ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, November 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mun Dandana Kudarmu A 2022, In Ji ‘Yan Kasuwa A Jihar Gombe

by Leadership Hausa
3 years ago
Gombe

A watan farko da shigowa sabuwar shekarar 2023 (wato janairu), ‘yan kasuwa a jihar Gombe, waiwaye suka yi a shekarar da ta gabace ta, wato 2022 inda da yawa sukayi kukan cewa, sun dandana kudar su a shekarar, saboda, hauhawar farashi a kan duk kayayyakin kasuwanci, musamman abinci da kayan masarufi da kuma rashin tsaro, suna mai kukan cewa ‘’kar Allah ya sake maimaita mana irin wannan masifa’’.

A wani zagaya, da ‘yan jarida suka yi a ranar Litinin din wannan makon, ta ji wasu da dama cikin yan kasuwa, manya da kanana, suna kukan cewa, ‘’gwamnatin Buhari ba ta’ yankasuwa ba ce, domin mu bamu taba fuskantar rayuwa kamr a karkashin mulkin shi (Buhari) ba’’.

  • Tsokaci Kan Dukan Da Wasu Maza Ke Wa Matansu
  • An Yi Gwanjon Rigar Da Pele Ya Buga Kofin Duniya Na Karshe Da Ita

Fitaccen dan kasuwan kayayyakin gini, kuma shugaban Sabham (Nig) Ltd, Gombe, Alhaji Sabo Adamu, ya ce, ai sake bada umurnin a bude kan iyakokin kasar bayan rufe su, na daya daga cikin abubuwan da suka jawo hauhawar farashi a Najeriya.

ADVERTISEMENT

‘’Don haka, Gwamnatin ta sake tunani a kan lamarin ta kuma bada unurni a rurrufe bodojin, saboda hakan zai sa ‘yan kasa su dukufa wajen bunkasa kayayyakin cikin gida, kaya da abinci su yawaita, kuma za’a samu saukin rayuwa’’ inji shi.

A hira da Babban Manajan sanannen kamfanin hada – hadar dilolin atamfofi da kayayyakin amfanin yau da kullum na maza da mata da yara, wato SAN HUSSEIN SUPER MARKETS Gombe, Alhaji Muhammad Umar Kawu, Shi nuna godiya ya yi ga Allah da shigowar sabuwar shekarar 2023 lami lafiya.

LABARAI MASU NASABA

Wasu Mahara Sun Kashe Mata 2, Tare Da da Ƙona Gidansu A Tudun Yola

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje

Dangane da tsadar rayuwa da ‘Yan Najeriya suke ta kuka a kai kuwa, sai Alhaji Muhammad Kawu yace, ‘‘mu koma ga Allah, duk da mun san irin halin da muka shiga sai adu’a, ita ce kawai mafita ‘’.

Sai ya shawarci ‘Yan Jihar ta Gombe, da ma ‘yan kasa baki daya, da su rinka yi wa Shugabanni Addu’a, maimakon aibantasu , yana kuma matukar hamdala da kamfanonin SAN HUSSEIN, da suka kara bunkasa  saboda sassautawa kwastomomin su farashin kayayyaki, ‘‘Don haka, ina fata ‘Yan kasuwa, takwarorin mu, su tausayawa talakokin mu wajen rage tsadar kayayyakin su saboda yin haka ce zai sa suga alheri da ci gaba a kasuwancin su’’.

Manajan kuma, sai ya yi fatan Allah Ya kawo wa Najeriya ci gaba a wannan sabon shekara ta 2023, da kuma adu’ar Allah Yasa zabubbuka masu zuwa, za’a yisu cikin lumana da kwanciyar hankali. Kusan kashi 75 cikin dari (75%) da aka zanta da su, sun dora laifin ne akan Gwamnatin Shugaba Buhari suna nanata cewar ‘’ kar Allah Ya sake maimaita mana’’.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Wasu Mahara Sun Kashe Mata 2, Tare Da da Ƙona Gidansu A Tudun Yola
Manyan Labarai

Wasu Mahara Sun Kashe Mata 2, Tare Da da Ƙona Gidansu A Tudun Yola

November 15, 2025
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje
Rahotonni

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje

November 15, 2025
Fashi Da Makami: An Yanke Wa ’Yan Nijeriya Hudu Mazauna Birtaniya Hukuncin Daurin Shekara 55 A Gidan Yari
Kotu Da Ɗansanda

Fashi Da Makami: An Yanke Wa ’Yan Nijeriya Hudu Mazauna Birtaniya Hukuncin Daurin Shekara 55 A Gidan Yari

November 15, 2025
Next Post
Benzema Ya Karya Tarihin Raul Gonzalez

Benzema Ya Karya Tarihin Raul Gonzalez

LABARAI MASU NASABA

Shakirat Ta Tsallaka Mataki Na Ƙarshe Na Zama Gwarzuwar Ƴar Wasan Afrika

Shakirat Ta Tsallaka Mataki Na Ƙarshe Na Zama Gwarzuwar Ƴar Wasan Afrika

November 15, 2025
Wasu Mahara Sun Kashe Mata 2, Tare Da da Ƙona Gidansu A Tudun Yola

Wasu Mahara Sun Kashe Mata 2, Tare Da da Ƙona Gidansu A Tudun Yola

November 15, 2025
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje

November 15, 2025
Fashi Da Makami: An Yanke Wa ’Yan Nijeriya Hudu Mazauna Birtaniya Hukuncin Daurin Shekara 55 A Gidan Yari

Fashi Da Makami: An Yanke Wa ’Yan Nijeriya Hudu Mazauna Birtaniya Hukuncin Daurin Shekara 55 A Gidan Yari

November 15, 2025
Shugaban APC Na Kano Ya Nemi Afuwa Daga Al’ummar Fagge Kan Kalamansa

Shugaban APC Na Kano Ya Nemi Afuwa Daga Al’ummar Fagge Kan Kalamansa

November 15, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Cafke Wani Da Ake Zargin Dan Ta’adda Ne A Jihar Kebbi

November 15, 2025
Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

November 14, 2025
NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

November 14, 2025
NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

November 14, 2025
Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

November 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.