ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 6, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kokarin Hadin Kai Don Samar Da Isasshen Abinci A Nahiyar Afirka

by CGTN Hausa
3 years ago
Afirka

A yau an kaddamar da taron kolin tabbatar da wadatar abinci a duniya a kasar Birtaniya don neman daidaita matsalar rashin isasshen abinci dake dada tsananta sakamakon sauyawar yanayi, da rikicin siyasa, gami da tafiyar hawainiyar tattalin arzikin duniya. Wani rahoton hukumar samar da abinci da raya aikin gona ta MDD ya nuna cewa, a halin yanzu, akwai mutane kimanin miliyan 735 dake fama da yunwa a duniyarmu, adadin da ya karu da miliyan 122 bisa na shekarar 2019. Kana a kasashen Afirka 35 dake kudu da hamadar Sahara, kimanin mutane miliyan 146 na fuskantar matsalar rashin isasshen abinci. 

Ta yaya za mu iya daidaita wannan matsala? Daya daga cikin matakan da ake iya dauka, shi ne hadin kai tsakanin mabambantan kasashe ta fuskar kimiyya da fasaha masu alaka da aikin gona, don raya tsare-tsaren aikin gona masu inganci a duk fadin duniya. Kana kasar Sin da kasashen Afirka sun riga sun cimma dimbin nasarorin da za su iya zame wa sauran kasashe misalai a wannan fanni.

  • Ana Fatan Sakamakon Ganawar Xi Da Biden Zai Taka Rawa Wajen Kyautata Dangantakar Sin Da Amurka
  • Xi Da Putin Sun Aike Da Sakon Taya Murna Ga Taron Tattaunawa Tsakanin Manyan Jami’yyun Siyasar Sin Da Rasha

Yanzu a dimbin kasashen dake nahiyar Afirka, nau’in amfanin gona na kasar Sin, da fasahohin kasar a fannin aikin gona, sun sa ana samun girbi mai armashi, da kwantar da hankalin jama’ar kasashen Afirka a fannin wadatar abinci. Misali, a jihar Morogoro ta kasar Tanzania, wasu kwararru Sinawa daga jami’ar nazarin aikin gona ta kasar Sin sun yada fasaha mai inganci ta shuka masara, inda har yawan masarar da ake girbi ya ninka sau 3. Sa’an nan sun ci gaba da yada fasahar shuka wake tsakanin masara, don baiwa manoman wurin damar samun karin kudin shiga. Yanzu haka ruwan wake da Sinawa suka saba da shansa, wanda ake samu ta hanyar dafawa, da nikawa, da tace wake, ya zama wani nau’in abinci mai farin jini a jihar Morogoro ta kasar Tanzania. Kana wasu manoma sun samu karin kudi ta hanyar shuka wake, da sayar da ruwan wake, har ma sun bude wuraren cin abinci na kansu. Wato, ba kawai sun kawar da matsalar yunwa ba, har ma sun kama hanyar samun wadata.

ADVERTISEMENT

Sai dai a fannin noman sauran amfanin gona, tabbatar da samun girbi mai armashi bai isa ba. Misali, rogon da ake yawan nomansa a kasashen Afrika. Idan an yi girbin rogo, dole ne a sarrafa shi cikin sa’o’i 48, don hana shi lalacewa. Wannan halayya ta kan sa a samu hasarar kashi 40% cikin rogon da aka girbe, a wasu kasashen dake nahiyar Afirka. Saboda haka fasaha mai inganci a fannin sarrafa rogo tana da muhimmanci sosai, abin da ya sa ta zama wani muhimmin bangaren da Sin da Afirka suke hadin kai a kansa. Yanzu haka, a cikin wata cibiyar nuna fasahohin aikin gona masu inganci da kasar Sin ta gina wa kasar Kongo Brazaville a matsayin tallafi, wasu injuna na sarrafa rogo na aiki cikin sauri, inda wadannan injuna ke wankewa, da yayankawa, da nikawa, da busar da rogo, da mai da shi gari. A cewar Paul Ngobo, minista mai kula da aikin gona, da kiwon dabbobi, da kamun kifi na kasar Kongo Brazaville, ta hanyar sarrafa rogo da injunan zamani, ana iya samar da garin rogo ga jama’a ta wani farashi mai karko, kuma an sa bukatarsa ta karu, baya ga taimakawa manoma samun karin kudin shiga.

