• English
  • Business News
Wednesday, October 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mohammed Idris Malagi A Ma’aunin Siyasa

by Sulaiman and Jibrin Baba Ndace
3 years ago
Malagi

An shafe shekaru masu yawa, tun ma kafin samun ‘yancin Nijeriya, fitattun ‘yan jarida da mawallafa su na taka muhimmiyar rawa a harkokin siyasar ƙasar nan. Sun tsunduma siyasa ne baya ga ayyukan sadaukarwar da su ka riƙa yi wa jama’a a gidajen jaridu. A duniya ma masu kafafen yaɗa labarai sun zama mashahuran shugabanni da manyan ‘yan siyasa.

Kafin ma a samu ‘yanci kafafen yaɗa labarai sun kasance masu bayar da gagarumar gudunmawar neman ‘yanci. Kuma masu kafafen yaɗa labaran nan da ‘yan jarida sun yi rawar gani sosai a manyan muƙaman siyasa. Kafin samun ‘yanci an samu bayyanar manyan masu damawa a harkokin jarida sun zama mashahuran ‘yan siyasa, wato Sa Herbert Macaulay da Dakta Nnamdi Azikiwe, wanda shi ne ya zama Shugaban Ƙasa na farko a ranar da Nijeriya ta samu ‘yanci, wato 1 ga Oktoba, 1960.

  • Jami’an Tsaro Sun Kubutar Da Mutum Bakwai Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Kaduna

Fitattun ‘yan jarida da masu gidajen jaridu sun ci gaba da kutsawa cikin harkokin siyasa, tun daga wancan lokacin har zuwa yau, inda a Jamhuriya ta Biyu aka samu biyu daga cikin su sun yi nasarar zama gwamna: Lateef Jakande ya zama Gwamnan Jihar Legas, Segun Osoba kuma ya zama na Jihar Ogun.

Waɗansun su kuma da dama sun riƙe muƙamai daban-daban, tun daga ‘yan majalisa, ciyamomi da kansiloli, ko kuma sun riƙe shugabancin wasu hukumomi da cibiyoyi.

A cikin Oktoba 2019, mawallafin jaridun Blueprint da Manhaja, Alhaji Mohammed Idris Malagi, ya yanke shawarar shiga wancan daji na siyasa da manyan ‘yan jarida da mawallafa su ka keta. Da ya shiga kuwa, ya fito gadan-gadan neman muƙamin siyasa. Tun daga lokacin kuwa tafiya mai nisan zangon watanni 31 ana tuntuɓar jama’a, ganawa, kamun-ƙafa da tattauna yadda za a kai ga cimma nasara.

LABARAI MASU NASABA

Babu Rikici A Jam’iyyar APC A Nasarawa — Shugaban Jam’iyya

Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu

Lokacin da Malagi ya fito, wasu mutane sun riƙa cewa ya dai fito ne don ya tayar da ƙura kawai. Wasu ma cewa su ke yi wasa ya ke yi. Akwai kuma masu yi masa kallon mutumin da ya yi samun kuɗin da ake cewa ‘dare ɗaya Allah kan yi Bature’, wanda ya rasa yadda zai kashe kuɗin sa, wai shi ya sa ya shiga siyasa, kawai don ya yi ɓarusa. Akwai wasu da su ka riƙa yi masa kallon sabon-yanka-rake ne a siyasa, wanda a ganin su bai isa ya yi gasa da tsofaffin ‘yan alewar siyasa ba.

Dukkan waɗanda su ka riƙa tofa albarkacin bakin su dangane da shigar Malagi siyasa sun yi tsammanin da ya fara, za a neme shi a rasa, wato zai yi tashin kumfar gishirin Andurus. Sun yi tsammanin ya shiga ne kawai don neman suna.

Da ma haka aka riƙa yi masa irin wannan mummunar fassara lokacin da ya fara wallafa jaridar Blueprint. Saboda ya shiga harkar da ƙarfin sa, har ya girgiza waɗanda su ka fara yi masa kallon raini a lokacin. To irin haka lamarin ya maimaita kan sa lokacin da ya shiga siyasa, inda manyan masu ruwa da tsaki da masu ganin sai irin su wane da wane ke iya yin gwamna a Jihar Neja su ka riƙa yi masa kallon sabon-shiga.

Malagi ya shafe watanni 30 ana gwagwagwa da shi, inda ya jajirce, ya nuna cewa shi fa ya kawo ƙarfi, don haka ya fi wane ya girme ni.

