• English
  • Business News
Tuesday, October 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Minista Ya Gargaɗi Jami’an Gwamnati Kan Rashin Sanin Ilimin Tantance Ingantattun Labarai

by Sulaiman
6 months ago
Labarai

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya yi gargaɗin cewa jami’an gwamnati da ba su da ilimi kan kafofin watsa labarai suna cikin haɗarin faɗawa tarkon yarda da labaran ƙarya.

 

Mataimaki na musamman ga Ministan kan yaɗa labarai, Rabiu Ibrahim, ya faɗa a takardar sanarwa ga manema labarai cewa Idris ya yi wannan bayanin ne a ranar Talata a birnin Abuja, a wajen Taron Masu Magana da Yawu karo na biyu wanda Cibiyar Ƙwararrun Masana Hulɗa da Jama’a ta Nijeriya (NIPR) ta shirya tare da haɗin gwiwar Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da Kai.

  • CMG Ta Kulla Yarjejeniyar Hadin Gwiwa Da Gidan Talabijin Na Kasar Vietnam
  • Kotu Ta Tsare Matasa 2 Kan Wallafa Bidiyon Batsa A TikTok A Kano

Ya ce: “Ina so in yi amfani da wannan dama ta wannan taron na ƙwararru domin jaddada muhimmancin rungumar abin da ake kira ‘Information and Media Literacy’, wata haɗaɗɗiyar ƙwarewa da Ƙungiyar Ilimi, Kimiyya, da Al’adu ta Majalisar Ɗinkin Duniya (UNESCO) ta fara gabatarwa a shekarar 2008, wadda ke haɗa dabarun fahimtar bayanai da fahimtar kafofin watsa labarai.”

 

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Mutum 3, Wasu 7 Sun Jikkata Sakamakon Ɓarkewar Rikici A Jihar Jigawa

Rashin Tsaro A Nijeriya Ba Zai Ƙare Ba Matuƙar Ba A Samar da Ayyukan Yi Da Mulki Na Adalci Ba – Amaechi

A cewar Ministan, samun wannan ƙwarewar ya zama wajibi a wannan zamani da kowa da kowa – wato daga masana hulɗa da jama’a zuwa shugabannin kamfanoni – yake taka rawa a matsayin mai magana da yawun wani.

 

Idris ya ce: “Yau a wannan zamani da kowa ke zama mai magana da yawu – ko ɗan hulɗa da jama’a ne ko shugaban kamfani a ɓangaren gwamnati da masu zaman kan su – wajabcin samun ilimi kan kafofin watsa labarai ya zama abu mai matuƙar muhimmanci, domin yana ba da damar fahimta, nazari da tantance sahihancin saƙonnin da ke yawo a kafafen watsa labarai, wanda hakan zai ba da damar yanke sahihin hukunci da mu’amala da labarai yadda ya kamata.

 

“A ‘yan kwanakin nan, saboda rashin wannan ilimi – wato rashin iya nazarin abin da ke cikin kafafen labarai da tantance sahihancin sa – jami’an gwamnati da ma al’umma gaba ɗaya sun fara faɗawa tarkon labaran ƙarya da yaɗa bayanan da ba su da tushe.”

 

Ya ce samun wannan ilimi zai ba da dama ga masu magana da yawun hukumomi su inganta dabarun su wajen tantance sahihancin labarai, gano son zuciya ko ɓangaranci a cikin su, da kuma amfani da hanyoyin bincike da tantance gaskiya.

 

Domin cimma wannan buri, Ministan ya bayyana cewa ma’aikatar sa ta kusa kammala shiri domin buɗe Cibiyar Ilimin Kafofin Watsa Labarai ta UNESCO – wacce za ta kasance ta farko a duniya – a Buɗaɗɗiyar Jami’ar Ƙasa ta Nijeriya (NOUN) da ke Abuja.

 

Ya ce: “Na dawo daga Paris, a ƙasar Faransa, kwanan nan inda na gana da manyan jami’an UNESCO, kuma buɗe wannan cibiyar ya kasance babban maudu’i a tattaunawar.”

 

Ministan ya kuma bayyana cewa ma’aikatar sa ta samu gagarumar nasara a bara, inda aka samar da sabon matsayi na “public relations” a cikin tsarin aikin Gwamnatin Tarayya.

 

“Abin da wannan ke nufi shi ne, ‘Public Relations’ yanzu yana da nasa hanyar aikin kai-tsaye a cikin aikin gwamnati tun daga watan Disamba 2023.

 

“Haka nan, tsohuwar muƙamin ‘Information Officer’ yanzu an sake masa suna zuwa ‘Information and Public Relations Officer’, da kuma ‘Executive Officer (Information and Public Relations)’.

 

“Ina kuma so in ƙara da cewa NIPR ce ta taka rawar gani wajen ganin wannan cigaba ya samu.”

 

Idris ya kuma jaddada cewa gwamnatin Tinubu za ta ci gaba da goyon bayan ‘yancin faɗar albarkacin baki da kuma ƙarfafa kafafen watsa labarai masu zaman kansu.

