• English
  • Business News
Sunday, June 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mu Kula Da Rayuwar ‘Ya’ya Mata Masu Shaye-Shaye (II)

by Abubakar Abba
2 years ago
in Marurun Zuciya
0
Mu Kula Da Rayuwar ‘Ya’ya Mata Masu Shaye-Shaye (II)
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Matsalar bai wa yara rashin kulawa daga bangaren iyaye, inda za ka ga wasu iyayen basu damu da jan ‘ya’yan su a jiki ba, har su san damuwarsu, irin wannan yana kawo matsalar da a Turanci ake kira ‘depression’, a bisa nazarin masana halayyar dan Adam. Kuma hakan har wa yau ya zo daidai da fahimtar wata malamar makaranta Aishatu Suleiman Abubakar da ke Jos da marubuciya Rahama Sabo Usman da ke Kano, wadanda ke ganin lalacewar tarbiyyar iyaye ne ke jawo wa, saboda rashin jan yaransu a jiki da ba su fuskar da za su amayar da damuwarsu ko neman shawara.

Sannan kuma ana iya samun wannan matsalar a tsakanin ma’aurata da suke samun matsala ta fahimtar juna a tsakaninsu, rashin samun wadanda za su nemi shawara a wajensu ko yawan zurfin ciki, na daga cikin abin da zai sa wasu matan su fara shaye-shaye. Sakamakon yadda mijinta, kishiyarta, ‘ya’yan miji ko wasu abokan zama suke kuntata mata, ko sun tsangwami rayuwar ta, ta yi kokarin sanar wa iyaye ko makusantan ta halin da take ciki an kasa fahimtar halin da take ciki. Daga nan ne sai ka ga mata ta fara nemarwa kanta mafita tana shaye shaye, don dauke hankalinta daga damuwar da ke cinta a rai. Wata kuma tana fara wa ne da shan magungunan karin kuzari don ta samu zafin naman yin aikace aikacen gida nata ko na mutanen da take yi wa aikatau, daga nan kuma in jiki ya saba sai a zarce da harka.

  • Duniya Na Fatan A Tabbatar Da Daidaiton Da Aka Cimma A San Francisco
  • Hadarin Mota: NIS Ta Tabbatar Da Mutuwar Jamianta 4, 7 Sun Ji Rauni A Kano

Mu’amala da kawaye ko abokan zama na cikin gida masu shaye-shaye a boye shi ma yana janyo yawaitar wannan matsalar da bazuwar ta a cikin al’umma ba tare da an ankara ba. Wasu iyaye mata suna da sakacin shan magani barkatai idan suna da ciki, wanda hakan na iya taba jinjiri kafin ma ya zo duniyar an koyar da shi. Ko kuma mata masu ajiye magani barkatai a ko’ina suka ga dama, har yaro ya dauka ya fara sha ba tare da an lura ba.
Har wa yau, an gano cewa wani lokaci likitoci kansu suna janyo wanan matsalar ta hanyar hada mutum da maganin da jininsa ba zai iya dauka ba. A hankali kuma sai jikin mutum ya saba har ya ajiye kwalin maganin ko takardar likita ya rika zuwa Kemis yana saye, ko da bayan ya samu lafiya.

Na hadu da mutane da dama, wadanda a zahiri idan ka gansu cikin karamci da sutura ta mutunci ba za ka taba yi musu tunanin suna suna shaye-shayen magungunan kara kuzari da dauke damuwa ba. Kamar yadda wata abokiyar aiki da nake girmamawa ta taba yi min tayin shan wasu kwayoyi masu saurin dauke gajiya da sa a ji garau, bayan wani aikin rangadi na zagayen duba wasu ayyuka da muka yi. Saboda a ganinta shaye-shayen kwayoyin maganin cire gajiya ba wani abin damuwa ba ne, abu ne da ya zama gama gari, kuma ita ta saba, sai ta sha take barci.