Hakika, a yanzu haka, hadin gwiwar da ake yi tsakanin kasar Sin da kasashen Afirka a fannin fasahohin aikin gona, bai tsaya a kasa ba, har ma yana wakana a sararin samaniya. Kasar Sin ta yi amfani da taurarin dan Adam wajen tsara fasahohin binciken yanayin aikin gona daga nesa, kana kasar ta koyar da fasahar ga duk kasar dake da bukata, ba tare da karbar kudi ba, don taimaka musu wajen binciken yanayin aikin gona, da samun alkaluman da ake bukata, ta yadda za a iya tsara ayyukan noma cikin kima, da tinkarar bala’i daga indallahi yadda ya kamata. Rakiya Abdullahi Babamaaj, mataimakiyar darektan sashen kula da tsare-tsare masu alaka da fasahohin sararin samaniya na hukumar kula da sararin samaniya ta kasar Najeriya, ta taba halartar aikin da kasar Sin ta tsara a wannan fanni, gami da samun horo. Ta ce, nazarin hadin kai da ake yi, da ayyukan karfafa kwarewa, sun samar da fasahohi da bayanai da kasar Najeriya take bukata, a kokarin ta na cimma burin kawar da yunwa.

LABARAI MASU NASABA

Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

Akwai misalai masu tarin yawa, na hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka don tabbatar da samar da isasshen abinci ga al’ummun nahiyar Afirka. Sai dai me ya sa kasar Sin ke son zuba dimbin kudi don gudanar da hadin kai a wannan fanni? Dalili shi ne ra’ayin kasar Sin na samun “al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai daya a duniya”. Abin da ra’ayin ya kunsa ya shafi kula da bukatar sauran kasashe, yayin da ake neman biyan bukatun kai, da tabbatar da ganin ci gaban kasashe daban daban na bai daya, yayin da ake kokarin raya kai. A ganin kasar Sin, jama’ar duniya na da babbar moriya ta bai daya. Idan dimbin mutanen dake nahiyar Afirka na fama da yunwa, to, ba za su samu kudin sayen kayayyaki kirar kasar Sin ba. Kana idan tattalin arzikin kasashen Afirka ya kasa samun ci gaba, to, kamfanonin kasar Sin ma za su rasa damammaki na habaka zuba jari don samun karin riba. Wannan ra’ayi na tabbatar da moriyar juna, da moriyar bai daya, ya sa hadin gwiwar Sin da Afirka zai dore. Tun da ba mataki ne da aka dauka bisa tausayi ba, to, ba za a nuna girman kai, ko kuma tsoma baki cikin harkokin gidan sauran kasashe ba. Ta haka, hadin gwiwa zai iya haifar da karin nasarori, da sauye-sauyen yanayi mai armashi ga duniyarmu. (Bello Wang)

Afirka
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

MASU ALAKA

Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

July 5, 2026
An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”
Daga Birnin Sin

An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

July 5, 2026
Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa
Daga Birnin Sin

Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa

July 5, 2026
Next Post
Sin Ta Taimaka Wajen Gudanar Da Shirin Horas Da Daliban Jami’ar IPRC Ta Rwanda

Sin Ta Taimaka Wajen Gudanar Da Shirin Horas Da Daliban Jami’ar IPRC Ta Rwanda

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Kwace Kadarori 57 Na Tsohon Minista Malami

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Kwace Kadarori 57 Na Tsohon Minista Malami

July 6, 2026
Ƴan Bindiga Sun Kashe Manoma 9, Sun Sace Da Dama A Birnin Gwari

Ƴan Bindiga Sun Kashe Manoma 9, Sun Sace Da Dama A Birnin Gwari

July 6, 2026
Gwamnatin Kano Ta Kashe Biliyan 928 A Ayyukan Ci Gaba 1,508

Gwamnatin Kano Ta Kashe Biliyan 928 A Ayyukan Ci Gaba 1,508

July 6, 2026
Jonathan Ya Musanta Zargin Tayin Naira Biliyan 500 Domin Raba Kuri’un Kudu Maso Kudu

Jonathan Ya Musanta Zargin Tayin Naira Biliyan 500 Domin Raba Kuri’un Kudu Maso Kudu

July 6, 2026
FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

July 5, 2026
Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

July 5, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

July 5, 2026
An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

July 5, 2026
Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

July 5, 2026
Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

July 5, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.