• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Bayern Liverkusen Ta Kori Erik Ten Hag Bayan Wasanni Biyu?

by Abba Ibrahim Wada
3 weeks ago
in Wasanni
0
Me Ya Sa Bayern Liverkusen Ta Kori Erik Ten Hag Bayan Wasanni Biyu?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanaki kaɗan bayan kama aiki a ƙungiyar Bayer Leɓerkusen, tsohon mai horas da Manchester United Eric Ten Hag ya gaza jagorantar ƙungiyar na tsawon ko da mako 10.

Ba mako 10 ba ma, ko mako 9 bai cika ba, inda ya yi kwana 62 kacal a ƙungiyar, bayan buga wasan gasar Bundesliga biyu kacal. An kore shi ne bayan Leɓerkusen ta gaza yin nasara a karawarta da Werder Bremen a ranar Asabar. Da farko Leɓerkusen ce ta shige gaba da ci 3-1, inda Bremen ta samu jan kati, amma daga baya aka tashi wasan canjaras 3-3.

  • Al Hilal Za Ta Biya Yuro Miliyan 53 Don Ɗaukar Nunez Daga Liverpool
  • Barcelona Ta Tube Ter Stergen Daga Mukaminsa Na Kaftin Din Kungiyar 

Hakan ya biyo bayan kashin da Leɓerkusen ta sha a gida a hannun Hoffenheim a wasanta na farko na gasar Bundesliga na wannan kaka. Wasa ɗaya ne kacal Ten Hag ya samu nasara a matsayin mai horas da Leɓerkusen.

An naɗa Ten Hag a muƙamin ne a ƙarshen watan Mayu domin maye gurbin tsohon kocin ƙungiyar Ɗabi Alonso, wanda ya koma Real Madrid. Da farko, Leɓerkusen ta yi tsammanin zai iya jan ragamar sake gina ƙungiyar bayan rasa ƴan  wasanta irin su Florian Wirtz da Jonathan Tah.

To sai dai sakamakon wasannin farko-farko na wannan kakar ba su yi kyau ba, amma ba wannan ne babban dalili ko kuma ɗaya daga cikin manyan dalilan da suka haifar da korar Ten Hag ba. Kusan tun farko Ten Hag ya fara shafa wa kansa baƙin fenti sanadiyyar wasu matakai da ya ɗauka da kuma halayyarsa.

Labarai Masu Nasaba

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Misali, ya sauya lokacin da aka tsara yin wasan sada zumunta da ƴan  ƙasa da shekara 20 na ƙungiyar Flamengo a lokacin da Leɓerkusen ta je atisaye a Brazil. An buga wasan kwana biyar kafin ranar da aka tsara tun farko, inda Leɓerkusen ta sha kashi da ci 5-1.

Haka nan a kusan wannan lokacin ne Ten Hag ya yanke hukunci kan batun tafiyar Granit Ɗhaka, inda ya ce ya kamata ya tsaye saboda Leɓerkusen ta rasa manyan ƴan  wasa da yawa.

Sai dai tuni ƙungiyar ta sanar cewa Ɗhaka zai iya tafiya idan aka samu tayi mai kyau. Daga baya ya tafi Sunderland. Haka nan kuma Ten Hag ya soki ƴan  wasansa tare da cewa ba su da kuzarin da ya kamata duk da cewa shi da tawagarsa ne suka jagoranci tawagar.

Bugu da ƙari an zargi Ten Hag da rashin kwarjinin da ake koci ke buƙata domin jan ragamar babbar ƙungiya, musamman ma ƙungiyar da ta kawo sabbin ƴan  wasa da dama.

