• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Amurka Ta Sake Komawa UNESCO Bayan Da Ta Sha Ficewa Daga Hukumar?

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Me Ya Sa Amurka Ta Sake Komawa UNESCO Bayan Da Ta Sha Ficewa Daga Hukumar?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Amurka za ta sake komawa hukumar kula da ilmi da kimiyya da al’adu ta MDD, wato UNESCO a takaice. 

A ranar 30 ga watan Yuni, an zartas da wani daftarin kuduri yayin taron musamman na babban taron UNESCO, inda aka amince da maido da kujerar kasar Amurka a hukumar tun daga watan Yulin da ake ciki daga dukkanin fannoni. Hakan nan ya zama karo na uku da Amurka za ta kasance mamban hukumar, wato bayan da ta fice daga hukumar a shekarar 1984 da ta 2018.

  • Sin: Ya Dace Amurka Ta Ingiza Hada Kan UNESCO Bayan Dawowarta Hukumar

Amma me ya sa Amurka ta sake komawa hukumar? Me ya sa kuma ta sha komawa bayan ficewa?

Wata kila muna iya gano amsar tambayar daga jawabin da mataimakin sakataren harkokin wajen kasar John Bass ya yi, a gun taron manema labarai da ma’aikatar harkokin wajen kasar ta gudanar a watan Maris da ya gabata, inda ya ce, a ganin gwamnatin kasar Amurka, komawa hukumar UNESCO zai taimakawa Amurka wajen takarar da take yi da kasar Sin a duniya.

A hakika, a cikin ’yan shekarun baya, Amurka ta sha ficewa da kuma komawa hukumomi, da yarjejeniyoyi na kasa da kasa. Idan ba a manta ba, baya ga UNESCO, Amurka ta kuma fice daga yarjejeniyar Paris, da yarjejeniyar bakin haure ta duniya, da yarjejeniyar nukiliya ta Iran, da majalisar hakkin dan Adam ta MDD, da hukumar lafiya ta duniya da dai sauransu.

Labarai Masu Nasaba

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

In dai mun yi nazari a kan dalilin ficewarta da komarta kuma, za mu gano cewa, kullum tana neman kujera a kungiyoyin duniya ne don biyan bukatunta, amma idan ba ta cimma buri ba sa ta fice. Lallai, don cimma moriyarta, da ma kiyaye babakeren da ta kafa ne take shiga kungiyoyin duniya.

Sai dai kuma neman wakilci a kungiyoyin duniya ba wasa ba ne, kuma bai kamata a mai da shi a matsayin dabarar yin takara da wasu don cimma burin siyasa ba.

Idan dai da sahihiyar zuci ne Amurka ke son komawa a wannan karo, to, ya kamata ta sauke nauyin da ke wuyanta, ta biya kudin karo-karo na hukumar yadda ya kamata, sa’an nan ta kiyaye cudanyar da ke tsakanin bangarori daban daban, da ma ikon mulki, da tsarinsu na mabanbantan kasashe, ta yi kokarin inganta fahimtar juna, da hadin gwiwa da tsakanin kasashe kambobin hukumar, don tinkarar kalubale na bai daya da duniyarmu ke fuskanta. (Mai Zane: Mustapha Bulama)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Hadin Gwiwa Da Sin Na Ingiza Ci Gaban Kasashen Afirka, In Ji Wani Kwararre

Next Post

Gidan Yari Da Amurka Ta Kafa A Ketare Ya Keta Hakkin Bil Adama

Related

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

11 hours ago
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata
Daga Birnin Sin

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

12 hours ago
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

14 hours ago
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya
Daga Birnin Sin

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

15 hours ago
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar
Daga Birnin Sin

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

22 hours ago
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

24 hours ago
Next Post
Gidan Yari Da Amurka Ta Kafa A Ketare Ya Keta Hakkin Bil Adama

Gidan Yari Da Amurka Ta Kafa A Ketare Ya Keta Hakkin Bil Adama

LABARAI MASU NASABA

Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.