• English
  • Business News
Tuesday, July 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Na Duniya Su Riƙa Bayar Da Rahoton Gaskiya Kan Nijeriya

by Sulaiman
11 months ago
in Labarai
0
Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Na Duniya Su Riƙa Bayar Da Rahoton Gaskiya Kan Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya buƙaci kafafen yaɗa labarai na ƙasa da ƙasa da su riƙa bin ƙa’idojin adalci da sahihanci a cikin rahotannin su da suka shafi Nijeriya.

 

Idris ya bayyana hakan ne a lokacin da ya karɓi baƙuncin wata tawaga daga BBC a ofishin sa a ranar Alhamis.

  • Sojoji Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda 5 Da Karbar Wadanda Suka Yi Saranda 44 A Borno
  • Al’ummar Arewa: Bango Ne Ya Tsage Kadangare Ya Samu Wurin Shiga

A wata sanarwa da Mataimakin Ministan na Musamman kan Harkokin Yaɗa Labarai, Rabiu Ibrahim, ya fitar, an bayyana cewa ministan ya ce yayin da manufofin gwamnatin Tinubu ke ci gaba da tabbatar da ‘yancin ‘yan jarida, gwamnati na sa ran ƙungiyoyin yaɗa labaran duniya su tabbatar da gaskiya da adalci a cikin rahotonnin su.

 

Labarai Masu Nasaba

Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Ministan ya jaddada muhimmancin daidaito da rashin son kai wajen bayar da rahotanni, kuma ya bayyana cewa yayin da Nijeriya, kamar kowace ƙasa, take fuskantar ƙalubale, yana da matuƙar muhimmanci kafafen yaɗa labarai na duniya su ba da cikakken bayani, maimakon mayar da hankali kan abubuwa marasa kyau.

 

Ya ce, “Za mu kuma roƙe ku da ku ci gaba da daidaita labaran ku don jin ta bakin mu kan labari. Ba kawai munanan abubuwan da ke fitowa daga Nijeriya ba, akwai abubuwa masu kyau da yawa kuma na tabbata wakilan ku da ke nan sun ga cewa muna da abubuwa masu kyau da muke yi a ƙasar nan kuma akwai cigaba zuwa ga wadata da muke gani.

 

“Ina so in bayyana maku ƙudirin gwamnatin Nijeriya ga kowace ƙungiya mai tattara labarai. Ƙudurin mu shi ne cewa muna son mu kasance cikin mai da hankali da rashin son zuciya kuma cikin ‘yanci.”

 

Ministan ya tabbatar da cewa gwamnatin Nijeriya ba ta samu wani rahoto da ya shafi cin zarafin ‘yan jarida da ke aiki da kafafen yaɗa labarai na duniya a ƙasar ba.

 

Ya ce, “Manufar gwamnatin Tinubu ita ce kowace ƙungiya ta labarai tana da ‘yancin gudanar da wannan sana’a kuma ina farin ciki da ba ku kawo mana rahoton wani ma’aikacin ku ba, wanda aka ci zarafin sa ko kuma ya fuskanci matsin lamba daga gwamnatin Nijeriya ba.”

 

Idris ya yaba wa irin hazaƙar da BBC ta yi wajen mayar da ɗakin watsa labarai na Sashen Hausa daga birnin Landan zuwa Abuja, inda masu kallo da kasuwanni suke, yana mai jaddada cewa wannan gagarumin shiri ya sa aka haɗa ‘yan Nijeriya kusan 200 da ke aiki da BBC a faɗin ƙasar.

 

Ministan ya bayyana jin daɗin sa da ɗorewar amana da mutunta juna tsakanin BBC da masu saurare a Nijeriya, dangantakar da ke da ƙarfi tun kusan shekaru 60.

 

Ya ce, “Haƙiƙa al’ummar Nijeriya abokan haɗin gwiwa ne da BBC kuma wannan ƙawancen ya fara shekaru da dama da suka wuce kuma ba a daina wannan sadaukarwar da muka ji a BBC da kuma mutuntawa da amincewar mutanen mu tun shekaru biyar zuwa sittin da suka gabata.”

 

Ya jinjina wa BBC kan yadda ta fara aikin gina ƙwarewar wasu ‘yan jarida da ke aiki da ƙungiyoyin yaɗa labarai na gwamnati, ya kuma yi kira ga BBC da su yi makamancin hakan ga kafafen yaɗa labarai masu zaman kan su.

 

A nasa jawabin, Daraktan Labaran Duniya kuma Mataimakin Shugaban BBC, Mista Jonathan Munro, wanda ya zo Nijeriya a karon farko, ya ce ya yi matuƙar farin ciki da shaharar BBC a ƙasar.

 

Ya ce BBC ta faɗaɗa zuwa kafofin watsa labarai da yawa a Nijeriya kuma yanzu tana yaɗa shirye-shiryen ta a cikin harsunan Pijin da Hausa da Ibo da kuma Yarbanci domin isa ga masu sauraro daban-daban a ƙasar.

 

Mista Munro, wanda ya bayyana Nijeriya a matsayin ƙasa mai ƙarfin faɗa-a-ji a duniya, ya ce kimanin mutane miliyan 30 ne ke ziyartar sashen labarai na BBC a Nijeriya a duk mako, wanda hakan ya sa Nijeriya ta zama ta uku a duniya wajen tallata BBC bayan Amurka da Indiya.

 

Mista Munro ya samu rakiyar Shugaban Harsunan Yammacin Afirka, Ehizojie Okharadia; Shugaban Sashen Labarai na Afirka, Juliet Njeri, da Shugaban Sashen Hausa na BBC, Malam Aliyu Tanko.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: NBCVOA
ShareTweetSendShare
Previous Post

A Yanzu Nijeriya Na Sayar Da Makamai Ga Kasashen Afrika – Matawalle

Next Post

Dakatar Da Harajin Shigowa Da Abinci: Gwamnati Za Ta Yi Asarar Kudin Shiga Naira Biliyan 188.37 

Related

Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC
Manyan Labarai

Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC

10 minutes ago
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano
Labarai

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

9 hours ago
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa
Manyan Labarai

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

11 hours ago
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina
Labarai

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

11 hours ago
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara
Manyan Labarai

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

13 hours ago
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata
Labarai

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

18 hours ago
Next Post
Dakatar Da Harajin Shigowa Da Abinci: Gwamnati Za Ta Yi Asarar Kudin Shiga Naira Biliyan 188.37 

Dakatar Da Harajin Shigowa Da Abinci: Gwamnati Za Ta Yi Asarar Kudin Shiga Naira Biliyan 188.37 

LABARAI MASU NASABA

Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC

Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC

July 1, 2025
Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

June 30, 2025
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

June 30, 2025
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

June 30, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

June 30, 2025
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.