• English
  • Business News
Friday, August 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Amurka Ta Sake Rura Wuta Kan Batun Gano Asalin Annobar Covid-19?

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Me Ya Sa Amurka Ta Sake Rura Wuta Kan Batun Gano Asalin Annobar Covid-19?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanan nan, gwamnatin kasar Amurka ta sake rura wuta kan batun gano asalin annobar Covid-19, inda bi da bi, ma’aikatar makamashi ta kasar da hukumar bincike ta FBI suka bayyana cewa, “Ta yiwu” annobar ta samo asalinta ne daga dakin gwaji na kasar Sin, sai kuma majalisun dokokin kasar suka zartas da shirin doka, da ya shafi batun gano asalin annobar, wanda kuma shugaba Biden na Amurkar ya sa hannu a kansa don ya zama doka. 

Duk da cewa, gano asalin cutar nauyi ne na bai daya dake wuyan kasa da kasa, amma akwai shakku game da yadda Amurkar ke “gano asalinta”. Na farko, gano asalin cutar aiki ne da ya shafi kimiyya, wanda ya kamata a dorawa masana ilimin kimiyya na kasa da kasa, amma me ya sa Amurkar ta dora aikin a wuyan sassan kula da makamashi da na leken asiri? Na biyu kuwa, me ya sa Amurka ta yi ta yayata karairayi game da wai “cutar na daga dakin gwaji” tare da nuna yatsa ga kasar Sin, amma ba tare da samar da shaidu ba? Lallai, ta hakan muna iya ganin yadda take siyasantar da cutar, a kokarin cimma burinta na shafa wa kasar Sin kashin kaza.

  • CGTN Global Poll: Babu Demokuradiyyar Da Ta Fi Wata

Hasali ma dai, Amurka ta saba da daukar irin wannan mataki don cimma burinta. Idan ba a manta ba, yau shekaru 20 da suka wuce, ta zargi kasar Iraki da mallakar makaman kare dangi, kuma da wannan hujja ce ta kaddamar da yaki a kasar, amma ga shi har yanzu ta kasa samar da shaidu kan hakan, duk da haka Iraki ta lalace sakamakon yakin. Ga kuma abin da ta aikata a Syria da ma a kan batun bututun iskar gas na “Nord Stream”, hakika abubuwan da ta yi sun wuce zaton al’umma.

A cikin ‘yan shekarun baya, Amurka ta dauki duk matakan da ta ga dama don dakile kasar Sin, da haka muke iya fahimtar me ya sa take sake rura wuta a kan batun gano asalin cutar. A hakika, wannan daya ne daga cikin jerin matakanta na kalubalantar kasar Sin.

Sama da shekaru uku ke nan bayan aukuwar annobar Covid-19, kuma kasashen duniya na farfadowa daga barnar da annobar ta haifar. Annobar ta kuma sake shaida mana cewa, a gaban mummunar matsalar da ta shafi duniya baki daya, kasa da kasa na cikin babban jirgi daya ne a maimakon kowanensu na cikin karamin jirgi daya tilo, kuma babban jirgin na iya tinkarar guguwa mai karfi a maimakon karamin jirgi.

Labarai Masu Nasaba

Sashen Aikewa Da Kunshin Sakwanni Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni 7 Na Farkon Bana

Salon Zamanantarwa Na Sin Kyakkyawan Misali Ne Ga Kasashen Afirka

Har kullum, kasar Sin na goyon baya tare da sa hannu a aikin gano asalin cutar da aka gudanar a kimiyyance, amma kuma tana adawa da siyasantar da cutar ta ko wace hanya. Jirgi daya ne ‘Yan Adam suke ciki, don haka, ya kamata su hada gwiwa da juna a maimakon yin fito na fito, ta hakan kuma suke iya isa inda suka dosa. Kamata ya yi Amurka ta yi watsi da ra’ayin cacar baka, ta hada kai da kasar Sin da ma sauran kasashen duniya baki daya, don ta taka rawar da ta dace da matsayinta, a fannonin gano asalin cutar, da farfado da tattalin arzikin duniya da ma gudanar da harkokin duniya. (Mai zane: Mustapha Bulama)

 

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Cika Shekaru 10 Tun Bayan Da Xi Jinping Ya Gabatar Da Ra’ayin Gina Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Daukacin Bil’adama

Next Post

Zan Yi Mulki Da Kowa, Zan Rike Amanar Al’ummar Jihar Kaduna – Uba Sani

Related

Sashen Aikewa Da Kunshin Sakwanni Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni 7 Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Sashen Aikewa Da Kunshin Sakwanni Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni 7 Na Farkon Bana

