• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Minista Ya Ce Kirkirarriyar Basira ‘AI’ Za Ta Taimaka Wajen Kare Makarantu

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
Minista Ya Ce Kirkirarriyar Basira ‘AI’ Za Ta Taimaka Wajen Kare Makarantu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Karamin Ministan Ilimi, Dakta Yusuf Tanko Sununu, ya jaddada cewa amfani da kirkirarriyar basira (Artificial Intelligence) zai bunkasa da kyautata fasahohin da ake da su a bangaren koyarwa da tsaron makarantu.

Wanda ke magana a wajen taron kwararru kan fasahar sadarwar zamani na 2024 karo na goma sha takwas da ya gudana a Abuja.
A cewarsa, “Amfani da basirar AI a dukkanin makarantunmu zai taimaka mana wajen koyarwa, bibiya da kuma tabbatar da makarantunmu suna cikin tsaro.”

  • Ana Fargabar Shigo Da Shinkafar Da Ta Jima A Ajiye Daga Thailand
  • Ana Samun Saukin Yaduwar Bakuwar Cutar Da Ta Barke A Zamfara

Ya ce, akwai gayar bukatar amfani da fasahohin zamani ciki kuwa har da na AI wajen karfafa wa sintiri da sanya ido kan muhallan makarantu, a cewarsa, “Ya zama dole a garemu mu rungumi yadda za mu tafiya da fasahohi, ciki har da na AI wajen aza tubalin bibiya da ayyukan sirri na tsawo da za su kaimu ga kare makarantunmu.”

Ya nemi taron kwararrun da cewa zai bullo da wasu hanyoyi da shawarorin yadda za su taimaka wa gwamnati wajen zuba na’urorin zamani kuma a tabbatar da sun yi aiki bisa hadin guiwa domin kyautata tattalin arziki, matakin fasaha, da wayar da kai kan tsaron kasar nan.

“Mun gani kuma muna kan ganin alfanu da fa’idar fasahar sadarwar zamani (IT) a karni na 21 da kuma irin rawar da take takawa wajen kyautata tattalin arzikin duniya.
“Mun kuma gano irin tasirin da take da shi wajen fadadawa da saukaka hanyoyin samun ilimi a dukkanin matakai,” ya shaida.

Labarai Masu Nasaba

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Ministan ya tabbatar da cewa gwamnatin tarayya a shirye take ta bi dukkanin matakan da suka dace wajen amfani da fasaha don ganin an samu nasarar bunkasa cigaba da rungumar fasahar sadarwar zamani a tsarin ilimin Nijeriya.

“Gwamnatin tarayya ta dukufa wajen ganin ta kai Nijeriya da ajiyeta a matsayin shugaba a duniya, musamman a Afrika. Bangaren fasahar sadarwar zamani na taka muhimmiyar rawa wajen cimma wannan manufar da gwamnati ta sanya a gaba,” Sununu ya shaida.

Ya bukaci kwararrun da su mara wa yunkuri da shirin gwamnati baya gami da bada nasu gudunmawar domin cigaba da daurewar tattalin arzikin kasar nan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Da Hannun Nuhu Ribaɗo Wajen Yunƙurin Dawo Da Aminu Ado Sarauta

Next Post

Hukumomin Tsaro A Kano Sun Ƙi Biyayya Ga Umarnin Gwamnan Kano

Related

Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC
Labarai

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

1 hour ago
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa
Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

2 hours ago
Sojoji
Labarai

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

3 hours ago
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya
Labarai

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

4 hours ago
NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
Manyan Labarai

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

6 hours ago
Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci
Ra'ayi Riga

Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

7 hours ago
Next Post
Hukumomin Tsaro A Kano Sun Ƙi Biyayya Ga Umarnin Gwamnan Kano

Hukumomin Tsaro A Kano Sun Ƙi Biyayya Ga Umarnin Gwamnan Kano

LABARAI MASU NASABA

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

September 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

September 16, 2025
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

September 16, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

September 16, 2025
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

September 16, 2025
Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

September 16, 2025
NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.