Wadannan su ne hanyoyin na daga cikin sanannun dalilan da ke hadddasa matsalar shaye-shaye a cikin al’umma. Kuma duk da kokarin da Hukumar NDLEA mai yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ke yi, na fadakarwa da kama masu kasuwancin wannan harka a birane da lunguna, abin kullum sai kara ta’azzara yake yi.

Labarai Masu Nasaba

Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana (2)

Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Ya'ya mataKannywood
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gimbiya Sirindhorn Ta Thailand:Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya” Ta Inganta Hadin Gwiwar Al’ummun Kasa Da Kasa

Next Post

Boko Haram Sun Raunata Jami’an Tsaron Gwamnan Yobe 6

Related

Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki 
Marurun Zuciya

Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana (2)

5 months ago
Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki 
Marurun Zuciya

Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki 

5 months ago
Ba Gwamnati Ce Kadai Za Ta Magance Yawan Barace-Barace Ba
Marurun Zuciya

Ba Gwamnati Ce Kadai Za Ta Magance Yawan Barace-Barace Ba

1 year ago
Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki (1)
Marurun Zuciya

Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki (1)

1 year ago
Ya Kamata Mu Dore Da Ibadu Da Kyawawan Halayenmu Na Ramadan
Marurun Zuciya

Ya Kamata Mu Dore Da Ibadu Da Kyawawan Halayenmu Na Ramadan

1 year ago
Kuncin Rayuwa: Jan Hankali Ga Iyaye Da Yayyen ‘Yan Mata
Marurun Zuciya

Kuncin Rayuwa: Jan Hankali Ga Iyaye Da Yayyen ‘Yan Mata

1 year ago
Next Post
Boko Haram Sun Raunata Jami’an Tsaron Gwamnan Yobe 6

Boko Haram Sun Raunata Jami'an Tsaron Gwamnan Yobe 6

LABARAI MASU NASABA

Alfanu Da Rashin Alfanun Tallata Shirin Aure Tun Kafin Lokacin Ya Zo

Alfanu Da Rashin Alfanun Tallata Shirin Aure Tun Kafin Lokacin Ya Zo

June 1, 2025
Yadda Za Ki Hada Funkasonki

Yadda Za Ki Hada Funkasonki

June 1, 2025
Wakilin Sin Ya Soki Yadda Amurka Ke Tafiyar Da Kudurin Takunkuman Sudan Ta Kudu

Wakilin Sin Ya Soki Yadda Amurka Ke Tafiyar Da Kudurin Takunkuman Sudan Ta Kudu

May 31, 2025
CMG Ya Watsa Shirin Musamman Na Bikin Duanwu Na 2025

CMG Ya Watsa Shirin Musamman Na Bikin Duanwu Na 2025

May 31, 2025
Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (2)

Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (2)

May 31, 2025
Gwamnatin Kano Ta Ba Iyalan Mamatan Wasanni Tallafin Naira Miliyan Ɗaya Kowane

Gwamnatin Kano Ta Ba Iyalan Mamatan Wasanni Tallafin Naira Miliyan Ɗaya Kowane

May 31, 2025
Ministocin Wajen Sin Da Kamaru Sun Gana Kan Alakar Kasashensu Da Batun Kafa IOMed

Ministocin Wajen Sin Da Kamaru Sun Gana Kan Alakar Kasashensu Da Batun Kafa IOMed

May 31, 2025
Wasu ‘Yan Siyasa Da Jami’an Tsaro Na Taimaka Wa Boko Haram – Zulum

Zulum Ya Ba Da Tallafin Karatu Ga Mata ‘Yan Asalin Jihar Da Suka Samu Maki 250 A JAMB

May 31, 2025
Nijeriya Ta Lashe Gasar Unity Cup Bayan Doke Jamaica A Bugun Fenarati

Nijeriya Ta Lashe Gasar Unity Cup Bayan Doke Jamaica A Bugun Fenarati

May 31, 2025
Hadin Gwiwar Sin Da Kasashe Masu Tasowa Ya Dade Da Zama Kan Gaba A Bangaren Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Waje

Hadin Gwiwar Sin Da Kasashe Masu Tasowa Ya Dade Da Zama Kan Gaba A Bangaren Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Waje

May 31, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.