• English
  • Business News
Saturday, June 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Za A Sake Zabar Kasar Sin?

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Me Ya Sa Za A Sake Zabar Kasar Sin?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

“Wurin da ya fi kasar Sin kyau a nan gaba, shi ne kasar Sin ta nan gaba.” Kwanan baya, shugaba Xi Jinping ya ambato wannan ra’ayin rukunonin masana’antu da kasuwanci cikin jawabinsa, yayin halartar tarukan kungiyar APEC a San Francisco ta kasar Amurka, lamarin da ya ja hankalin duniya.

Me ya sa rukunonin masana’antu da kasuwanci na kasa da kasa suka zabi kasar Sin? Manufofi 3 da shugaba Xi ya jaddada a yayin tarukan APEC, wadanda kasar Sin ba za ta sauya ba, sun ba da amsa.

  • Ana Fatan Sakamakon Ganawar Xi Da Biden Zai Taka Rawa Wajen Kyautata Dangantakar Sin Da Amurka
  • Wang Yi Ya Tattauna Da Takwarorinsa Na Kasashen Larabawa Da Na Musulmi

Kasar Sin, inji ne mafi girma dake ingiza ci gaban tattalin arzikin duniya. Gudummawar da za ta bayar kan bunkasar tattalin arzikin duniya a bana za ta kai kashi 1 cikin kashi 3. A ‘yan kwanankin baya, asusun ba da lamuni na duniya IMF ya kyautata hasashen da aka yi kan karuwar GDP din kasar Sin a shekarar 2023 zuwa 5.4%. Hakan ya tabbatar da cewa, kasar Sin na da karfin juriya da boyayyen karfi, da dabaru da dama wajen raya tattalin arziki, kana tubalin tattalin arzikin Sin na samun ci gaba ba zai sauya ba.

Har ila yau, cikin manyan abokan cinikayyar kasar Sin guda 10, wasu 8 na cikin kungiyar APEC, haka kuma, kasar Sin ta kasance abokiyar ciniki mafi girma ga rukunoni 13 na kungiyar APEC. A yayin tarukan APEC a bana, kasar Sin ta gabatar da wasu sabbin matakan kara azama kan bude kofa ga ketare, ciki had da rika kyautata tsarin kare hakkin baki ‘yan kasuwa na zuba jari, ci gaba da rage abubuwan da aka tanada cikin jerin sana’o’i da ayyukan da aka haramta zuba jari kansu, yin adalci tsakanin baki da ‘yan kasar a fannin zuba jari kan kamfanoni da dai sauransu. Lamarin ya nuna cewa, kasar Sin ba za ta sauya aniyarta ta samar da yanayin kasuwanci da ya kai mizanin kasa da kasa wanda zai dace da bukatun kasuwa kuma bisa doka ba. Kana ba za ta sauya manufarta ta yin adalci a tsakanin baki da ‘yan kasar wajen samun kyakkyawar hidima ba.

Lallai wadannan manufofin 3 da kasar Sin ba za ta sauya ba, sun samar da tabbaci da kwanciyar hankali, wadanda duniya ke matukar bukata yayin da take fuskantar sauye-sauye da rashin kwanciyar hankali. (Tasallah Yuan)

Labarai Masu Nasaba

Sin Ta Harba Tauraron Dan Adam Na Lura Da Yanayin Bala’u

An Samu Babban Canji Kan Tsarin Ciniki A Tsakanin Sin Da Afirka


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KasuwanciRashaTattalin Arziki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wang Yi Ya Tattauna Da Takwarorinsa Na Kasashen Larabawa Da Na Musulmi

Next Post

Kokarin Hadin Kai Don Samar Da Isasshen Abinci A Nahiyar Afirka

Related

Sin Ta Harba Tauraron Dan Adam Na Lura Da Yanayin Bala’u
Daga Birnin Sin

Sin Ta Harba Tauraron Dan Adam Na Lura Da Yanayin Bala’u

2 hours ago
An Samu Babban Canji Kan Tsarin Ciniki A Tsakanin Sin Da Afirka
Daga Birnin Sin

An Samu Babban Canji Kan Tsarin Ciniki A Tsakanin Sin Da Afirka

2 hours ago
Sin Ta Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Kaddamar Da Hare-hare Kan Iran
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Kaddamar Da Hare-hare Kan Iran

3 hours ago
Taron Koli Na Sin Da Kasashen Yankin Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu Zai Ingiza Manufar Kara Dunkulewar Sassan Yankin
Daga Birnin Sin

Taron Koli Na Sin Da Kasashen Yankin Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu Zai Ingiza Manufar Kara Dunkulewar Sassan Yankin

21 hours ago
Babban Jami’in Diflomasiyyar Kasar Sin Ya Yi Kiran Karfafa Alaka Da Afirka
Daga Birnin Sin

Babban Jami’in Diflomasiyyar Kasar Sin Ya Yi Kiran Karfafa Alaka Da Afirka

23 hours ago
Xi Ya Yi Kira Da A Kara Azamar Gina Kasa A Gabar Da Ake Bikin Cika Shekaru 120 Da Haihuwar Dan Mazan Jiya Chen Yun
Daga Birnin Sin

Xi Ya Yi Kira Da A Kara Azamar Gina Kasa A Gabar Da Ake Bikin Cika Shekaru 120 Da Haihuwar Dan Mazan Jiya Chen Yun

23 hours ago
Next Post
Kokarin Hadin Kai Don Samar Da Isasshen Abinci A Nahiyar Afirka

Kokarin Hadin Kai Don Samar Da Isasshen Abinci A Nahiyar Afirka

LABARAI MASU NASABA

Danbun Shinkafa Da Nama Da Kifi

Danbun Shinkafa Da Nama Da Kifi

June 14, 2025
Wutar Lantarki Mai Ƙarfi Ta Yi Ajalin Mutum Biyar A Gombe

Wutar Lantarki Mai Ƙarfi Ta Yi Ajalin Mutum Biyar A Gombe

June 14, 2025
Sin Ta Harba Tauraron Dan Adam Na Lura Da Yanayin Bala’u

Sin Ta Harba Tauraron Dan Adam Na Lura Da Yanayin Bala’u

June 14, 2025
An Samu Babban Canji Kan Tsarin Ciniki A Tsakanin Sin Da Afirka

An Samu Babban Canji Kan Tsarin Ciniki A Tsakanin Sin Da Afirka

June 14, 2025
Muhimmanci, Tasiri Da Kuma Amfanin Jigida Ga Mata

Muhimmanci, Tasiri Da Kuma Amfanin Jigida Ga Mata

June 14, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Kaddamar Da Hare-hare Kan Iran

Sin Ta Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Kaddamar Da Hare-hare Kan Iran

June 14, 2025
Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi

June 14, 2025
Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (1)

Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (1)

June 14, 2025
Wasu Abubuwa Da Ke Sa Maza Hana Mata Fita Unguwa (Uwargida)

Kula Da Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi

June 14, 2025
Gwamnati Ta Yi Barazanar Matakai Masu Tsauri Kan Masu Fasa Bututun Mai

Gwamnati Ta Yi Barazanar Matakai Masu Tsauri Kan Masu Fasa Bututun Mai

June 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.