• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mulkin Dimokuradiyya Ya Kawo Ci Gaba Mai Dorewa A Gombe Da Nijeriya -Inuwa

byKhalid Idris Doya
3 years ago
Inuwa

Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya ya bayyana cewa, shekaru 23 a jere na mulkin dimokuradiyya sun haifar da ci gaba mai dorewa a Jihar Gombe da ma kasa baki daya, lamarin da ya taimaka wajen bunkasa rayuwar al’ummar jihar.

Kan hakan sai ya bukaci al’ummar Jihar Gombe su ci gaba da taka rawa wajen karfafa dimokuradiyya ta hanyar shiga a dama da su yadda ya kamata a harkokin zabe wadda ya ce yana ci gaba da ingantuwa a tsawon shekaru.

  • Cikin Shekara 3 Mun Yi Aiki Tukuru Don Ci Gaban Jihar Gombe —Inuwa Yahaya

Ya yi kira ga al’ummar jihar su shiga a dama da su wajen jajirce a harkar shugabanci.

A wani sakon taya murna na alamta ranar ta dimokuradiyya ta 12 ga watan Yuni wanda Kakakin gwamnan, Ismaila Uba Misilli ya fitar, Gwamna Inuwa ya ce dimokuradiyya ta samu wurin zama a kasar nan. Ya kuma bayyana jin dadin yadda aka gudanar da zabukan fid da gwani cikin nasara, yana mai kira ga al’ummar jihar su ci gaba da dabbaka wannan dattakun yayin da harkokin zaben 2023 ke dab da kankama.

Sai ya bukaci jama’a su yi amfani da damar ci gaba da rajistar masu kada kuri’a, musamman wadanda yanzu ne suka kai shekarun jefa kuri’a ko wadanda ba su yi rajistar ba a baya, don samun nasu katin zaben kuma su samu damar kada kuri’u wajen bayar da tasu gudunmawan gina kasa.

LABARAI MASU NASABA

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

Ya yaba wa shugabannin jihar na yanzu da na baya, yana mai cewa kokarin da suka yi ya tabbatar da Jihar Gombe a matsayin dunkulalliyar jiha, “Mu a Jihar Gombe babu wata jayayya cewa, dimokuradiyya ta kawo ci gaba mai dorewa a jiharmu. Gwamnonin farar fula uku sun yi mulki, lamarin da ya share fagen shigowar tamu gwamnatin.

“Ina amfani da wannar dama wajen yabo da jinjina ga tsofaffi da shugabanninmu masu ci, wadanda suka ba da gudunmawa wajen karfafa dimokradiyya da harkokin siyasarmu.

Don haka ina kira a gare mu, mu kara jajircewa wajen gina kasa, mu kara hada kai wajen tunkarar matsalolinmu ta hanyar jajircewa ga addu’o’i. Dole ne mu sani cewa aikin gina kasa alhakki ne a kanmu baki daya,” a cewar Gwamnan.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Next Post
Goro

Goron Jumu'a

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version