15 hours ago
Salon Zamanantarwa Na Sin Kyakkyawan Misali Ne Ga Kasashen Afirka
Daga Birnin Sin

Salon Zamanantarwa Na Sin Kyakkyawan Misali Ne Ga Kasashen Afirka

16 hours ago
Tsarin Samar Da Kayayyaki Na Masana’antar Lantarki Ya Ci Gaba Da Samun Karfin Juriya A Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Tsarin Samar Da Kayayyaki Na Masana’antar Lantarki Ya Ci Gaba Da Samun Karfin Juriya A Kasar Sin

17 hours ago
Kuri’ar Jin Ra’ayi Ta CGTN: Manufar “Tsaunuka Biyu” Ta Sin Ta Samu Gagarumar Karbuwa A Duniya
Daga Birnin Sin

Kuri’ar Jin Ra’ayi Ta CGTN: Manufar “Tsaunuka Biyu” Ta Sin Ta Samu Gagarumar Karbuwa A Duniya

18 hours ago
‘Yan Sama Jannatin Shenzhou-20 Za Su Gudanar Da Zagaye Na 3 Na Aiki A Wajen Cibiyar Binciken Sararin Samaniya Ta Sin
Daga Birnin Sin

‘Yan Sama Jannatin Shenzhou-20 Za Su Gudanar Da Zagaye Na 3 Na Aiki A Wajen Cibiyar Binciken Sararin Samaniya Ta Sin

19 hours ago
An Samu Gagarumin Ci Gaba Kan Habaka Fasahar Zamani Ta Sin Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Na 14 
Daga Birnin Sin

An Samu Gagarumin Ci Gaba Kan Habaka Fasahar Zamani Ta Sin Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Na 14 

20 hours ago
Next Post
Zan Yi Mulki Da Kowa, Zan Rike Amanar Al’ummar Jihar Kaduna – Uba Sani

Zan Yi Mulki Da Kowa, Zan Rike Amanar Al'ummar Jihar Kaduna - Uba Sani

LABARAI MASU NASABA

GORON JUMA’A

GORON JUMA’A

August 15, 2025
Ma’aikatan Sufurin Jiregen Sama Sun Bukaci Tinubu Ya Janye Shirin Sayar Da Filayen Jiragen Sama

Ma’aikatan Sufurin Jiregen Sama Sun Bukaci Tinubu Ya Janye Shirin Sayar Da Filayen Jiragen Sama

August 15, 2025
Sojoji Sun Ceto Shugaban Fulani, Mutane 5 Daga Hannun Ƴan Bindiga A Kogi

Sojoji Sun Ceto Shugaban Fulani, Mutane 5 Daga Hannun Ƴan Bindiga A Kogi

August 15, 2025
Cire Tallafin Mai Ya Taimaka Mana Wajen Aiwatar da Ayyuka, In Ji Gwamna Mbah

Cire Tallafin Mai Ya Taimaka Mana Wajen Aiwatar da Ayyuka, In Ji Gwamna Mbah

August 15, 2025
NPA Ta Fito Da Sabuwar Doka Kan Kayan Da Ake Ajiyewa A Tashoshinta

NPA Ta Fito Da Sabuwar Doka Kan Kayan Da Ake Ajiyewa A Tashoshinta

August 15, 2025
An Taƙaita Zirga-Zirga A Ƙananan Hukumomi 4 Kafin Zaben Cike Gurbi A Kano

An Taƙaita Zirga-Zirga A Ƙananan Hukumomi 4 Kafin Zaben Cike Gurbi A Kano

August 15, 2025
Manufofin Hulda Da Kasashen Wajen Da Nijeriya Ke Bukata

Manufofin Hulda Da Kasashen Wajen Da Nijeriya Ke Bukata

August 15, 2025
Shugaba Tinubu Ya Naɗa Sabon Darakta-Janar Na NTA Da Wasu Daraktoci

Shugaba Tinubu Ya Naɗa Sabon Darakta-Janar Na NTA Da Wasu Daraktoci

August 15, 2025
Tinubu Ya Yi Wa Arewa Kokari Fiye Da Duk Wani Shugaba A Tarihin Nijeriya -Kwamared Dauda

Tinubu Ya Yi Wa Arewa Kokari Fiye Da Duk Wani Shugaba A Tarihin Nijeriya -Kwamared Dauda

August 15, 2025
Bayan Gargadi Daga Gwamnatin Tarayya: Jihohin Arewa 15 Sun Fara Daukar Matakan Dakile Ambaliyar Ruwa

Bayan Gargadi Daga Gwamnatin Tarayya: Jihohin Arewa 15 Sun Fara Daukar Matakan Dakile Ambaliyar Ruwa

August 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.