ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Fatan Sakamakon Ganawar Xi Da Biden Zai Taka Rawa Wajen Kyautata Dangantakar Sin Da Amurka

by Sulaiman
3 years ago
Xi

Duniya ta kasa kunne ta ji sakamakon tattaunawar da shugabannin tattalin arziki biyu mafi girma a duniya wato shugaban kasar Sin Xi Jinping da takwaransa na Amurka Joe Biden suka yi, a gefen taron kolin kungiyar APEC da ya gudana a ranar 15 ga watan Nuwamba. Shugabannin biyu sun shafe sama da sa’o’i hudu suna tattaunawa kan batutuwan da za su daidaita dangantakar dake tsakanin Sin da Amurka, wanda a bayyane ta kasance alakar diflomasiyya mafi muhimmanci a duniya a yau.   

An samu kyakkyawar fahimtar juna a tattaunawar. Bangarorin biyu sun sanar da samun ci gaba a fannonin da Amurka ta dade take son kara yin hadin gwiwa da kasar Sin, ciki har da batun samar da sinadarin fentanyl a kasar Sin, gami da sake dawo da tattaunawar soja tsakanin kasashen biyu, wani bangaren da Amurka ke son a tabbatar da cewa an kauce wa rashin fahimtar juna da rikidewa zuwa rikicin soja.

  • Shugaban Kasar Sin Ya Tattauna Da Takwaransa Na Faransa
  • Xi Da Putin Sun Aike Da Sakon Taya Murna Ga Taron Tattaunawa Tsakanin Manyan Jami’yyun Siyasar Sin Da Rasha

Bangarorin biyu sun fuskanci juna da nufin nuna wa duniya cewa a shirye suke su daidaita dangantakarsu cikin gaskiya. Don haka, kowanensu na cike da kwarin gwiwa wajen bayyana gaskiya da adalci da ci gaba. Kuma hakan ba shakka ya ginu ne bisa sakamakon taron Bali na bara, da kuma goyon bayan ci gaba da harkokin diflomasiyyar da suka gudana a baya-bayan nan, da daidaita matakan aiki kan wasu muhimman batutuwan da suka ambata.

ADVERTISEMENT

Shugaba Xi, a jawabinsa na bude taron, ya jaddada cewa, duniya na da girmar da kowace kasa za ta gudanar da harkokinta ba tare da kawo tsaiko ga wata kasa ba, kana, nasarar da wata kasa ta samu dama ce ga wata kasa daban, yayin da shugaba Biden shi kuma ya bayyana muhimmancin tabbatar da cewa gasa ba ta nufin rikici.

A ra’ayi na, tattaunawa da sadarwa su ne mabudin cimma daidaiton da ya dace. Matukar za mu iya sarrafa rashin jituwar dake tsakaninmu ta hanyar tattaunawa da sadarwa da kuma fahimtar juna, ina ganin akwai damar nunawa jama’a da duniya cewa za a iya tafiyar da dangantakar wadannan kasashen biyu cikin gaskiya da adalci. Yana da matukar muhimmanci ga bangarorin biyu su mayar da martani ga bukatun duniya ta hanyar mutunta alakar dake tsakaninsu.

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Duniya a halin yanzu tana fama da ainihin rikice-rikice da dama, kama daga rikicin sauyin yanayi da rashin tabbacin tattalin arziki, zuwa rikice-rikicen dake tasowa na rashin wadatar abinci a dalilin rashin tsaro. Wadannan su ne tarin matsalolin da duniya ke fuskanta da ya kamata a warware a cikin wannan karni na 21, kuma zaman lafiya da jituwa tsakanin Amurka da Sin ka iya zama silar daidaituwar wadannan matsaloli.

Kasashen duniya ba sa so a bar su da zabi tsakanin Amurka da Sin. Duniyar da aka gina a kan bangaranci da rarrabuwar kawuna inda Amurka ke jagorantar wani bangare yayin da Sin ke jan ragamar wani bangare ba shi da amfani ga kasashen duniya. Kuma ba zai taimaka wajen warware matsalolin da duniya ke ciki ba. (Muhammed Yahaya)

Xi
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • Sulaiman
    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

MASU ALAKA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
Daga Birnin Sin

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
Daga Birnin Sin

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
Daga Birnin Sin

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Next Post
Ratciffe Na Dab Da Sayen Kashi 25 Na Manchester United

Ratciffe Na Dab Da Sayen Kashi 25 Na Manchester United

LABARAI MASU NASABA

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.