• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Babban Limamin Masallacin Minna

by Sulaiman
12 months ago
Masallacin Minna

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya jajanta wa al’ummar Musulmin garin Minna da Gwamnatin Jihar Neja bisa rasuwar Babban Limamin Masallacin Minna, Sheikh Isah Fari.

 

A cikin wata sanarwa da Mataimakin sa na Musamman kan Harkokin Yaɗa Labarai, Rabiu Ibrahim ya fitar, ministan ya bayyana marigayi Sheikh Fari wanda ya rasu yana da shekaru 93 a duniya a matsayin babban malamin addini wanda ya sadaukar da rayuwar sa wajen bautar Allah, yaɗa Musulunci, da kuma inganta zaman lafiya a Jihar Neja da ma ƙasar baki ɗaya.

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci ‘Yansanda Su Rungumi Yarjejeniyar Ɗa’a ta Ƙasa
  • ‘Yan Bindiga Sun Kone Gonakin Manoma A Zamfara

Ya ce: “Marigayi Sheikh Isah Fari ya nuna maƙasudin addinin Musulunci, wanda shi ne fifikon zaman lafiya da haɗin kai a tsakanin al’umma, ta yadda a shekarun da ya yi yana matsayin Babban Limamin Babban Masallacin Minna an ɗauke shi a matsayin wanda ke jaddada zaman lafiya da kwanciyar hankali a Jihar Neja.”

 

LABARAI MASU NASABA

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

Idris ya miƙa ta’aziyyar sa ga Gwamnan Jihar Neja, Alhaji Umaru Bago, da Sarkin Minna, Alhaji Dakta Umar Faruq Bahago, tare da jaddada gagarumar gudunmawar da marigayi Babban Limamin ya bayar wajen bunƙasa zamantakewa da tattalin arzikin Masarautar Minna da Jihar Neja.

 

Ya ce: “Ina miƙa alhini na ga Gwamnan Jihar Neja, Mai Girma Umaru Bago, da Sarkin Minna, Mai Martaba Sarkin Minna, Alhaji Dr Umar Faruq Bahago, bisa rashin wani masani wanda ilimin sa ya zame tushe na shawarwari masu inganci don cigaban zamantakewa da tattalin arzikin masarautar Minna da Jihar Neja baki ɗaya.”

 

Ministan ya buƙaci al’ummar Jihar Neja da su kiyaye koyarwar soyayya, haƙuri da juna da haɗin kai da Sheikh Fari ya bayar a lokacin rayuwar sa, tare da yin addu’ar Allah ya jiƙan marigayin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma
Manyan Labarai

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP
Labarai

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu!
Rahotonni

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

November 7, 2025
Next Post
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

Gwamnati Ta Ɗage Haramcin Tura Masu Yi Wa Ƙasa Hidima Bankuna Da Sauran Masana’antu 

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

November 7, 2025
An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

November 7, 2025
Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

November 7, 2025
APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025
Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.