Ministan harkokin wajen kasar Sin Qin Gang, ya yi kira da a yi kokarin sa kaimi ga bunkasuwar dunkulewar duniya baki daya, da karfafa hadin gwiwar bangarori daban-daban a yayin taron ministocin harkokin wajen kasashen G20 da ake yi a New Delhin kasar Indiya
Yayin da yake gabatar da jawabin karfafa hadin gwiwar bangarori daban-daban da inganta ci gaban duniya a yayin taron Alhamis din nan, Qin ya bukaci manyan kasashe masu karfin tattalin arziki, da su dauki nauyin yin aiki tare domin ci gaban duniya da samun wadata. (Ibrahim Yaya)
ADVERTISEMENT














