• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mece Ce Mafitar Warware Matsalar Ukraine?

byCGTN Hausa
2 years ago
Ukraine

Yau ake cika shekaru biyu da barkewar rikici tsakanin Ukraine da Rasha. Alkaluman da aka samu na nuna cewa, a cikin wadannan shekaru biyu, al’ummomin kasashen biyu sama da dubu 500 ne suka halaka, baya ga al’ummar kasar Ukraine sama da miliyan 10 da aka raba da muhallansu. Ba kawai kasashen Rasha da Ukraine rikici ya shafa ba, har ma ya haifar da hauhawar farashin makamashi da hatsi a fadin duniya, inda wasu kasashen Afirka har suka fuskanci matsalar yunwa.

Sai dai abin takaici shi ne, har yanzu babu alamar kawo karshen rikicin.

  • A Kwai Bukatar Iyaye Su Tashi Tsaye Wajen Kula Da Tarbiyyar ‘Ya’yansu – Fatima Sa’ad
  • Sin Ta Harba Sabon Tauraron Dan Adam Na Gwajin Fasahar Sadarwa

Duk da mummunan tasirin da rikicin ya haifar wa akasarin kasashen biyu, amma Amurka ta amfana matuka daga rikicin. Masana’antun samar da makaman soja da sauran sassa masu ruwa da tsaki na kasar sun ci kazamar riba daga rikicin, baya ga yadda kasar ta ci riba mai tsoka ta fannonin makamashi da hatsi da kasuwar hannayen jari sakamakon rikicin. Baya ga rura wutar rikicin, Amurka ta kuma yaudari Ukraine, tare da raunana Rasha da Turai da kuma fadada kungiyar tsaro ta NATO, kamar yadda Bahaushe kan ce jifar tsuntsu biyu da dutse guda. Ma iya cewa, muddin rikici ya ci gaba, to, ba za a samu kwanciyar hankali a Turai ba, abin da zai sa kasashen nahiyar su kara dogara ga Amurka, ta hakan kuma Amurka za ta kara cin gajiya da kuma kiyaye matsayinta na nuna fin karfi a duniya.

Idan mun waiwayi rikici, za mu gano cewa, ra’ayin cacar baka da nuna fin karfi shi ne ainihin abin da ya haifar da rikicin. Dalilin da ya sa Amurka ta rura wutar rikicin, shi ne kiyaye matsayinta na fin karfi a duniya, tare da cin mummunar riba. A gun taron harkokin tsaro na Munich da aka gudanar a kwanan baya, sakataren harkokin wajen kasar Amurka Antony Blinken ya ce, “Ta fuskar al’amuran kasa da kasa, in dai ba a zama mai cin abinci ba, to, za a zama abinci ke nan”, furucin da ya tona mana ainihin alkiblar manufar Amurka a kan harkokin kasa da kasa, wato wadanda ke da karfi ya ke ci, yayin da wadanda ba su da karfi su ake cinye wa.

Irin yanayin da ake ciki na rashin kwanciyar hankali a duniya, ya sanya wa karin kasashe damuwar tsaronsu. Kowa na son tabbatar da tsaro, amma ta yaya hakan zai tabbata?

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Domin cimma burin tabbatar da cikakken tsaro, Amurka da sauran kasashen yamma suka ware makudan kudade a bangaren soja. A gun taron ministocin tsaro na kasashen kungiyar NATO da aka kira a kwanan baya, ma’aikatar harkokin wajen Amurka da babban sakataren NATO sun sake sa kaimin kasashe mambobin NATO da su kara kasafin kudin tsaro, inda suka nemi a kalla kasashe 18 na NATO su ware kasafin kudin tsaro da yawansa ya kai kimanin kaso 2 na GDP dinsu.

Duk da kwararan matakan da kasashen suka dauka, amma yanayin tsaronsu sai kara tabarbarewa yake yi a maimakon ingantuwa, shin mene ne dalilin haka?Sabo da tsaron da Amurka da sauran kasashen yamma suke nema shi ne tsaro na kansu, maimakon tsaron Bil Adam baki daya. Sa’an nan, a yayin da suke zancen kiyaye tsaron duniya, a hakika, suna magana ne a kan kiyaye babakeren da suka kafa. Wannan ya sa, suke ta kaddamar da yake-yake da kulla kawance da wasu, da ma ta da rikici da wasu, kuma hakan ya lalata tsaron kasashen duniya na bai daya.

A hakika, ko a kasashen yamma da kasashen gabas, ko kuma a kasashe masu ci gaba da kuma kasashe masu tasowa, burin al’ummar kasa da kasa daya ne, wato a tabbatar da zaman lafiya da tsaro a kasashensu. Abin da kawai ya bambanta shi ne wane irin tsaro ne muke so?

Game da wannan tambaya, kasar Sin ta ba da amsarta bisa shawarar kiyaye tsaro na duniya da ta gabatar, wato Global Security Initiative a Turance, inda ta shawarci kasa da kasa da su yi kokarin tabbatar da tsaronsu na bai daya. A gun taron harkokin tsaro na Munich a wannan karo, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya gabatar da jawabi, inda ya yi nuni da cewa, kamata ya yi kasa da kasa su yi kokarin neman cin nasara tare, kuma su hada kai da juna. Ya jaddada cewa, kasar Sin na bin shawarar kiyaye tsaro na duniya, kuma tana kokarin neman cimma daidaito tsakanin kasa da kasa game da batun tsagaita bude wuta a rikicin Ukraine da Rasha, tare da share fagen yin shawarwarin shimfida zaman lafiya.

A ganin kasar Sin, kasashen duniya makomarsu daya ce, kuma babu kasar da za ta iya tsira daga tashe-tashen hankula da ake fuskanta a sassan duniya.

Domin fita daga mawuyacin halin tsaro da suke ciki, ya kamata kasashen yamma su gyara tunaninsu na cin nasara daga faduwar wani bangare. Illa dai kasashen duniya su hada hannu wajen kiyaye tsaronsu na bai daya, daga karshe za a kai ga daidaita matsalar Ukraine daga tushe, da ma tabbatar da dauwamammen zaman lafiya da tsaro a duniya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci
Daga Birnin Sin

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?
Daga Birnin Sin

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
Next Post
Tsarin Mulkin Firayminista: ‘Yan Arewa Mu Yi Taka-tsan-tsan

Tsarin Mulkin Firayminista: ‘Yan Arewa Mu Yi Taka-tsan-tsan

LABARAI MASU NASABA

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version