ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 8, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mu Kula Da Rayuwar ‘Ya’ya Mata Masu Shaye-Shaye (II)

by Abubakar Abba
3 years ago
Mata

Matsalar bai wa yara rashin kulawa daga bangaren iyaye, inda za ka ga wasu iyayen basu damu da jan ‘ya’yan su a jiki ba, har su san damuwarsu, irin wannan yana kawo matsalar da a Turanci ake kira ‘depression’, a bisa nazarin masana halayyar dan Adam. Kuma hakan har wa yau ya zo daidai da fahimtar wata malamar makaranta Aishatu Suleiman Abubakar da ke Jos da marubuciya Rahama Sabo Usman da ke Kano, wadanda ke ganin lalacewar tarbiyyar iyaye ne ke jawo wa, saboda rashin jan yaransu a jiki da ba su fuskar da za su amayar da damuwarsu ko neman shawara.

Sannan kuma ana iya samun wannan matsalar a tsakanin ma’aurata da suke samun matsala ta fahimtar juna a tsakaninsu, rashin samun wadanda za su nemi shawara a wajensu ko yawan zurfin ciki, na daga cikin abin da zai sa wasu matan su fara shaye-shaye. Sakamakon yadda mijinta, kishiyarta, ‘ya’yan miji ko wasu abokan zama suke kuntata mata, ko sun tsangwami rayuwar ta, ta yi kokarin sanar wa iyaye ko makusantan ta halin da take ciki an kasa fahimtar halin da take ciki. Daga nan ne sai ka ga mata ta fara nemarwa kanta mafita tana shaye shaye, don dauke hankalinta daga damuwar da ke cinta a rai. Wata kuma tana fara wa ne da shan magungunan karin kuzari don ta samu zafin naman yin aikace aikacen gida nata ko na mutanen da take yi wa aikatau, daga nan kuma in jiki ya saba sai a zarce da harka.

  • Duniya Na Fatan A Tabbatar Da Daidaiton Da Aka Cimma A San Francisco
  • Hadarin Mota: NIS Ta Tabbatar Da Mutuwar Jamianta 4, 7 Sun Ji Rauni A Kano

Mu’amala da kawaye ko abokan zama na cikin gida masu shaye-shaye a boye shi ma yana janyo yawaitar wannan matsalar da bazuwar ta a cikin al’umma ba tare da an ankara ba. Wasu iyaye mata suna da sakacin shan magani barkatai idan suna da ciki, wanda hakan na iya taba jinjiri kafin ma ya zo duniyar an koyar da shi. Ko kuma mata masu ajiye magani barkatai a ko’ina suka ga dama, har yaro ya dauka ya fara sha ba tare da an lura ba.
Har wa yau, an gano cewa wani lokaci likitoci kansu suna janyo wanan matsalar ta hanyar hada mutum da maganin da jininsa ba zai iya dauka ba. A hankali kuma sai jikin mutum ya saba har ya ajiye kwalin maganin ko takardar likita ya rika zuwa Kemis yana saye, ko da bayan ya samu lafiya.

ADVERTISEMENT

Na hadu da mutane da dama, wadanda a zahiri idan ka gansu cikin karamci da sutura ta mutunci ba za ka taba yi musu tunanin suna suna shaye-shayen magungunan kara kuzari da dauke damuwa ba. Kamar yadda wata abokiyar aiki da nake girmamawa ta taba yi min tayin shan wasu kwayoyi masu saurin dauke gajiya da sa a ji garau, bayan wani aikin rangadi na zagayen duba wasu ayyuka da muka yi. Saboda a ganinta shaye-shayen kwayoyin maganin cire gajiya ba wani abin damuwa ba ne, abu ne da ya zama gama gari, kuma ita ta saba, sai ta sha take barci.

Wadannan su ne hanyoyin na daga cikin sanannun dalilan da ke hadddasa matsalar shaye-shaye a cikin al’umma. Kuma duk da kokarin da Hukumar NDLEA mai yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ke yi, na fadakarwa da kama masu kasuwancin wannan harka a birane da lunguna, abin kullum sai kara ta’azzara yake yi.

LABARAI MASU NASABA

A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki

Falalar Goman Farko Na Zul-hajji 

Mata
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Ɗaura Ɗamarar Magance Matsalolin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Matatar Ɗangote Ta Ƙaryata Iƙirarin Dillalan Man Fetur 

MASU ALAKA

A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki
Marurun Zuciya

A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki

June 20, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Marurun Zuciya

Falalar Goman Farko Na Zul-hajji 

May 23, 2026
marayu
Marurun Zuciya

Bukatar Kulawa Da Marayu Da Masu Karamin Karfi

May 17, 2026
Next Post
Boko Haram Sun Raunata Jami’an Tsaron Gwamnan Yobe 6

Boko Haram Sun Raunata Jami'an Tsaron Gwamnan Yobe 6

LABARAI MASU NASABA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Kwankwaso Ya Mayar wa Ali Modu Sheriff Martani, Ya Ce Peter Obi Na da Gagarumin Goyon Baya a Arewa

July 8, 2026
Sojoji Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Waɗanda Aka Sace A Taraba

Sojoji Da NDLEA Sun Kama Mutanen Da Ake Zargi Da Kai wa ’Yan Ta’adda Miyagun Ƙwayoyi A Katsina

July 8, 2026
An Gudanar Da Manyan Tarurruka 3 Game Da Kimiyya Da Fasaha A Beijing

An Gudanar Da Manyan Tarurruka 3 Game Da Kimiyya Da Fasaha A Beijing

July 8, 2026
Majalisar Zartarwa Ta Jihar Kaduna Ta Amince Da Manufofin Haɓaka Walwalar Al’ummar Jihar

Majalisar Zartarwa Ta Jihar Kaduna Ta Amince Da Manufofin Haɓaka Walwalar Al’ummar Jihar

July 8, 2026
Dole Ne Mace Ta Gaya Wa Mijinta Gaskiya Domin Ranar Hisabi – Matar Gwamnan Jigawa

Gwamnatin Jigawa Ta Ɗaga Mafi Ƙarancin Fansho Zuwa Naira 20,000

July 8, 2026
Rahoton Bankin Duniya: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Dore

Rahoton Bankin Duniya: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Dore

July 7, 2026
Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi

Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi

July 7, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Na ADC, Ya Gana da El-Rufai, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Mulkin APC

July 7, 2026
Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

July 7, 2026
Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

July 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.