ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Duniya Na Fatan A Tabbatar Da Daidaiton Da Aka Cimma A San Francisco

by CGTN Hausa
3 years ago
Francisco

Yanzu haka, duniyarmu na fuskantar manyan sauye-sauyen da ba’a taba ganin irinsa ba. Kasancewarsu manyan kasashe biyu, yadda Sin da Amurka suke hulda da juna, na haifar da muhimmin tasiri ga makomar dan Adam da ta duniya. Kamar dai yadda mataimakin babban editan jaridar Al-Ahram ta kasar Masar ya fada, “Sin da Amurka kasashe biyu ne mafiya tasiri a duniya, wadanda suke daukar babban nauyi na kiyaye kwanciyar hankali da ci gaba a duniya.” 

To ko ina ne huldar kasashen biyu za ta dosa? Akwai zabi guda biyu a gabansu, na farko shi ne daya ta dage neman nasara daga faduwar dayar, ta rura wutar adawa tsakanin sassa daban daban, kana ta jagoranci duniya zuwa turbar yamutsi da rarrabuwar kawuna; Na biyu kuma shi ne karfafa dunkulewa, da hadin gwiwa da aiki tare, don warware kalubalen da duniya ke fuskanta, da ingiza nasarar tsaro da wadata a duniya. Wadannan zabi 2 na wakiltar alkibla biyu mabambanta, wadanda za su haifar da sakamako biyu masu bambanci da juna.

  • Xi Jinping Ya Tashi Zuwa Kasar Amurka Domin Gudanar Da Taron Shugabannin Kasashen Sin Da Amurka Da Taron APEC Karo Na 30
  • Ganawar San Francisco: Tsaraba Daga Jawabin Shugaba Xi Kan Bukatar Sin Da Amurka Su Nuna Su Manya Ne A Aikace

Hakika, ganawar shugabannin kasashen biyu a ranar 15 ga wata a birnin San Francisco na kasar Amurka, ta samar da amsa game da me ya kamata kasashen biyu suka zaba, wato ya kamata kasashen Sin da Amurka su yi sabon hangen nesa, tare da gina ginshikai biyar tare, don inganta alakar dake tsakaninsu. Na farko, habaka daidaitacciyar fahimta tare, Na biyu, magance rashin jituwa tare yadda ya kamata. Na uku, ciyar da hadin gwiwar moriyar juna gaba tare, sai na hudu, sauke nauyin dake wuyansu a matsayinsu na manyan kasashe. Kana na biyar kuma na karshe, shi ne inganta mu’amala tsakanin al’ummomin kasashen biyu.

ADVERTISEMENT

Wannan ziyarar da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya kai San Francisco ta kasance ziyarar da ya kai kasar ta Amurka bayan tsawon shekaru shida, haka kuma ganawar da ya yi tare takwaransa na Amurka Joe Biden, ta wakana ne biyo bayan ganawar da suka yi a tsibirin Bali na kasar Indonesia a shekarar bara. A yayin ganawarsu, shugaba Xi Jinping ya yi nuni da cewa, “takara tsakanin manyan kasashe masu karfin fada a ji ba ita ce taken wannan zamani ba, kuma ba za ta warware matsalolin Sin da na Amurka da na duniya baki daya ba. Wannan duniya na da fadin da zai wadatar da Sin da Amurka, kuma nasarorinmu damammaki ne gare mu baki daya.”

A hakika, dalilin da ya sa huldar da ke tsakanin Sin da Amurka ta shiga mawuyacin yanayi a shekarun baya shi ne, yadda Amurka ta yi kuskuren daukar Sin din a matsayin babbar abokiyar takara da ta fi yi mata barazana, abin da ya sa ta dauki munanan matakan da ba su dace ba.

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Yadda huldar Sin da Amurka za ta bunkasa a hakika ta dogara ne ga yadda kasashen biyu suke fahimtar juna. In dai suna daukar juna a matsayin abokan hadin gwiwa, to, huldarsu za ta yi ta inganta. Amma idan sun dauki juna a matsayin abokan takara, to, za a kara samun yanayi na fito na fito a tsakaninsu.

Ba ma kawai Sin da Amurka za su amfana daga kyakkyawar huldar da ke tsakaninsu ba, har ma da kasashen duniya baki daya. Kamar yadda masanin kasar Senegal kan nazarin harkokin kasar Sin Amadou Diop ya fada, duniya da ke neman karin hadin kai, da bude kofa ga juna, da ma albarka na bukatar a maido da huldar Sin da Amurka kan turbar da ta kamata. “Sin da Amurka dukkansu manyan abokan ciniki ne ga Afirka. Kyakkyawar dangantakar kasashen biyu na da matukar muhimmanci wajen tabbatar da bunkasar tattalin arziki, da ciniki, da zaman lafiya, da tsaro, da dauwamammen ci gaba a Afirka. Don haka, Afirka na bukatar Sin da Amurka su kara inganta huldarsu.”

A yayin ganawarsu, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya kuma jaddada cewa, kamata ya yi a yi la’akari, gami da tsara shirin raya dangantakar Sin da Amurka, ta yin la’akari da makomar dan Adam da ta duniya.

Daga tsibirin Bali har zuwa San Francisco, farfadowar huldar Sin da Amurka ba abu ne mai sauki ba, abubuwan da suka faru sun shaida cewa, muddin dai an tabbatar da daidaiton da shugabannin kasashen biyu suka cimma, za a kai ga kyautata huldar kasashen biyu, kuma duniya na fatan a tabbatar da daidaiton da aka cimma a San Francisco. (Lubabatu Lei)

 

Francisco
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

MASU ALAKA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa
Daga Birnin Sin

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Next Post
Gimbiya Sirindhorn Ta Thailand:Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya” Ta Inganta Hadin Gwiwar Al’ummun Kasa Da Kasa

Gimbiya Sirindhorn Ta Thailand:Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya” Ta Inganta Hadin Gwiwar Al’ummun Kasa Da Kasa

LABARAI MASU NASABA

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.