 

Ya ce: “A ɓangaren mu, za mu ci gaba da faɗaɗa hanyoyin sadarwa a ƙasar nan da kuma bunƙasa damar zuba jari da tattalin arziki da ke cikin ta.”

 

Har ila yau, Ministan ya yaba wa shugaban NIPR, Dakta Ike Neliaku, saboda ƙara sabon ɓangare mai muhimmanci a wannan taro, wato ‘Information Ministerial Clinic’, inda tsofaffin ministocin yaɗa labarai suka raba gogewar da suka samu da abubuwan da suka fuskanta yayin gudanar da aikin su.

 

Tsofaffin ministocin da suka halarci buɗaɗɗen taron sun haɗa da Farfesa Jerry Gana, Cif John Nwodo, Mista Frank Nweke (Jnr), Mista Labaran Maku, da Alhaji Lai Mohammed.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Kashe Mutum 3, Wasu 7 Sun Jikkata Sakamakon Ɓarkewar Rikici A Jihar Jigawa
Labarai

An Kashe Mutum 3, Wasu 7 Sun Jikkata Sakamakon Ɓarkewar Rikici A Jihar Jigawa

October 14, 2025
Rashin Tsaro A Nijeriya Ba Zai Ƙare Ba Matuƙar Ba A Samar da Ayyukan Yi Da Mulki Na Adalci Ba – Amaechi
Manyan Labarai

Rashin Tsaro A Nijeriya Ba Zai Ƙare Ba Matuƙar Ba A Samar da Ayyukan Yi Da Mulki Na Adalci Ba – Amaechi

October 14, 2025
Amnesty International Ta Soki Tinubu Kan Yi Wa Masu Laifin Take Haƙƙin Ɗan Adam Afuwa
Manyan Labarai

Amnesty International Ta Soki Tinubu Kan Yi Wa Masu Laifin Take Haƙƙin Ɗan Adam Afuwa

October 14, 2025
Next Post
UEFA: Barcelona Ta Kai Zagayen Kusa Da Karshe A Karon Farko Cikin Shekaru 9

UEFA: Barcelona Ta Kai Zagayen Kusa Da Karshe A Karon Farko Cikin Shekaru 9

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Majalisa 60 Sun Yi Barazanar Ficewa Daga PDP

PDP Ta Ɗage Babban Taronta Biyo Bayan Ficewar Wasu Manyan Jiga-jigai

October 14, 2025
An Kashe Mutum 3, Wasu 7 Sun Jikkata Sakamakon Ɓarkewar Rikici A Jihar Jigawa

An Kashe Mutum 3, Wasu 7 Sun Jikkata Sakamakon Ɓarkewar Rikici A Jihar Jigawa

October 14, 2025
Rashin Tsaro A Nijeriya Ba Zai Ƙare Ba Matuƙar Ba A Samar da Ayyukan Yi Da Mulki Na Adalci Ba – Amaechi

Rashin Tsaro A Nijeriya Ba Zai Ƙare Ba Matuƙar Ba A Samar da Ayyukan Yi Da Mulki Na Adalci Ba – Amaechi

October 14, 2025
Amnesty International Ta Soki Tinubu Kan Yi Wa Masu Laifin Take Haƙƙin Ɗan Adam Afuwa

Amnesty International Ta Soki Tinubu Kan Yi Wa Masu Laifin Take Haƙƙin Ɗan Adam Afuwa

October 14, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Ɗan Jarida A Kan Hanyarsa Ta Zuwa Ɗaukar Horo A Kwara

‘Yan Bindiga Sun Sace Ɗan Jarida A Kan Hanyarsa Ta Zuwa Ɗaukar Horo A Kwara

October 14, 2025
Zaman Gidan Yari Ya Nuna Min Mutanen Da Ya Kamata Na Yi Hulɗar Siyasa Da Su — Faruk Lawan

Zaman Gidan Yari Ya Nuna Min Mutanen Da Ya Kamata Na Yi Hulɗar Siyasa Da Su — Faruk Lawan

October 14, 2025
Majalisa Na Shirin Sauya Lokacin Zaɓen 2027 Zuwa Nuwamba 2026

Majalisa Na Shirin Sauya Lokacin Zaɓen 2027 Zuwa Nuwamba 2026

October 13, 2025
Yajin Aiki: Malaman Jami’a Sun Ce Barazanar ‘Ba Aiki, Ba Biya’ Ba Zata Tsorata Su Ba

Yajin Aiki: Malaman Jami’a Sun Ce Barazanar ‘Ba Aiki, Ba Biya’ Ba Zata Tsorata Su Ba

October 13, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba

October 13, 2025
Matakan Da Sin Ta Dauka Na Mai Da Martani Ga Bincike Mai Lamba “301” Da Amurka Ta Gudanar Sun Zama Wajibi Don Kare Hakkinta

Matakan Da Sin Ta Dauka Na Mai Da Martani Ga Bincike Mai Lamba “301” Da Amurka Ta Gudanar Sun Zama Wajibi Don Kare Hakkinta

October 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.