• English
  • Business News
Wednesday, June 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Minista Ya Buƙaci Sabbin Shugabannin NIPR Su Faɗakar da Jama’a Yadda Ya Dace 

by Sulaiman
6 months ago
in Labarai
0
Minista Ya Buƙaci Sabbin Shugabannin NIPR Su Faɗakar da Jama’a Yadda Ya Dace 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya buƙaci sabbin mambobin Cibiyar Hulɗa da Jama’a ta Nijeriya (NIPR) da su gudanar da harkokin sadarwa yadda ya dace da kuma bayar da gudunmawa ga cigaban ƙasa.

 

Ministan wanda ya samu wakilcin Daraktan Yaɗa Labarai da Hulɗa da Jama’a, Dakta Sulaiman Haruna, ya bayyana hakan ne a wajen taron rantsar da sababbin jami’an yaɗa labarai da hulɗa da jama’a da aka gudanar a Ma’aikatar Yaɗa Labarai ta Tarayya, Abuja.

  • Sanatocin Kudu Maso Gabas Sun Bukaci Duba Kudirin Dokar Gyaran Haraji
  • Netanyahu Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Zargin Rashawa

A nasa jawabin, Ministan ya jaddada muhimmiyar rawar da hulɗa da jama’a ke takawa wajen tabbatar da gaskiya da riƙon amana tsakanin gwamnati da ‘yan ƙasa.

 

Labarai Masu Nasaba

An Kama Mutane 26 Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Kogi

Majalisar Wakilai Ta Fara Binciken Yadda Aka Raba Naira Tiriliyan 1.12 Kan Shirin Lamuni Ga Manoma Da Masana’antu

Ya buƙaci waɗanda aka rantsar da su yi amfani da basirar su da ilimin su wajen daƙile yaɗa labaran ƙarya, inganta haɗin kai, da kuma ɗaukaka martabar Nijeriya a duniya.

 

“Cibiyar Hulɗa da Jama’a ta Nijeriya ta daɗe tana zama ginshiƙin nagarta, tana ba da horo, ba da shaida, da kuma tsarin ɗa’a a fagen hulɗa da jama’a.

 

“Ta hanyar ƙoƙarin ta, NIPR ta samar da ƙwararrun masana da ke ci gaba da taka rawa wajen gina ƙasa,” inji shi.

 

Ya yaba wa shugabannin NIPR bisa jajircewar su wajen ciyar da wannan aiki gaba tare da jaddada aniyar Gwamnatin Tarayya na samar da ingantacciyar hanyar sadarwa a matsayin ginshiƙin shugabanci na gari.

 

Ya ce: “A matsayi na na Mai Girma Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, na himmatu wajen tabbatar da cewa tsarin sadarwar mu na da inganci, da gaskiya, kuma sun dace da ingantattun ayyuka.

 

“Wannan rantsarwar ta yi daidai da babban burin mu na ƙarfafa iyawar jami’an watsa labarai a duk sassan gwamnati domin su yi hulɗa da jama’a da kuma daƙile yaɗa labaran ƙarya yadda ya kamata.”

 

Ministan ya buƙaci waɗanda aka rantsar ɗin da su kiyaye ƙwarewa da riƙon amana, musamman a zamanin gidan yana, inda ya bayyana rawar da suke takawa a matsayin mai muhimmanci ga haɗin kan ƙasa da kuma bunƙasa al’adun gargajiyar Nijeriya.

 

“Ga sababbin membobin da aka rantsar, yau ne farkon wani sabon babi a tafiyar ku ta aiki.

 

“Aikin ku ba wai kawai yana nuna yadda ƙungiyarku ko cibiyar ku yake ba; yana nuni ga ɗaukacin al’ummar ƙasar. Ku kiyaye ƙa’idojin NIPR kuma ku kasance jakadun gaskiya da nagarta,” inji shi.

 

Da yake jawabi a wurin taron, Shugaban Cibiyar Hulɗa da Jama’a ta Nijeriya (NIPR), Dakta Ike Neliaku, ya bayyana jin daɗin sa da shigar da sabbin mambobi cikin cibiyar.

 

Shugaban ya jaddada muhimmancin aikin hulɗa da jama’a, inda ya ce, “Ba sa’a kawai kuka yi ba, haƙiƙa kun samu albarka, domin a yanzu kun shiga cikin aikin fitattun mutane, aiki ɗaya tilo da ba ya tsufa, aiki ɗaya tilo da ke mu ku jagorar samun abubuwa mafi kyawu daga rayuwa.”

 

Shugaban ya miƙa godiyar sa ga Ministan Yaɗa Labarai bisa rawar da ya taka wajen inganta harkar hulɗa da jama’a.

 

Ya bayyana ƙoƙarin da Ministan ya yi wajen ganin an amince da hulɗa da jama’a a matsayin aiki a aikin gwamnati.

 

“A shekarar da ta gabata, ya ɗauki nauyin rubutawa majalisa ta 45 kan kafawar a Bauchi, kuma a ranar 13 ga Disamba, 2023, majalisar ta yi la’akari da wannan takardar kuma ta amince da shi,” inji shugaban.

 

“Wannan wani muhimmin cigaba ne ga aikin mu, saboda yana nuna mahimmancin sadarwa mai inganci a cikin shugabanci.”