Za a iya cewa da alama ya riƙa shan wahala wajen shawo kan ƴan  wasa su bi tsarinsa, domin wasu majiyoyi sun ce bai iya yi wa ƴan  wasa wata ƙwaƙƙwarar huɗuba gabanin buga wasa. Sannan an bayyana cewa bai yi wa ƴan  wasan jawabi ba gabanin karawarsu ta farko da Hoffenheim. Akasin Alonso, wanda aka ce shi ya riƙa ƙarin ganin ya ƙara ƙwarewa a harshen Jamusanci tare da samun ƙarin gogewa lokacin da yake jagorantar ƙungiyar ta Leɓerkusen.

Abin ya ba da mamaki sosai yadda shugabannin Leɓerkusen suka yanke shawarar korar Ten Hag da wurwuri haka domin wannan ba abu ne mai alfanu ba ga daraktan wasanni na ƙungiyar Simon Rolfes – wanda ya dage kan a ɗauki Ten Hag a lokacin da ƙungiyar ke son ɗaukar sabon koci a watan Mayu – har ma da shugaban ƙungiyar Fernando Carro.

A ƴan  shekarun da suka gabata Ten Hag ya kasance ƙwararren mai horaswa lokacin da ya samu nasara sosai a Ajaɗ. Ya lashe gasar Holland sau uku sannan ya kai wasan kusa da na ƙarshe a gasar zakarun nahiyar Turai ta Champions League a shekara ta 2019.

Ko a shekarar farko na jagorancin Manchester United aikinsa ya yi kyau babu laifi, kuma an alaƙanta barin aikinsa daga ƙungiyar kan rikicin da ƙungiyar ta fuskanta amma ba domin gazawarsa a matsayin mai horaswa ba. Amma a yanzu Leɓerkusen da alama tana cikin ruɗani. Kusan za a iya cewa a shirye suke su sayer da duk wani ɗan wasa da ya nuna aniyar barin ƙungiyar. A lokaci guda kuma ƴan  wasa irin su Malik Tillman da Jarell Ƙuansah sun tafi ƙungiyar tare da sa ran cewa Ten Hag ne zai ci gaba da horaswa.

A yanzu Leɓerkusen na buƙatar nemo wanda zai maye gurbinsa. Akwai rahotannin cewa sun tattauna da tsohon kocin Barcelona Ɗaɓi, haka nan kuma tsohon mai horas da Dortmund da Leipzig Marco Rose na cikin waɗanda ake ganin za su iya samun aikin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FOOTBALLLiverkusen
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Karrama Fitattun Fina-Finai A Bikin “Golden Panda” Da Ya Gudana A Lardin Sichuan Na Kasar Sin

Next Post

Sama Da Fam Biliyan Uku Aka Kashe A Firimiyar Ingila Wajen Sayen Ƴan Wasa

Related

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or
Wasanni

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

18 hours ago
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya
Wasanni

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

21 hours ago
Ƴar Wasan Gaban Nijeriya, Ifeoma Onumonu Ta Yi Ritaya
Wasanni

Ƴar Wasan Gaban Nijeriya, Ifeoma Onumonu Ta Yi Ritaya

23 hours ago
Lamine Yamal Zai Shafe Mako 3 Yana Jinya
Wasanni

Lamine Yamal Zai Shafe Mako 3 Yana Jinya

2 days ago
PSG Ta Doke Barcelona Har Gida A Gasar Zakarun Turai
Wasanni

PSG Ta Doke Barcelona Har Gida A Gasar Zakarun Turai

4 days ago
Mbappe Ya Jefa Kwallonsa Ta 60 A Gasar Zakarun Turai A Wasan Da Real Madrid Ta Doke Kairat 
Wasanni

Mbappe Ya Jefa Kwallonsa Ta 60 A Gasar Zakarun Turai A Wasan Da Real Madrid Ta Doke Kairat 

4 days ago
Next Post
Sama Da Fam Biliyan Uku Aka Kashe A Firimiyar Ingila Wajen Sayen Ƴan Wasa

Sama Da Fam Biliyan Uku Aka Kashe A Firimiyar Ingila Wajen Sayen Ƴan Wasa

LABARAI MASU NASABA

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

October 5, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

October 5, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

October 5, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.