• Leadership Hausa
Thursday, June 1, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mulkin Dimokuradiyya Ya Kawo Ci Gaba Mai Dorewa A Gombe Da Nijeriya -Inuwa

by Khalid Idris Doya
12 months ago
in Labarai
0
Mulkin Dimokuradiyya Ya Kawo Ci Gaba Mai Dorewa A Gombe Da Nijeriya -Inuwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya ya bayyana cewa, shekaru 23 a jere na mulkin dimokuradiyya sun haifar da ci gaba mai dorewa a Jihar Gombe da ma kasa baki daya, lamarin da ya taimaka wajen bunkasa rayuwar al’ummar jihar.

Kan hakan sai ya bukaci al’ummar Jihar Gombe su ci gaba da taka rawa wajen karfafa dimokuradiyya ta hanyar shiga a dama da su yadda ya kamata a harkokin zabe wadda ya ce yana ci gaba da ingantuwa a tsawon shekaru.

  • Cikin Shekara 3 Mun Yi Aiki Tukuru Don Ci Gaban Jihar Gombe —Inuwa Yahaya

Ya yi kira ga al’ummar jihar su shiga a dama da su wajen jajirce a harkar shugabanci.

A wani sakon taya murna na alamta ranar ta dimokuradiyya ta 12 ga watan Yuni wanda Kakakin gwamnan, Ismaila Uba Misilli ya fitar, Gwamna Inuwa ya ce dimokuradiyya ta samu wurin zama a kasar nan. Ya kuma bayyana jin dadin yadda aka gudanar da zabukan fid da gwani cikin nasara, yana mai kira ga al’ummar jihar su ci gaba da dabbaka wannan dattakun yayin da harkokin zaben 2023 ke dab da kankama.

Sai ya bukaci jama’a su yi amfani da damar ci gaba da rajistar masu kada kuri’a, musamman wadanda yanzu ne suka kai shekarun jefa kuri’a ko wadanda ba su yi rajistar ba a baya, don samun nasu katin zaben kuma su samu damar kada kuri’u wajen bayar da tasu gudunmawan gina kasa.

Labarai Masu Nasaba

Tallafin Mai: Ba A Cimma Matsaya Tsakanin Gwamnatin Tarayya Da NLC Ba

China Ta Yi Alkawarin Ci Gaba Da Kulla Alakar Tattalin Arziki Da Nijeriya

Ya yaba wa shugabannin jihar na yanzu da na baya, yana mai cewa kokarin da suka yi ya tabbatar da Jihar Gombe a matsayin dunkulalliyar jiha, “Mu a Jihar Gombe babu wata jayayya cewa, dimokuradiyya ta kawo ci gaba mai dorewa a jiharmu. Gwamnonin farar fula uku sun yi mulki, lamarin da ya share fagen shigowar tamu gwamnatin.

“Ina amfani da wannar dama wajen yabo da jinjina ga tsofaffi da shugabanninmu masu ci, wadanda suka ba da gudunmawa wajen karfafa dimokradiyya da harkokin siyasarmu.

Don haka ina kira a gare mu, mu kara jajircewa wajen gina kasa, mu kara hada kai wajen tunkarar matsalolinmu ta hanyar jajircewa ga addu’o’i. Dole ne mu sani cewa aikin gina kasa alhakki ne a kanmu baki daya,” a cewar Gwamnan.

