• English
  • Business News
Saturday, October 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mun Biya Miliyan 250 Don Ceto Dalibai 121 Da Aka Sace A Kaduna – CAN

by Sadiq
2 years ago
CAN

Shugaban kungiyar Kiristocin Nijeriya (CAN) reshen Jihar Kaduna, Rabaran John Joseph Hayab, ya bayyana cewa sun biya kudin fansa Naira miliyan 250 domin a sako dalibai 121 na makarantar sakandare ta Bethel Baptist da aka yi garkuwa da su a watan Yuli 2021.

Rabaran Hayab ya bayyana haka ne a wata ziyarar ban girma da ya kai wa Gwamna Uba Sani a Kaduna.

Ya kuma bayyana cewa Treasure Ayuba, dalibin Bethel na karshe da ya tsere daga hannun wadanda suka yi garkuwa da su kimanin mako daya da ya wuce,ya musanta rade-radin da ake na cewar dalibin ya nuna sha’awar zama a hannun maharan.

Shugaban na CAN ya bayyana cewa an yi kokarin ganin an sako Treasure, ciki har da aika kudin fansa ga maharan har sau biyu, ya kara da cewa jimillar kudaden da aka biya domin a sako su a karshe ya kai Naira miliyan 250.

“A yau, mun taru a nan don nuna godiya. Muna maraba da dawowar Treasure Ayuba, dalibi na karshe da ya rage a hannun ‘yan bindiga na makarantar sakandaren Bethel Baptist da ke nan Kaduna.

LABARAI MASU NASABA

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

Ya bayyana irin kalubalen da ‘yan uwan Treasure suka fuskanta wajen ganin an sako shi da kuma sace-sacen da aka yi a lokacin da aka kai kudin fansa.

Da yake mayar da martani, Gwamna Uba Sani ya ba iwa Treasure Ayuba tabbacin goyon bayan gwamnatin jihar tare da bayyana cewa ana daukar matakan inganta lafiyar dalibai a makarantun jihar.

Uba Sani ya ce kafa kwamitocin tsaro a makarantu, tura jami’an ‘yan banga na Kaduna (KADVIS), da kuma tabbatar da harabar makarantu ta hanyar gina shinge na daga cikin matakan tabbatar da tsaron dalibai da kuma inganta yanayin karatu.

“Mun dauki matakin kare makarantunmu da kuma tabbatar da cewa yaranmu sun samu ilimi a yanayi mai kyau. Za mu kafa kwamitocin tsaro a dukkan makarantu, mu tabbatar da tura jami’an tsaro na KADVIS (Kaduna Vigilance Service) zuwa dukkan makarantunmu, tare da tabbatar da tsaron makarantunmu ta hanyar gina katanga a kewayen makarantun, da sauran matakan da za mu dauka,” in ji shi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

October 18, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas
Tsaro

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

October 18, 2025
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja
Tsaro

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

October 18, 2025
Next Post
Kasar Sin Za Ta Inganta Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Gabatar Da Karin Damarmaki Ga Duniya

Kasar Sin Za Ta Inganta Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Gabatar Da Karin Damarmaki Ga Duniya

LABARAI MASU NASABA

gombe

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

October 18, 2025
Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

October 18, 2025
An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

October 18, 2025
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

October 18, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

October 18, 2025
Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

October 18, 2025
ASUU

Cikin Wata 9 Farfesoshi 309 Sun Bar Aiki A Jami’o’in Gwamnati, In Ji ASUU

October 18, 2025
Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

October 18, 2025
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

October 18, 2025
Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai

Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai

October 18, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.