• English
  • Business News
Monday, November 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Minista Ya Buƙaci Sabbin Shugabannin NIPR Su Faɗakar da Jama’a Yadda Ya Dace 

by Sulaiman
11 months ago
Minista

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya buƙaci sabbin mambobin Cibiyar Hulɗa da Jama’a ta Nijeriya (NIPR) da su gudanar da harkokin sadarwa yadda ya dace da kuma bayar da gudunmawa ga cigaban ƙasa.

 

Ministan wanda ya samu wakilcin Daraktan Yaɗa Labarai da Hulɗa da Jama’a, Dakta Sulaiman Haruna, ya bayyana hakan ne a wajen taron rantsar da sababbin jami’an yaɗa labarai da hulɗa da jama’a da aka gudanar a Ma’aikatar Yaɗa Labarai ta Tarayya, Abuja.

  • Sanatocin Kudu Maso Gabas Sun Bukaci Duba Kudirin Dokar Gyaran Haraji
  • Netanyahu Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Zargin Rashawa

A nasa jawabin, Ministan ya jaddada muhimmiyar rawar da hulɗa da jama’a ke takawa wajen tabbatar da gaskiya da riƙon amana tsakanin gwamnati da ‘yan ƙasa.

 

LABARAI MASU NASABA

Rundunar Sojin Sama Ta Kai Hari Kan ISWAP Da Ƴan Bindiga A Borno, Kwara Da Katsina

Gwamnatin Kaduna Za Ta Ɗauki Ma’aikatan Lafiya 9,000 Cikin Shekaru 5 – Maiyaki 

Ya buƙaci waɗanda aka rantsar da su yi amfani da basirar su da ilimin su wajen daƙile yaɗa labaran ƙarya, inganta haɗin kai, da kuma ɗaukaka martabar Nijeriya a duniya.

 

“Cibiyar Hulɗa da Jama’a ta Nijeriya ta daɗe tana zama ginshiƙin nagarta, tana ba da horo, ba da shaida, da kuma tsarin ɗa’a a fagen hulɗa da jama’a.

 

“Ta hanyar ƙoƙarin ta, NIPR ta samar da ƙwararrun masana da ke ci gaba da taka rawa wajen gina ƙasa,” inji shi.

 

Ya yaba wa shugabannin NIPR bisa jajircewar su wajen ciyar da wannan aiki gaba tare da jaddada aniyar Gwamnatin Tarayya na samar da ingantacciyar hanyar sadarwa a matsayin ginshiƙin shugabanci na gari.

 

Ya ce: “A matsayi na na Mai Girma Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, na himmatu wajen tabbatar da cewa tsarin sadarwar mu na da inganci, da gaskiya, kuma sun dace da ingantattun ayyuka.

 

“Wannan rantsarwar ta yi daidai da babban burin mu na ƙarfafa iyawar jami’an watsa labarai a duk sassan gwamnati domin su yi hulɗa da jama’a da kuma daƙile yaɗa labaran ƙarya yadda ya kamata.”

 

Ministan ya buƙaci waɗanda aka rantsar ɗin da su kiyaye ƙwarewa da riƙon amana, musamman a zamanin gidan yana, inda ya bayyana rawar da suke takawa a matsayin mai muhimmanci ga haɗin kan ƙasa da kuma bunƙasa al’adun gargajiyar Nijeriya.

 

“Ga sababbin membobin da aka rantsar, yau ne farkon wani sabon babi a tafiyar ku ta aiki.

 

“Aikin ku ba wai kawai yana nuna yadda ƙungiyarku ko cibiyar ku yake ba; yana nuni ga ɗaukacin al’ummar ƙasar. Ku kiyaye ƙa’idojin NIPR kuma ku kasance jakadun gaskiya da nagarta,” inji shi.

 

Da yake jawabi a wurin taron, Shugaban Cibiyar Hulɗa da Jama’a ta Nijeriya (NIPR), Dakta Ike Neliaku, ya bayyana jin daɗin sa da shigar da sabbin mambobi cikin cibiyar.

 

Shugaban ya jaddada muhimmancin aikin hulɗa da jama’a, inda ya ce, “Ba sa’a kawai kuka yi ba, haƙiƙa kun samu albarka, domin a yanzu kun shiga cikin aikin fitattun mutane, aiki ɗaya tilo da ba ya tsufa, aiki ɗaya tilo da ke mu ku jagorar samun abubuwa mafi kyawu daga rayuwa.”

