• English
  • Business News
Thursday, June 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mulkin Dimokuradiyya Ya Kawo Ci Gaba Mai Dorewa A Gombe Da Nijeriya -Inuwa

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Labarai
0
Mulkin Dimokuradiyya Ya Kawo Ci Gaba Mai Dorewa A Gombe Da Nijeriya -Inuwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya ya bayyana cewa, shekaru 23 a jere na mulkin dimokuradiyya sun haifar da ci gaba mai dorewa a Jihar Gombe da ma kasa baki daya, lamarin da ya taimaka wajen bunkasa rayuwar al’ummar jihar.

Kan hakan sai ya bukaci al’ummar Jihar Gombe su ci gaba da taka rawa wajen karfafa dimokuradiyya ta hanyar shiga a dama da su yadda ya kamata a harkokin zabe wadda ya ce yana ci gaba da ingantuwa a tsawon shekaru.

  • Cikin Shekara 3 Mun Yi Aiki Tukuru Don Ci Gaban Jihar Gombe —Inuwa Yahaya

Ya yi kira ga al’ummar jihar su shiga a dama da su wajen jajirce a harkar shugabanci.

A wani sakon taya murna na alamta ranar ta dimokuradiyya ta 12 ga watan Yuni wanda Kakakin gwamnan, Ismaila Uba Misilli ya fitar, Gwamna Inuwa ya ce dimokuradiyya ta samu wurin zama a kasar nan. Ya kuma bayyana jin dadin yadda aka gudanar da zabukan fid da gwani cikin nasara, yana mai kira ga al’ummar jihar su ci gaba da dabbaka wannan dattakun yayin da harkokin zaben 2023 ke dab da kankama.

Sai ya bukaci jama’a su yi amfani da damar ci gaba da rajistar masu kada kuri’a, musamman wadanda yanzu ne suka kai shekarun jefa kuri’a ko wadanda ba su yi rajistar ba a baya, don samun nasu katin zaben kuma su samu damar kada kuri’u wajen bayar da tasu gudunmawan gina kasa.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Asibiti, Motocin Bas Na CNG A Kaduna

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 24 A Katsina

Ya yaba wa shugabannin jihar na yanzu da na baya, yana mai cewa kokarin da suka yi ya tabbatar da Jihar Gombe a matsayin dunkulalliyar jiha, “Mu a Jihar Gombe babu wata jayayya cewa, dimokuradiyya ta kawo ci gaba mai dorewa a jiharmu. Gwamnonin farar fula uku sun yi mulki, lamarin da ya share fagen shigowar tamu gwamnatin.

“Ina amfani da wannar dama wajen yabo da jinjina ga tsofaffi da shugabanninmu masu ci, wadanda suka ba da gudunmawa wajen karfafa dimokradiyya da harkokin siyasarmu.

Don haka ina kira a gare mu, mu kara jajircewa wajen gina kasa, mu kara hada kai wajen tunkarar matsalolinmu ta hanyar jajircewa ga addu’o’i. Dole ne mu sani cewa aikin gina kasa alhakki ne a kanmu baki daya,” a cewar Gwamnan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotu Ta Daure Wata Mata Shekara 30 Saboda Ta Yi Bari

Next Post

Goron Jumu’a

Related

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Asibiti, Motocin Bas Na CNG A Kaduna
Labarai

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Asibiti, Motocin Bas Na CNG A Kaduna

11 minutes ago
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 24 A Katsina
Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 24 A Katsina

2 hours ago
NDLEA Ta Kama Tabar Wiwi Buhu 116 A Jihar Kano
Labarai

NDLEA Ta Kai Samame Fitattun Wuraren Shaye-shaye, Ta Cafke Mutane 19 A Kano

2 hours ago
Gwamnatin Tarayya Da Jamus Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Yuro Miliyan 20 A Ɓangaren Makamashi
Labarai

Gwamnatin Tarayya Da Jamus Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Yuro Miliyan 20 A Ɓangaren Makamashi

4 hours ago
Sojoji Sun Kai Farmaki Masana’antar Kera Bindiga, Sun Yi Kame A Taraba
Manyan Labarai

An Kashe ‘Yan Ta’adda 6,260, An Ceto Mutane 5,365 Acikin Shekaru Biyu – Hedikwatar Tsaro 

5 hours ago
Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya
Ra'ayi Riga

Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya

6 hours ago
Next Post
Goro

Goron Jumu'a

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Asibiti, Motocin Bas Na CNG A Kaduna

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Asibiti, Motocin Bas Na CNG A Kaduna

June 19, 2025
An Bude Baje Kolin Kayayyakin Sin Da Kudancin Asiya Karo Na 9 A Kunming

An Bude Baje Kolin Kayayyakin Sin Da Kudancin Asiya Karo Na 9 A Kunming

June 19, 2025
Sin Za Ta Hanzarta Duba Bukatun Samun Lasisin Fitar Da Ma’adanan “Rare Earth” Zuwa Ketare

Sin Za Ta Hanzarta Duba Bukatun Samun Lasisin Fitar Da Ma’adanan “Rare Earth” Zuwa Ketare

June 19, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 24 A Katsina

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 24 A Katsina

June 19, 2025
NDLEA Ta Kama Tabar Wiwi Buhu 116 A Jihar Kano

NDLEA Ta Kai Samame Fitattun Wuraren Shaye-shaye, Ta Cafke Mutane 19 A Kano

June 19, 2025
Xi Ya Tattauna Da Shugaban Rasha Ta Wayar Tarho

Xi Ya Tattauna Da Shugaban Rasha Ta Wayar Tarho

June 19, 2025
Yunkurin Tauye Ci Gaban Fasahar Kera “Chips” Ta Sin Ba Zai Haifar Da Da Mai Ido Ba

Yunkurin Tauye Ci Gaban Fasahar Kera “Chips” Ta Sin Ba Zai Haifar Da Da Mai Ido Ba

June 19, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Jamus Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Yuro Miliyan 20 A Ɓangaren Makamashi

Gwamnatin Tarayya Da Jamus Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Yuro Miliyan 20 A Ɓangaren Makamashi

June 19, 2025
Sin Ta Fadada Matakin Rage Haraji Ga Kasashe Masu Raunin Tattalin Arziki

Sin Ta Fadada Matakin Rage Haraji Ga Kasashe Masu Raunin Tattalin Arziki

June 19, 2025
Sin Na Son Taka Rawar Gani Wajen Maido Da Kwanciyar Hankali A Yankin Gabas Ta Tsakiya Cikin Sauri

Sin Na Son Taka Rawar Gani Wajen Maido Da Kwanciyar Hankali A Yankin Gabas Ta Tsakiya Cikin Sauri

June 19, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.