• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mun Biya Miliyan 250 Don Ceto Dalibai 121 Da Aka Sace A Kaduna – CAN

by Sadiq
2 years ago
in Labarai
0
Mun Biya Miliyan 250 Don Ceto Dalibai 121 Da Aka Sace A Kaduna – CAN
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kungiyar Kiristocin Nijeriya (CAN) reshen Jihar Kaduna, Rabaran John Joseph Hayab, ya bayyana cewa sun biya kudin fansa Naira miliyan 250 domin a sako dalibai 121 na makarantar sakandare ta Bethel Baptist da aka yi garkuwa da su a watan Yuli 2021.

Rabaran Hayab ya bayyana haka ne a wata ziyarar ban girma da ya kai wa Gwamna Uba Sani a Kaduna.

Ya kuma bayyana cewa Treasure Ayuba, dalibin Bethel na karshe da ya tsere daga hannun wadanda suka yi garkuwa da su kimanin mako daya da ya wuce,ya musanta rade-radin da ake na cewar dalibin ya nuna sha’awar zama a hannun maharan.

Shugaban na CAN ya bayyana cewa an yi kokarin ganin an sako Treasure, ciki har da aika kudin fansa ga maharan har sau biyu, ya kara da cewa jimillar kudaden da aka biya domin a sako su a karshe ya kai Naira miliyan 250.

“A yau, mun taru a nan don nuna godiya. Muna maraba da dawowar Treasure Ayuba, dalibi na karshe da ya rage a hannun ‘yan bindiga na makarantar sakandaren Bethel Baptist da ke nan Kaduna.

Labarai Masu Nasaba

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

Ya bayyana irin kalubalen da ‘yan uwan Treasure suka fuskanta wajen ganin an sako shi da kuma sace-sacen da aka yi a lokacin da aka kai kudin fansa.

Da yake mayar da martani, Gwamna Uba Sani ya ba iwa Treasure Ayuba tabbacin goyon bayan gwamnatin jihar tare da bayyana cewa ana daukar matakan inganta lafiyar dalibai a makarantun jihar.

Uba Sani ya ce kafa kwamitocin tsaro a makarantu, tura jami’an ‘yan banga na Kaduna (KADVIS), da kuma tabbatar da harabar makarantu ta hanyar gina shinge na daga cikin matakan tabbatar da tsaron dalibai da kuma inganta yanayin karatu.

“Mun dauki matakin kare makarantunmu da kuma tabbatar da cewa yaranmu sun samu ilimi a yanayi mai kyau. Za mu kafa kwamitocin tsaro a dukkan makarantu, mu tabbatar da tura jami’an tsaro na KADVIS (Kaduna Vigilance Service) zuwa dukkan makarantunmu, tare da tabbatar da tsaron makarantunmu ta hanyar gina katanga a kewayen makarantun, da sauran matakan da za mu dauka,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: CANDalibaiKadunaKudin FansaRabaranUba SaniYan bindiga
ShareTweetSendShare
Previous Post

NLC Da TUC Sun Rufe Titin Zuwa Filin Jirgin Saman Abuja, Sun Bukaci A Hana Zuwa Imo

Next Post

Kasar Sin Za Ta Inganta Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Gabatar Da Karin Damarmaki Ga Duniya

Related

Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja
Labarai

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

2 hours ago
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?
Da ɗumi-ɗuminsa

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

2 hours ago
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 
Labarai

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

3 hours ago
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi
Labarai

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

4 hours ago
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

6 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

7 hours ago
Next Post
Kasar Sin Za Ta Inganta Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Gabatar Da Karin Damarmaki Ga Duniya

Kasar Sin Za Ta Inganta Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Gabatar Da Karin Damarmaki Ga Duniya

LABARAI MASU NASABA

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.