 

Shugaban ya miƙa godiyar sa ga Ministan Yaɗa Labarai bisa rawar da ya taka wajen inganta harkar hulɗa da jama’a.

 

Ya bayyana ƙoƙarin da Ministan ya yi wajen ganin an amince da hulɗa da jama’a a matsayin aiki a aikin gwamnati.

 

“A shekarar da ta gabata, ya ɗauki nauyin rubutawa majalisa ta 45 kan kafawar a Bauchi, kuma a ranar 13 ga Disamba, 2023, majalisar ta yi la’akari da wannan takardar kuma ta amince da shi,” inji shugaban.

 

“Wannan wani muhimmin cigaba ne ga aikin mu, saboda yana nuna mahimmancin sadarwa mai inganci a cikin shugabanci.”

 

Ya nanata muhimmancin jami’an hulɗa da jama’a wajen samar da amana da fahimtar juna tsakanin gwamnati da jama’a.

 

“Idan aka yi hulɗa da jama’a yadda ya kamata, za su mallaki shirye-shiryen gwamnati. Idan aka yi hulɗa da jama’a yadda ya kamata, suna ba da shawarar abin da ya kamata a yi. Idan aka bai wa ‘yan kasa damar bayyana ra’ayoyinsu, yana da matuƙar amfani wajen samar da daidaito,” inji shi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Rundunar Sojin Sama Ta Kai Hari Kan ISWAP Da Ƴan Bindiga A Borno, Kwara Da Katsina
Manyan Labarai

Rundunar Sojin Sama Ta Kai Hari Kan ISWAP Da Ƴan Bindiga A Borno, Kwara Da Katsina

November 10, 2025
Gwamnatin Kaduna Za Ta Ɗauki Ma’aikatan Lafiya 9,000 Cikin Shekaru 5 – Maiyaki 
Labarai

Gwamnatin Kaduna Za Ta Ɗauki Ma’aikatan Lafiya 9,000 Cikin Shekaru 5 – Maiyaki 

November 10, 2025
Da Dumi-duminsa: ‘Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Basarake A Ondo
Labarai

Wani Sabon Hari Kan Al’ummar Da Ke Iyaka Da Katsina A Kano Ya Rutsa Da Mata 5

November 10, 2025
Next Post
Yaki Da Talauci: Yadda Kasar Sin Ke Taka Rawar Gani A Duniya 

Yaki Da Talauci: Yadda Kasar Sin Ke Taka Rawar Gani A Duniya 

LABARAI MASU NASABA

Rundunar Sojin Sama Ta Kai Hari Kan ISWAP Da Ƴan Bindiga A Borno, Kwara Da Katsina

Rundunar Sojin Sama Ta Kai Hari Kan ISWAP Da Ƴan Bindiga A Borno, Kwara Da Katsina

November 10, 2025
Xi Ya Halarci Bikin Bude Gasar Wasanni Ta Sin Karo Na 15 A Guangzhou

Xi Ya Halarci Bikin Bude Gasar Wasanni Ta Sin Karo Na 15 A Guangzhou

November 10, 2025
Gwamnatin Kaduna Za Ta Ɗauki Ma’aikatan Lafiya 9,000 Cikin Shekaru 5 – Maiyaki 

Gwamnatin Kaduna Za Ta Ɗauki Ma’aikatan Lafiya 9,000 Cikin Shekaru 5 – Maiyaki 

November 10, 2025
Da Dumi-duminsa: ‘Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Basarake A Ondo

Wani Sabon Hari Kan Al’ummar Da Ke Iyaka Da Katsina A Kano Ya Rutsa Da Mata 5

November 10, 2025
Matatun mai

Yadda Sojoji Suka Tarwatsa Haramtattun Matatun Mai 14 A Yankin Neja Delta 

November 10, 2025
Jibrin Kofa

Ɗan Majalisar Wakilai, Jibrin Ƙofa Ya Sauya Sheƙa Daga NNPP Zuwa APC

November 10, 2025
Boko haram

Sojoji Sun Fatattaki Boko Haram, Sun Ceto Mutane 86 Da Aka Sace A Borno

November 10, 2025
Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

November 9, 2025
An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

November 9, 2025
Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL

Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL

November 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.