Daga lokacin da ya fara zuwa lokacin da ya fara shiga cikin zukatan jama’ar sa, Alhaji Mohammed Idris ya shimfiɗa hajar siyasar sa a farfajiyar Jihar Neja, inda ya riƙa shelar siyasar da babu tashe-tashen hankula, a gefe ɗaya kuma ya na kutsawa garuruwa da lunguna ya na jaddada kamfen a bisa batutuwan da su ka shafi cigaban jiha da al’ummar ta baki ɗaya.

Yayin da sauran ‘yan siyasa su ka mayar da hankali su na yarfe da bankaura ta hanyar amfani da soshiyal midiya, su ka riƙa raba kawunan jama’a, shi kuwa ci gaba ya yi da yi wa jama’a albishir da muhimmancin haɗin kai domin a gina ƙasaitacciyar Jihar Neja.

Cikin wannan lokacin ya gana da masu ruwa da tsaki na kowace shiyya a jihar. Dalilin haka abin koyi hatta ga su kan su abokan adawar siyasa, waɗanda kafin shigar Malagi siyasa ba su iya zama inuwa ɗaya.

Malagi ya riƙa kai wa dattawan jiha ziyara, su da sarakunan gargajiya, shugabannin addinai da jagororin jama’ar yankunan karkara. Kuma ya jawo matasa, dattawa da maza da mata. Sannan ya riƙa yin la’akari sosai da masu ruwa da tsakin APC mai mulki a jihar.

Ya yi amfani da kuɗin sa da lokacin sa da tsarin tafiyar sa har ya yi nasarar ratsa zukatan ‘yan jam’iyyar APC reshen Jihar Neja. Ya taka rawa sosai wajen bai wa jam’iyyar gudunmawa. Akwai lokacin da ya bayar da gudunmawar motoci 31 da naira miliyan 43.

Lokacin da ya ke yankar tikitin takarar gwamna, Malagi, wanda a yanzu shi ne Kakaaki Nupe, ya nanata babban dalilin sa na neman tsayawa takarar gwamna. Ya ce: “Niyya ta domin ganin na ciyar da Jihar Neja gaba ta bunƙasa a fili ta ke. Idan na zama gwamna zan yi aiki tuƙuru, tun daga sa’ar farkon shiga ta ofis domin in zaƙulo zarata kuma ƙwararru daga cikin maza da mata, matasa, masu ilmi da marasa ilmi, manoma, masu sana’o’in hannu, ‘yan tireda, kai da kowa da kowa, domin su bayar da gudunmawar da za su iya bayarwa.”

Tun daga lokacin da ya fara tuntuɓar jama’a, bai taɓa yarda zuciya ta ɗebe shi ya yi abin da ya saɓa wa kyawawan halaye da ɗabi’un sa ba. Yayin da wasu ‘yan siyasar jihar su ka rungumi ‘yan daba, siyasar ƙiyayya, ramuwar gayya da ɓata sunan abokin hamayya, shi kuwa sai ya mai da hankali wajen kamfen ɗin rashin tayar da hankula, haɗin kai da zaman lafiya. Sai da ya tuntuɓi dukkan ‘yan takarar gwamna a ƙarƙashin APC na Jihar Neja. Kuma irin wannan albishir ya riƙa yaɗawa a lokacin ganawar sa da ƙananan hukumomi da mazaɓun ‘yan Majalisar Tarayya na jiha.

A rangadin da ya yi tun daga Lapai zuwa Agaie, zuwa Bida, Kutigi da Borgu, har Kontagora da Minna, ya riƙa ganawa da sarakunan gargajiya, shugabannin karkara da ‘yan siyasa, bai taɓa yin wani furuci da zai harzuƙa wasu ko ya yi kalamin da zai rura wutar jituwa ba.

Kakaaki Nupe ya yi takara kuma an fafata da shi sosai. Lokacin da sakamakon zaɓen bai yi masa daɗi ba, tangarɗar rashin gudanar da zaɓen kamar yadda ƙa’ida ta gindiya bai hana shi fara taya murna ga wanda aka bayyana da yin nasara ba. Ko a bayan zaɓen fidda-gwanin an riƙa yi wa Malagi kallon da bai kamata ba a cikin jiga-jigan APC na jihar, amma ya dake tare da kai zuciya nesa.

Rashin nasarar da ya yi bai hana shi cika wa Ƙungiyar ‘Yan Jarida ta Nijeriya (NUJ) reshen Jihar Neja alƙawarin motar da ya yi masu ba. A ziyarar godiya da su ka kai masa, ya ce shi ba shi da abokin gaba a ciki ko a wajen harkar siyasa.

