ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, November 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Babban Limamin Masallacin Minna

by Sulaiman
12 months ago
Masallacin Minna

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya jajanta wa al’ummar Musulmin garin Minna da Gwamnatin Jihar Neja bisa rasuwar Babban Limamin Masallacin Minna, Sheikh Isah Fari.

 

A cikin wata sanarwa da Mataimakin sa na Musamman kan Harkokin Yaɗa Labarai, Rabiu Ibrahim ya fitar, ministan ya bayyana marigayi Sheikh Fari wanda ya rasu yana da shekaru 93 a duniya a matsayin babban malamin addini wanda ya sadaukar da rayuwar sa wajen bautar Allah, yaɗa Musulunci, da kuma inganta zaman lafiya a Jihar Neja da ma ƙasar baki ɗaya.

ADVERTISEMENT
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci ‘Yansanda Su Rungumi Yarjejeniyar Ɗa’a ta Ƙasa
  • ‘Yan Bindiga Sun Kone Gonakin Manoma A Zamfara

Ya ce: “Marigayi Sheikh Isah Fari ya nuna maƙasudin addinin Musulunci, wanda shi ne fifikon zaman lafiya da haɗin kai a tsakanin al’umma, ta yadda a shekarun da ya yi yana matsayin Babban Limamin Babban Masallacin Minna an ɗauke shi a matsayin wanda ke jaddada zaman lafiya da kwanciyar hankali a Jihar Neja.”

 

LABARAI MASU NASABA

MACBAN Ta Nemi Amurka Ta Cire Sunanta Daga Jerin Waɗanda Ta Ƙaƙabawa Takunkumi

Bai Dace Adalci Ya Zama Na Sayarwa Ba – Tinubu Ga Alƙalai 

Idris ya miƙa ta’aziyyar sa ga Gwamnan Jihar Neja, Alhaji Umaru Bago, da Sarkin Minna, Alhaji Dakta Umar Faruq Bahago, tare da jaddada gagarumar gudunmawar da marigayi Babban Limamin ya bayar wajen bunƙasa zamantakewa da tattalin arzikin Masarautar Minna da Jihar Neja.

 

Ya ce: “Ina miƙa alhini na ga Gwamnan Jihar Neja, Mai Girma Umaru Bago, da Sarkin Minna, Mai Martaba Sarkin Minna, Alhaji Dr Umar Faruq Bahago, bisa rashin wani masani wanda ilimin sa ya zame tushe na shawarwari masu inganci don cigaban zamantakewa da tattalin arzikin masarautar Minna da Jihar Neja baki ɗaya.”

 

Ministan ya buƙaci al’ummar Jihar Neja da su kiyaye koyarwar soyayya, haƙuri da juna da haɗin kai da Sheikh Fari ya bayar a lokacin rayuwar sa, tare da yin addu’ar Allah ya jiƙan marigayin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Labarai

MACBAN Ta Nemi Amurka Ta Cire Sunanta Daga Jerin Waɗanda Ta Ƙaƙabawa Takunkumi

November 17, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Bai Dace Adalci Ya Zama Na Sayarwa Ba – Tinubu Ga Alƙalai 

November 17, 2025
Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC
Manyan Labarai

Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC

November 17, 2025
Next Post
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

Gwamnati Ta Ɗage Haramcin Tura Masu Yi Wa Ƙasa Hidima Bankuna Da Sauran Masana’antu 

LABARAI MASU NASABA

An Sanya Hannu Kan Yarjejeniyoyin Cinikayya Na Biliyoyin Kudi Yayin Baje Kolin CHTF Na Kasar Sin

An Sanya Hannu Kan Yarjejeniyoyin Cinikayya Na Biliyoyin Kudi Yayin Baje Kolin CHTF Na Kasar Sin

November 17, 2025

MACBAN Ta Nemi Amurka Ta Cire Sunanta Daga Jerin Waɗanda Ta Ƙaƙabawa Takunkumi

November 17, 2025
Tinubu

Bai Dace Adalci Ya Zama Na Sayarwa Ba – Tinubu Ga Alƙalai 

November 17, 2025
Tsohon Firaministan Japan Ya Soki Kalaman Takaichi Dangane Da Batun Yankin Taiwan

Tsohon Firaministan Japan Ya Soki Kalaman Takaichi Dangane Da Batun Yankin Taiwan

November 17, 2025
Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC

Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC

November 17, 2025
Hakimi, Osimhen Da Salah Ƴan Wasan Da Ke Takara A Ƙyautar Gwarzon Afrika

Hakimi, Osimhen Da Salah Ƴan Wasan Da Ke Takara A Ƙyautar Gwarzon Afrika

November 17, 2025
Tsohuwar Firaministan Bangaladesh Sheikha Hasina,

An Yanke Wa Tsohuwar Shugabar Bangladesh Hukuncin Kisa

November 17, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi

Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi

November 17, 2025
Mutane 42 Sun Mutu A Wani Hatsarin Tankar Dizal Da Motar Masu Umrah A Hanyar Makka

Mutane 42 Sun Mutu A Wani Hatsarin Tankar Dizal Da Motar Masu Umrah A Hanyar Makka

November 17, 2025
Ba Mu Samu Labarin Kai Wa Laftanar Yerima Hari Ba – Ƴansanda

Ba Mu Samu Labarin Kai Wa Laftanar Yerima Hari Ba – Ƴansanda

November 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.