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotu Ta Daure Wata Mata Shekara 30 Saboda Ta Yi Bari

Next Post

Goron Jumu’a

Related

Tallafin Mai: Ba A Cimma Matsaya Tsakanin Gwamnatin Tarayya Da NLC Ba
Manyan Labarai

Tallafin Mai: Ba A Cimma Matsaya Tsakanin Gwamnatin Tarayya Da NLC Ba

4 hours ago
China Ta Yi Alkawarin Ci Gaba Da Kulla Alakar Tattalin Arziki Da Nijeriya
Labarai

China Ta Yi Alkawarin Ci Gaba Da Kulla Alakar Tattalin Arziki Da Nijeriya

5 hours ago
Za Mu Dauki Kwakkwaran Mataki Idan Gwamnati Ta Janye Tallafin Man Fetur —NLC
Manyan Labarai

Za Mu Dauki Kwakkwaran Mataki Idan Gwamnati Ta Janye Tallafin Man Fetur —NLC

6 hours ago
Akwai Wadataccen Mai Da Zai Ishi ‘Yan Kasa Nan Da Kwanaki 30 —NNPCL
Manyan Labarai

Akwai Wadataccen Mai Da Zai Ishi ‘Yan Kasa Nan Da Kwanaki 30 —NNPCL

7 hours ago
Tinubu Ya Gana Da Shugaban EFCC A Fadar Shugaban Kasa
Manyan Labarai

Tinubu Ya Gana Da Shugaban EFCC A Fadar Shugaban Kasa

8 hours ago
Kotu Ta Daure Basarake Shekaru 15 Saboda Garkuwa Da Kansa
Manyan Labarai

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Dakta Idris Abdulaziz

10 hours ago
Next Post
Goro

Goron Jumu'a

LABARAI MASU NASABA

Ya Dace ‘Yan Siyasan Amurka Su Yi Tunani Kan Kalaman Elon Musk

Ya Dace ‘Yan Siyasan Amurka Su Yi Tunani Kan Kalaman Elon Musk

May 31, 2023
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Samar Da Yanayin Da Ya Dace Na Tattaunawa Tsakanin Rundunonin Sojin Kasashen 2

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Samar Da Yanayin Da Ya Dace Na Tattaunawa Tsakanin Rundunonin Sojin Kasashen 2

May 31, 2023
Sin Na Son Hadin Kai Da Sauran Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Nazarin Sararin Samaniya

Sin Na Son Hadin Kai Da Sauran Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Nazarin Sararin Samaniya

May 31, 2023
Gudummawar Kasar Sin Ga Aikin Tabbatar Da Zaman Lafiya A Duniya Abu Ne Da Ake Gani A Zahiri

Gudummawar Kasar Sin Ga Aikin Tabbatar Da Zaman Lafiya A Duniya Abu Ne Da Ake Gani A Zahiri

May 31, 2023
Tallafin Mai: Ba A Cimma Matsaya Tsakanin Gwamnatin Tarayya Da NLC Ba

Tallafin Mai: Ba A Cimma Matsaya Tsakanin Gwamnatin Tarayya Da NLC Ba

May 31, 2023
Sin Na Goyon Bayan Gwamnatin Mali Wajen Yaki Da Ta’addanci Da Tabbatar Da Tsaron Kasa

Sin Na Goyon Bayan Gwamnatin Mali Wajen Yaki Da Ta’addanci Da Tabbatar Da Tsaron Kasa

May 31, 2023
An Gudanar Da Taro Karo Na 12 Na Dandalin Masanan Sin Da Afirka

An Gudanar Da Taro Karo Na 12 Na Dandalin Masanan Sin Da Afirka

May 31, 2023
China Ta Yi Alkawarin Ci Gaba Da Kulla Alakar Tattalin Arziki Da Nijeriya

China Ta Yi Alkawarin Ci Gaba Da Kulla Alakar Tattalin Arziki Da Nijeriya

May 31, 2023
Za Mu Dauki Kwakkwaran Mataki Idan Gwamnati Ta Janye Tallafin Man Fetur —NLC

Za Mu Dauki Kwakkwaran Mataki Idan Gwamnati Ta Janye Tallafin Man Fetur —NLC

May 31, 2023
Akwai Wadataccen Mai Da Zai Ishi ‘Yan Kasa Nan Da Kwanaki 30 —NNPCL

Akwai Wadataccen Mai Da Zai Ishi ‘Yan Kasa Nan Da Kwanaki 30 —NNPCL

May 31, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.