ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 18, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Amurka Ta Sake Rura Wuta Kan Batun Gano Asalin Annobar Covid-19?

by CMG Hausa
3 years ago
Covid-19

Kwanan nan, gwamnatin kasar Amurka ta sake rura wuta kan batun gano asalin annobar Covid-19, inda bi da bi, ma’aikatar makamashi ta kasar da hukumar bincike ta FBI suka bayyana cewa, “Ta yiwu” annobar ta samo asalinta ne daga dakin gwaji na kasar Sin, sai kuma majalisun dokokin kasar suka zartas da shirin doka, da ya shafi batun gano asalin annobar, wanda kuma shugaba Biden na Amurkar ya sa hannu a kansa don ya zama doka. 

Duk da cewa, gano asalin cutar nauyi ne na bai daya dake wuyan kasa da kasa, amma akwai shakku game da yadda Amurkar ke “gano asalinta”. Na farko, gano asalin cutar aiki ne da ya shafi kimiyya, wanda ya kamata a dorawa masana ilimin kimiyya na kasa da kasa, amma me ya sa Amurkar ta dora aikin a wuyan sassan kula da makamashi da na leken asiri? Na biyu kuwa, me ya sa Amurka ta yi ta yayata karairayi game da wai “cutar na daga dakin gwaji” tare da nuna yatsa ga kasar Sin, amma ba tare da samar da shaidu ba? Lallai, ta hakan muna iya ganin yadda take siyasantar da cutar, a kokarin cimma burinta na shafa wa kasar Sin kashin kaza.

  • CGTN Global Poll: Babu Demokuradiyyar Da Ta Fi Wata

Hasali ma dai, Amurka ta saba da daukar irin wannan mataki don cimma burinta. Idan ba a manta ba, yau shekaru 20 da suka wuce, ta zargi kasar Iraki da mallakar makaman kare dangi, kuma da wannan hujja ce ta kaddamar da yaki a kasar, amma ga shi har yanzu ta kasa samar da shaidu kan hakan, duk da haka Iraki ta lalace sakamakon yakin. Ga kuma abin da ta aikata a Syria da ma a kan batun bututun iskar gas na “Nord Stream”, hakika abubuwan da ta yi sun wuce zaton al’umma.

ADVERTISEMENT

A cikin ‘yan shekarun baya, Amurka ta dauki duk matakan da ta ga dama don dakile kasar Sin, da haka muke iya fahimtar me ya sa take sake rura wuta a kan batun gano asalin cutar. A hakika, wannan daya ne daga cikin jerin matakanta na kalubalantar kasar Sin.

Sama da shekaru uku ke nan bayan aukuwar annobar Covid-19, kuma kasashen duniya na farfadowa daga barnar da annobar ta haifar. Annobar ta kuma sake shaida mana cewa, a gaban mummunar matsalar da ta shafi duniya baki daya, kasa da kasa na cikin babban jirgi daya ne a maimakon kowanensu na cikin karamin jirgi daya tilo, kuma babban jirgin na iya tinkarar guguwa mai karfi a maimakon karamin jirgi.

LABARAI MASU NASABA

Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

Har kullum, kasar Sin na goyon baya tare da sa hannu a aikin gano asalin cutar da aka gudanar a kimiyyance, amma kuma tana adawa da siyasantar da cutar ta ko wace hanya. Jirgi daya ne ‘Yan Adam suke ciki, don haka, ya kamata su hada gwiwa da juna a maimakon yin fito na fito, ta hakan kuma suke iya isa inda suka dosa. Kamata ya yi Amurka ta yi watsi da ra’ayin cacar baka, ta hada kai da kasar Sin da ma sauran kasashen duniya baki daya, don ta taka rawar da ta dace da matsayinta, a fannonin gano asalin cutar, da farfado da tattalin arzikin duniya da ma gudanar da harkokin duniya. (Mai zane: Mustapha Bulama)

 

 

Covid-19
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

July 17, 2026
Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

July 17, 2026
Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA
Daga Birnin Sin

Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

July 17, 2026
Next Post
Zan Yi Mulki Da Kowa, Zan Rike Amanar Al’ummar Jihar Kaduna – Uba Sani

Zan Yi Mulki Da Kowa, Zan Rike Amanar Al'ummar Jihar Kaduna - Uba Sani

LABARAI MASU NASABA

Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

July 17, 2026
Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

July 17, 2026
Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

July 17, 2026
Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

July 17, 2026
Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

July 17, 2026
Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

July 17, 2026
Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

July 17, 2026
Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

July 17, 2026
Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

July 17, 2026
Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.