• English
  • Business News
Saturday, July 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Amurka Ta Sake Rura Wuta Kan Batun Gano Asalin Annobar Covid-19?

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Me Ya Sa Amurka Ta Sake Rura Wuta Kan Batun Gano Asalin Annobar Covid-19?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanan nan, gwamnatin kasar Amurka ta sake rura wuta kan batun gano asalin annobar Covid-19, inda bi da bi, ma’aikatar makamashi ta kasar da hukumar bincike ta FBI suka bayyana cewa, “Ta yiwu” annobar ta samo asalinta ne daga dakin gwaji na kasar Sin, sai kuma majalisun dokokin kasar suka zartas da shirin doka, da ya shafi batun gano asalin annobar, wanda kuma shugaba Biden na Amurkar ya sa hannu a kansa don ya zama doka. 

Duk da cewa, gano asalin cutar nauyi ne na bai daya dake wuyan kasa da kasa, amma akwai shakku game da yadda Amurkar ke “gano asalinta”. Na farko, gano asalin cutar aiki ne da ya shafi kimiyya, wanda ya kamata a dorawa masana ilimin kimiyya na kasa da kasa, amma me ya sa Amurkar ta dora aikin a wuyan sassan kula da makamashi da na leken asiri? Na biyu kuwa, me ya sa Amurka ta yi ta yayata karairayi game da wai “cutar na daga dakin gwaji” tare da nuna yatsa ga kasar Sin, amma ba tare da samar da shaidu ba? Lallai, ta hakan muna iya ganin yadda take siyasantar da cutar, a kokarin cimma burinta na shafa wa kasar Sin kashin kaza.

  • CGTN Global Poll: Babu Demokuradiyyar Da Ta Fi Wata

Hasali ma dai, Amurka ta saba da daukar irin wannan mataki don cimma burinta. Idan ba a manta ba, yau shekaru 20 da suka wuce, ta zargi kasar Iraki da mallakar makaman kare dangi, kuma da wannan hujja ce ta kaddamar da yaki a kasar, amma ga shi har yanzu ta kasa samar da shaidu kan hakan, duk da haka Iraki ta lalace sakamakon yakin. Ga kuma abin da ta aikata a Syria da ma a kan batun bututun iskar gas na “Nord Stream”, hakika abubuwan da ta yi sun wuce zaton al’umma.

A cikin ‘yan shekarun baya, Amurka ta dauki duk matakan da ta ga dama don dakile kasar Sin, da haka muke iya fahimtar me ya sa take sake rura wuta a kan batun gano asalin cutar. A hakika, wannan daya ne daga cikin jerin matakanta na kalubalantar kasar Sin.

Sama da shekaru uku ke nan bayan aukuwar annobar Covid-19, kuma kasashen duniya na farfadowa daga barnar da annobar ta haifar. Annobar ta kuma sake shaida mana cewa, a gaban mummunar matsalar da ta shafi duniya baki daya, kasa da kasa na cikin babban jirgi daya ne a maimakon kowanensu na cikin karamin jirgi daya tilo, kuma babban jirgin na iya tinkarar guguwa mai karfi a maimakon karamin jirgi.

Labarai Masu Nasaba

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

Har kullum, kasar Sin na goyon baya tare da sa hannu a aikin gano asalin cutar da aka gudanar a kimiyyance, amma kuma tana adawa da siyasantar da cutar ta ko wace hanya. Jirgi daya ne ‘Yan Adam suke ciki, don haka, ya kamata su hada gwiwa da juna a maimakon yin fito na fito, ta hakan kuma suke iya isa inda suka dosa. Kamata ya yi Amurka ta yi watsi da ra’ayin cacar baka, ta hada kai da kasar Sin da ma sauran kasashen duniya baki daya, don ta taka rawar da ta dace da matsayinta, a fannonin gano asalin cutar, da farfado da tattalin arzikin duniya da ma gudanar da harkokin duniya. (Mai zane: Mustapha Bulama)

 

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Cika Shekaru 10 Tun Bayan Da Xi Jinping Ya Gabatar Da Ra’ayin Gina Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Daukacin Bil’adama

Next Post

Zan Yi Mulki Da Kowa, Zan Rike Amanar Al’ummar Jihar Kaduna – Uba Sani

Related

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa
Daga Birnin Sin

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

10 hours ago
Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

11 hours ago
Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka
Daga Birnin Sin

Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

13 hours ago
Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya
Daga Birnin Sin

Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

14 hours ago
FRCN Ya Kaddamar Da Shirin Koyar Da Sinanci Mai Taken “Hello China”
Daga Birnin Sin

FRCN Ya Kaddamar Da Shirin Koyar Da Sinanci Mai Taken “Hello China”

15 hours ago
An Fitar Da Sanarwar Beijing Bayan Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adama
Daga Birnin Sin

An Fitar Da Sanarwar Beijing Bayan Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adama

16 hours ago
Next Post
Zan Yi Mulki Da Kowa, Zan Rike Amanar Al’ummar Jihar Kaduna – Uba Sani

Zan Yi Mulki Da Kowa, Zan Rike Amanar Al'ummar Jihar Kaduna - Uba Sani

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

July 12, 2025
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

July 11, 2025
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

July 11, 2025
Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

July 11, 2025
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

July 11, 2025
“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

July 11, 2025
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

July 11, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

July 11, 2025
Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

July 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.