Duk da yake an yi zaɓen fid da gwanin APC wanda aka yi hasashen shi ne zai yi nasara, amma hakan bai yiwu ba, a fili dai an bayyana cewa bai yi nasara a zaɓen ba, to amma kuma ai ya samu galabar riƙe alaƙar siyasa. Ya shiga tare da yin tasiri sosai a zukatan miliyoyin ‘yan Jihar Neja da sauran ‘yan Nijeriya masu cike da sanin cewa babban burin Malagi shi ne ya bunƙasa Jihar Neja.

Wata uku bayan zaɓen fid da gwanin, yanzu shi ne ya kasance abin kwatance a duk faɗin jihar. Kowa ya na nuna so da shauƙin yin kusanci da shi. Ana yi masa kallon sani sabon tauraron siyasar Jihar Neja, wanda duk sauran jam’iyyu ke shauƙin neman ya canja sheƙa ya koma cikin su, su tsayar da shi takarar gwamna kawai.

Mohammed Idris, ɗan shekara 56 a duniya, mawallafin jarida ne kuma ƙwarraren masanin iya hulɗa da jama’a. Yanzu ya zama wata rana da ta fito a siyasar Jihar Neja, wadda tafin hannu ba zai iya rufe ta ba. Ko ma dai me za a sake nanatawa dangane da sakamakon zaɓen fid da gwani da yadda aka gudanar da zaɓen, za a iya cewa an ɗauki ƙwaƙƙwaran darasi don gaba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Babu Rikici A Jam’iyyar APC A Nasarawa — Shugaban Jam’iyya
Siyasa

Babu Rikici A Jam’iyyar APC A Nasarawa — Shugaban Jam’iyya

October 21, 2025
Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu
Siyasa

Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu

October 20, 2025
Tsohon Ɗan Majalisar Bayelsa Ya Shawarci Jonathan Ya Guji Neman Takara A 2027
Siyasa

Tsohon Ɗan Majalisar Bayelsa Ya Shawarci Jonathan Ya Guji Neman Takara A 2027

October 17, 2025
Next Post
WTO Ta Yi Gargadin Fuskantar Matsin Tattalin Arziki A Duniya

WTO Ta Yi Gargadin Fuskantar Matsin Tattalin Arziki A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

October 21, 2025
Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

October 21, 2025
Aikin Jinya Kyauta: Gwamnatin Zamfara Ta Kammala Zagaye Na 10 Na Kula Da Marasa Lafiya 3,447

Aikin Jinya Kyauta: Gwamnatin Zamfara Ta Kammala Zagaye Na 10 Na Kula Da Marasa Lafiya 3,447

October 21, 2025
Ci Gaban Kasar Sin Ya Shaida Cewa Yawan Jama’a Ba Dalili Ne Na Rashin Ci Gaba Ba

Ci Gaban Kasar Sin Ya Shaida Cewa Yawan Jama’a Ba Dalili Ne Na Rashin Ci Gaba Ba

October 21, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Gwamna Yusuf Ya Buƙaci Hukumar NBC Da Ta Sa Ido Kan Gidajen Rediyo Da Talabijin Na Yanar Gizo

October 21, 2025
Me Aka Gano Kan Makomar Tattalin Arzikin Kasar Sin Daga Karuwar 5.2% Na Tattalin Arzikinta?

Me Aka Gano Kan Makomar Tattalin Arzikin Kasar Sin Daga Karuwar 5.2% Na Tattalin Arzikinta?

October 21, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Tabbatar Da Yusuf A Matsayin Sabon Shugaban NPC, Wasu 2 A Matsayin Kwamishinoni

October 21, 2025
Jirgin Kasa Mafi Saurin Gudu A Duniya Ya Fara Zirga-Zirgar Gwaji A Sin

Jirgin Kasa Mafi Saurin Gudu A Duniya Ya Fara Zirga-Zirgar Gwaji A Sin

October 21, 2025
Uba Sani Ya Amince Da Biyan Naira Biliyan ₦2.3 Ga Tsofaffin Ma’aikata Da Iyalansu

Ma’aikatan Manyan Makarantu Na Kaduna Sun Dakatar Da Yajin Aiki Yayin Da Gwamna Sani Ya Amince Da Sabon Tsarin Albashi

October 21, 2025
Jami’an Kasashen Afrika Na Koyon Dabarar Yaki Da Talauci Ta Sin A Jihar Ningxia

Jami’an Kasashen Afrika Na Koyon Dabarar Yaki Da Talauci Ta Sin A Jihar Ningxia

October 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.