• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mun Biya Miliyan 250 Don Ceto Dalibai 121 Da Aka Sace A Kaduna – CAN

by Sadiq
2 years ago
in Labarai
0
Mun Biya Miliyan 250 Don Ceto Dalibai 121 Da Aka Sace A Kaduna – CAN
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kungiyar Kiristocin Nijeriya (CAN) reshen Jihar Kaduna, Rabaran John Joseph Hayab, ya bayyana cewa sun biya kudin fansa Naira miliyan 250 domin a sako dalibai 121 na makarantar sakandare ta Bethel Baptist da aka yi garkuwa da su a watan Yuli 2021.

Rabaran Hayab ya bayyana haka ne a wata ziyarar ban girma da ya kai wa Gwamna Uba Sani a Kaduna.

Ya kuma bayyana cewa Treasure Ayuba, dalibin Bethel na karshe da ya tsere daga hannun wadanda suka yi garkuwa da su kimanin mako daya da ya wuce,ya musanta rade-radin da ake na cewar dalibin ya nuna sha’awar zama a hannun maharan.

Shugaban na CAN ya bayyana cewa an yi kokarin ganin an sako Treasure, ciki har da aika kudin fansa ga maharan har sau biyu, ya kara da cewa jimillar kudaden da aka biya domin a sako su a karshe ya kai Naira miliyan 250.

“A yau, mun taru a nan don nuna godiya. Muna maraba da dawowar Treasure Ayuba, dalibi na karshe da ya rage a hannun ‘yan bindiga na makarantar sakandaren Bethel Baptist da ke nan Kaduna.

Labarai Masu Nasaba

2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

Ya bayyana irin kalubalen da ‘yan uwan Treasure suka fuskanta wajen ganin an sako shi da kuma sace-sacen da aka yi a lokacin da aka kai kudin fansa.

Da yake mayar da martani, Gwamna Uba Sani ya ba iwa Treasure Ayuba tabbacin goyon bayan gwamnatin jihar tare da bayyana cewa ana daukar matakan inganta lafiyar dalibai a makarantun jihar.

Uba Sani ya ce kafa kwamitocin tsaro a makarantu, tura jami’an ‘yan banga na Kaduna (KADVIS), da kuma tabbatar da harabar makarantu ta hanyar gina shinge na daga cikin matakan tabbatar da tsaron dalibai da kuma inganta yanayin karatu.

“Mun dauki matakin kare makarantunmu da kuma tabbatar da cewa yaranmu sun samu ilimi a yanayi mai kyau. Za mu kafa kwamitocin tsaro a dukkan makarantu, mu tabbatar da tura jami’an tsaro na KADVIS (Kaduna Vigilance Service) zuwa dukkan makarantunmu, tare da tabbatar da tsaron makarantunmu ta hanyar gina katanga a kewayen makarantun, da sauran matakan da za mu dauka,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: CANDalibaiKadunaKudin FansaRabaranUba SaniYan bindiga
ShareTweetSendShare
Previous Post

NLC Da TUC Sun Rufe Titin Zuwa Filin Jirgin Saman Abuja, Sun Bukaci A Hana Zuwa Imo

Next Post

Kasar Sin Za Ta Inganta Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Gabatar Da Karin Damarmaki Ga Duniya

Related

2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe
Labarai

2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

35 minutes ago
Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari
Rahotonni

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

3 hours ago
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya
Labarai

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

12 hours ago
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi
Labarai

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

13 hours ago
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa
Labarai

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

13 hours ago
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba
Labarai

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

14 hours ago
Next Post
Kasar Sin Za Ta Inganta Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Gabatar Da Karin Damarmaki Ga Duniya

Kasar Sin Za Ta Inganta Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Gabatar Da Karin Damarmaki Ga Duniya

LABARAI MASU NASABA

2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

August 23, 2025
Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

August 23, 2025
Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

August 23, 2025
Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

August 22, 2025
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

August 22, 2025
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

August 22, 2025
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

August 22, 2025
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

August 22, 2025
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

August 22, 2025
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.