin yadda ya dace.

Ya ce, “Ina da tabbacin kwarewa a aikin nan, da gwamnatin jiha za ta sakar mana mara yadda ya dace ta hanyar ba mu kudaden aiki, duk wani salon karuwan nan da mun dakile shi, amma maganar kafa doka kan hana karuwanci a kan dalilan tsaro na nan daram tun ma kafin mu samu kanmu a wannan annobar ta rashin tsaro a wannan jihar.

“Kudin da ake ba mu a wannan bangaren da ya shafi biyan alawus na ‘yan Hisba da kudaden gudanar da aikin kamen a wata bai wuce dubu dari takwas zuwa miliyan daya ba, amma yanzu mun kai kusan shekaru uku gwamnati ba ta ba mu ba, kuma ba mu da wata hanyar samun kudin shiga da zai ba mu damar rike ‘yan Hisba dan gudanar da aikin.”

Koma dai mene ne, binciken da Jaridar LEADERSHIP Hausa ta gudanar kan karuwanci a Jihar Neja, ta gano cewa masu mummunar sana’ar suna amfani da wasu dubaru da salo ta hanyar fakewa da sunan neman abinci a dalilin rashin aiki da talauci.

A wasu lokutan ma har da matan auren da ke fakar idanun mazajensu, suna zuwa otel a tsakanin sallar Magriba zuwa Isha’i, wasu bayan isha’i zuwa karfe goma na dare bisa farashi dan kadan domin samun abin sanyawa aljihu.

Karuwanci
Muhammad Awwal Umar
+ postsBio
  • Muhammad Awwal Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-awwal-umar/
    Yadda Mayar Da Gonaki Fulotai Ke Tsananta Karancin Abinci
  • Muhammad Awwal Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-awwal-umar/
    Gwamnatoci Sun Fara Daukar Matakan Dakile Yunwa
  • Muhammad Awwal Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-awwal-umar/
    Neja Za Ta Gyara Makarantun Rugagen Fulani
  • Muhammad Awwal Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-awwal-umar/
    Ba Mu Hana Sulhu Da ‘Yan Ta’adda Ba, Amma A Bar Jami’an Tsaro Su Yi Aikinsu – Bosso

MASU ALAKA

Karuwanci
Rahotonni

Ko Yakin Iran Zai Kawo Karshen Kawancen Amurka Da Kasashen Larabawa?

May 17, 2026
Karuwanci
Rahotonni

Yadda Sauya Shekar ‘Yan Siyasa Ta Sauya Fasalin Majalisar Dokokin Kasa

May 16, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Rahotonni

Almajiranci:Matsala Ko Maslaha

May 10, 2026
Next Post
Jihar Nasarawa Ta Fadakar Da Al’ummarta A Kan Cutar Hanta

Jihar Nasarawa Ta Fadakar Da Al’ummarta A Kan Cutar Hanta

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.