 

Ya nanata muhimmancin jami’an hulɗa da jama’a wajen samar da amana da fahimtar juna tsakanin gwamnati da jama’a.

 

“Idan aka yi hulɗa da jama’a yadda ya kamata, za su mallaki shirye-shiryen gwamnati. Idan aka yi hulɗa da jama’a yadda ya kamata, suna ba da shawarar abin da ya kamata a yi. Idan aka bai wa ‘yan kasa damar bayyana ra’ayoyinsu, yana da matuƙar amfani wajen samar da daidaito,” inji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Jinping Ya Gana Da Manyan Jami’An Muhimman Kungiyoyin Tattalin Arziki Na Kasa Da Kasa

Next Post

Yaki Da Talauci: Yadda Kasar Sin Ke Taka Rawar Gani A Duniya 

Related

An Kama Mutane 26 Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Kogi
Labarai

An Kama Mutane 26 Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Kogi

5 hours ago
Majalisar Wakilai Ta Fara Binciken Yadda Aka Raba Naira Tiriliyan 1.12 Kan Shirin Lamuni Ga Manoma Da Masana’antu
Manyan Labarai

Majalisar Wakilai Ta Fara Binciken Yadda Aka Raba Naira Tiriliyan 1.12 Kan Shirin Lamuni Ga Manoma Da Masana’antu

7 hours ago
Kaftin Din Super Eagles, Ahmed Musa Ya Bukaci A Gaggauta Kawo Karshen Kashe-kashen Rayuka A Benuwe
Labarai

Kaftin Din Super Eagles, Ahmed Musa Ya Bukaci A Gaggauta Kawo Karshen Kashe-kashen Rayuka A Benuwe

9 hours ago
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

2025 UTME: Cibiyoyin Zana Jarabawar 11 Na Fuskantar Barazanar Dakatarwa – JAMB

11 hours ago
Daga Taklimakan Zuwa Sahara: Karin Abubuwan Al’ajabi Na Faruwa Bisa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Yaki Da Kwararar Hamada
Ra'ayi Riga

Daga Taklimakan Zuwa Sahara: Karin Abubuwan Al’ajabi Na Faruwa Bisa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Yaki Da Kwararar Hamada

12 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Kashe Jami’an Tsaro 4 Da Manoma A Katsina
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe Jami’an Tsaro 4 Da Manoma A Katsina

14 hours ago
Next Post
Yaki Da Talauci: Yadda Kasar Sin Ke Taka Rawar Gani A Duniya 

Yaki Da Talauci: Yadda Kasar Sin Ke Taka Rawar Gani A Duniya 

LABARAI MASU NASABA

Dalilin Da Ya Sa Sin Ta Samu Bunkasar Tattalin Arziki Mai Dorewa Duk Da Kalubalolin Da Ake Fuskanta A Duniya

Dalilin Da Ya Sa Sin Ta Samu Bunkasar Tattalin Arziki Mai Dorewa Duk Da Kalubalolin Da Ake Fuskanta A Duniya

June 17, 2025
An Kama Mutane 26 Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Kogi

An Kama Mutane 26 Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Kogi

June 17, 2025
Xi Da Shugabannin Kasashe 5 Na Tsakiyar Asiya Sun Halarci Bikin Rattaba Hannu

Xi Da Shugabannin Kasashe 5 Na Tsakiyar Asiya Sun Halarci Bikin Rattaba Hannu

June 17, 2025
Sin Ta Cimma Sabuwar Nasarar Bincike Duniyar Wata

Sin Ta Cimma Sabuwar Nasarar Bincike Duniyar Wata

June 17, 2025
Majalisar Wakilai Ta Fara Binciken Yadda Aka Raba Naira Tiriliyan 1.12 Kan Shirin Lamuni Ga Manoma Da Masana’antu

Majalisar Wakilai Ta Fara Binciken Yadda Aka Raba Naira Tiriliyan 1.12 Kan Shirin Lamuni Ga Manoma Da Masana’antu

June 17, 2025
An Gudanar Da Bikin Mu’amalar Jama’a Da Al’adu A Tsakanin Sin Da Tsakiyar Asiya A Astana

An Gudanar Da Bikin Mu’amalar Jama’a Da Al’adu A Tsakanin Sin Da Tsakiyar Asiya A Astana

June 17, 2025
Kaftin Din Super Eagles, Ahmed Musa Ya Bukaci A Gaggauta Kawo Karshen Kashe-kashen Rayuka A Benuwe

Kaftin Din Super Eagles, Ahmed Musa Ya Bukaci A Gaggauta Kawo Karshen Kashe-kashen Rayuka A Benuwe

June 17, 2025
Masu Karanta Adabin Shafin Intanet Na Sin Sun Kai Miliyan 575

Masu Karanta Adabin Shafin Intanet Na Sin Sun Kai Miliyan 575

June 17, 2025
Sin Ta Fara Aiwatar Da Matakin Soke Haraji Kan Kayayyakin Kasashen Afirka 53

Sin Ta Fara Aiwatar Da Matakin Soke Haraji Kan Kayayyakin Kasashen Afirka 53

June 17, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

2025 UTME: Cibiyoyin Zana Jarabawar 11 Na Fuskantar Barazanar Dakatarwa – JAMB

June 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.