• English
  • Business News
Saturday, July 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mun Dandana Kudarmu A 2022, In Ji ‘Yan Kasuwa A Jihar Gombe

by Leadership Hausa
2 years ago
in Labarai
0
Mun Dandana Kudarmu A 2022, In Ji ‘Yan Kasuwa A Jihar Gombe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A watan farko da shigowa sabuwar shekarar 2023 (wato janairu), ‘yan kasuwa a jihar Gombe, waiwaye suka yi a shekarar da ta gabace ta, wato 2022 inda da yawa sukayi kukan cewa, sun dandana kudar su a shekarar, saboda, hauhawar farashi a kan duk kayayyakin kasuwanci, musamman abinci da kayan masarufi da kuma rashin tsaro, suna mai kukan cewa ‘’kar Allah ya sake maimaita mana irin wannan masifa’’.

A wani zagaya, da ‘yan jarida suka yi a ranar Litinin din wannan makon, ta ji wasu da dama cikin yan kasuwa, manya da kanana, suna kukan cewa, ‘’gwamnatin Buhari ba ta’ yankasuwa ba ce, domin mu bamu taba fuskantar rayuwa kamr a karkashin mulkin shi (Buhari) ba’’.

  • Tsokaci Kan Dukan Da Wasu Maza Ke Wa Matansu
  • An Yi Gwanjon Rigar Da Pele Ya Buga Kofin Duniya Na Karshe Da Ita

Fitaccen dan kasuwan kayayyakin gini, kuma shugaban Sabham (Nig) Ltd, Gombe, Alhaji Sabo Adamu, ya ce, ai sake bada umurnin a bude kan iyakokin kasar bayan rufe su, na daya daga cikin abubuwan da suka jawo hauhawar farashi a Najeriya.

‘’Don haka, Gwamnatin ta sake tunani a kan lamarin ta kuma bada unurni a rurrufe bodojin, saboda hakan zai sa ‘yan kasa su dukufa wajen bunkasa kayayyakin cikin gida, kaya da abinci su yawaita, kuma za’a samu saukin rayuwa’’ inji shi.

A hira da Babban Manajan sanannen kamfanin hada – hadar dilolin atamfofi da kayayyakin amfanin yau da kullum na maza da mata da yara, wato SAN HUSSEIN SUPER MARKETS Gombe, Alhaji Muhammad Umar Kawu, Shi nuna godiya ya yi ga Allah da shigowar sabuwar shekarar 2023 lami lafiya.

Labarai Masu Nasaba

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

Dangane da tsadar rayuwa da ‘Yan Najeriya suke ta kuka a kai kuwa, sai Alhaji Muhammad Kawu yace, ‘‘mu koma ga Allah, duk da mun san irin halin da muka shiga sai adu’a, ita ce kawai mafita ‘’.

Sai ya shawarci ‘Yan Jihar ta Gombe, da ma ‘yan kasa baki daya, da su rinka yi wa Shugabanni Addu’a, maimakon aibantasu , yana kuma matukar hamdala da kamfanonin SAN HUSSEIN, da suka kara bunkasa  saboda sassautawa kwastomomin su farashin kayayyaki, ‘‘Don haka, ina fata ‘Yan kasuwa, takwarorin mu, su tausayawa talakokin mu wajen rage tsadar kayayyakin su saboda yin haka ce zai sa suga alheri da ci gaba a kasuwancin su’’.

Manajan kuma, sai ya yi fatan Allah Ya kawo wa Najeriya ci gaba a wannan sabon shekara ta 2023, da kuma adu’ar Allah Yasa zabubbuka masu zuwa, za’a yisu cikin lumana da kwanciyar hankali. Kusan kashi 75 cikin dari (75%) da aka zanta da su, sun dora laifin ne akan Gwamnatin Shugaba Buhari suna nanata cewar ‘’ kar Allah Ya sake maimaita mana’’.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan KasuwaGombe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ra’ayoyinku  A Kan Yarfen Da ‘Yan Takarar Shugabancin Kasa  Ke Yi Wa Junansu

Next Post

Benzema Ya Karya Tarihin Raul Gonzalez

Related

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa
Labarai

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

3 hours ago
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP
Manyan Labarai

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

3 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

6 hours ago
Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC
Manyan Labarai

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

7 hours ago
Abin Da Ya Sa ‘Yan Nijeriya Ba Su Mori Dimokuradiyya Ba Har Yanzu –Jega
Labarai

Shirin Tinubu Kan Kiwon Dabbobi Zai Samar Da Ayyukan Yi Miliyan 5 Ga Matasa – Jega

9 hours ago
‘Yan Kasuwa Na Kalubalantar Rage Faranshin Man Dangote
Labarai

‘Yan Kasuwa Na Kalubalantar Rage Faranshin Man Dangote

10 hours ago
Next Post
Benzema Ya Karya Tarihin Raul Gonzalez

Benzema Ya Karya Tarihin Raul Gonzalez

LABARAI MASU NASABA

Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

July 5, 2025
Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

July 5, 2025
Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (5)

Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (5)

July 5, 2025
ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

July 5, 2025
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

July 5, 2025
Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

July 5, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

July 5, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

July 5, 2025
Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

July 5, 2025
Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya

Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya

July 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.