• English
  • Business News
Friday, July 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Fatan Sakamakon Ganawar Xi Da Biden Zai Taka Rawa Wajen Kyautata Dangantakar Sin Da Amurka

by Sulaiman
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Ana Fatan Sakamakon Ganawar Xi Da Biden Zai Taka Rawa Wajen Kyautata Dangantakar Sin Da Amurka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Duniya ta kasa kunne ta ji sakamakon tattaunawar da shugabannin tattalin arziki biyu mafi girma a duniya wato shugaban kasar Sin Xi Jinping da takwaransa na Amurka Joe Biden suka yi, a gefen taron kolin kungiyar APEC da ya gudana a ranar 15 ga watan Nuwamba. Shugabannin biyu sun shafe sama da sa’o’i hudu suna tattaunawa kan batutuwan da za su daidaita dangantakar dake tsakanin Sin da Amurka, wanda a bayyane ta kasance alakar diflomasiyya mafi muhimmanci a duniya a yau.   

An samu kyakkyawar fahimtar juna a tattaunawar. Bangarorin biyu sun sanar da samun ci gaba a fannonin da Amurka ta dade take son kara yin hadin gwiwa da kasar Sin, ciki har da batun samar da sinadarin fentanyl a kasar Sin, gami da sake dawo da tattaunawar soja tsakanin kasashen biyu, wani bangaren da Amurka ke son a tabbatar da cewa an kauce wa rashin fahimtar juna da rikidewa zuwa rikicin soja.

  • Shugaban Kasar Sin Ya Tattauna Da Takwaransa Na Faransa
  • Xi Da Putin Sun Aike Da Sakon Taya Murna Ga Taron Tattaunawa Tsakanin Manyan Jami’yyun Siyasar Sin Da Rasha

Bangarorin biyu sun fuskanci juna da nufin nuna wa duniya cewa a shirye suke su daidaita dangantakarsu cikin gaskiya. Don haka, kowanensu na cike da kwarin gwiwa wajen bayyana gaskiya da adalci da ci gaba. Kuma hakan ba shakka ya ginu ne bisa sakamakon taron Bali na bara, da kuma goyon bayan ci gaba da harkokin diflomasiyyar da suka gudana a baya-bayan nan, da daidaita matakan aiki kan wasu muhimman batutuwan da suka ambata.

Shugaba Xi, a jawabinsa na bude taron, ya jaddada cewa, duniya na da girmar da kowace kasa za ta gudanar da harkokinta ba tare da kawo tsaiko ga wata kasa ba, kana, nasarar da wata kasa ta samu dama ce ga wata kasa daban, yayin da shugaba Biden shi kuma ya bayyana muhimmancin tabbatar da cewa gasa ba ta nufin rikici.

A ra’ayi na, tattaunawa da sadarwa su ne mabudin cimma daidaiton da ya dace. Matukar za mu iya sarrafa rashin jituwar dake tsakaninmu ta hanyar tattaunawa da sadarwa da kuma fahimtar juna, ina ganin akwai damar nunawa jama’a da duniya cewa za a iya tafiyar da dangantakar wadannan kasashen biyu cikin gaskiya da adalci. Yana da matukar muhimmanci ga bangarorin biyu su mayar da martani ga bukatun duniya ta hanyar mutunta alakar dake tsakaninsu.

Labarai Masu Nasaba

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

Duniya a halin yanzu tana fama da ainihin rikice-rikice da dama, kama daga rikicin sauyin yanayi da rashin tabbacin tattalin arziki, zuwa rikice-rikicen dake tasowa na rashin wadatar abinci a dalilin rashin tsaro. Wadannan su ne tarin matsalolin da duniya ke fuskanta da ya kamata a warware a cikin wannan karni na 21, kuma zaman lafiya da jituwa tsakanin Amurka da Sin ka iya zama silar daidaituwar wadannan matsaloli.

Kasashen duniya ba sa so a bar su da zabi tsakanin Amurka da Sin. Duniyar da aka gina a kan bangaranci da rarrabuwar kawuna inda Amurka ke jagorantar wani bangare yayin da Sin ke jan ragamar wani bangare ba shi da amfani ga kasashen duniya. Kuma ba zai taimaka wajen warware matsalolin da duniya ke ciki ba. (Muhammed Yahaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotun Daukaka Kara Ta Tabbatar Da Hyacinth A Matsayin Gwamnan Benuwe

Next Post

Ratciffe Na Dab Da Sayen Kashi 25 Na Manchester United

Related

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita
Daga Birnin Sin

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

11 hours ago
Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL
Daga Birnin Sin

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

12 hours ago
Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori
Daga Birnin Sin

Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

13 hours ago
Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

15 hours ago
An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing
Daga Birnin Sin

An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

16 hours ago
UNHRC Ta Zartas Da Kudurin Sin Kan Kiyaye Hakkin Dan Adam Ta Hanyar Samun Ci Gaba
Daga Birnin Sin

UNHRC Ta Zartas Da Kudurin Sin Kan Kiyaye Hakkin Dan Adam Ta Hanyar Samun Ci Gaba

1 day ago
Next Post
Ratciffe Na Dab Da Sayen Kashi 25 Na Manchester United

Ratciffe Na Dab Da Sayen Kashi 25 Na Manchester United

LABARAI MASU NASABA

NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta

NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta

July 11, 2025
Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

July 11, 2025
Yunkurin Magance Matsalar Tsaro Da Rigingimu A Arewa…

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

July 11, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

July 10, 2025
Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

July 10, 2025
Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

July 10, 2025
Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

July 10, 2025
Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

July 10, 2025
An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

July 10, 2025
Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

July 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.