• Leadership Hausa
Saturday, April 1, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mun Dandana Kudarmu A 2022, In Ji ‘Yan Kasuwa A Jihar Gombe

by Leadership Hausa
2 months ago
in Labarai
0
Mun Dandana Kudarmu A 2022, In Ji ‘Yan Kasuwa A Jihar Gombe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A watan farko da shigowa sabuwar shekarar 2023 (wato janairu), ‘yan kasuwa a jihar Gombe, waiwaye suka yi a shekarar da ta gabace ta, wato 2022 inda da yawa sukayi kukan cewa, sun dandana kudar su a shekarar, saboda, hauhawar farashi a kan duk kayayyakin kasuwanci, musamman abinci da kayan masarufi da kuma rashin tsaro, suna mai kukan cewa ‘’kar Allah ya sake maimaita mana irin wannan masifa’’.

A wani zagaya, da ‘yan jarida suka yi a ranar Litinin din wannan makon, ta ji wasu da dama cikin yan kasuwa, manya da kanana, suna kukan cewa, ‘’gwamnatin Buhari ba ta’ yankasuwa ba ce, domin mu bamu taba fuskantar rayuwa kamr a karkashin mulkin shi (Buhari) ba’’.

  • Tsokaci Kan Dukan Da Wasu Maza Ke Wa Matansu
  • An Yi Gwanjon Rigar Da Pele Ya Buga Kofin Duniya Na Karshe Da Ita

Fitaccen dan kasuwan kayayyakin gini, kuma shugaban Sabham (Nig) Ltd, Gombe, Alhaji Sabo Adamu, ya ce, ai sake bada umurnin a bude kan iyakokin kasar bayan rufe su, na daya daga cikin abubuwan da suka jawo hauhawar farashi a Najeriya.

‘’Don haka, Gwamnatin ta sake tunani a kan lamarin ta kuma bada unurni a rurrufe bodojin, saboda hakan zai sa ‘yan kasa su dukufa wajen bunkasa kayayyakin cikin gida, kaya da abinci su yawaita, kuma za’a samu saukin rayuwa’’ inji shi.

A hira da Babban Manajan sanannen kamfanin hada – hadar dilolin atamfofi da kayayyakin amfanin yau da kullum na maza da mata da yara, wato SAN HUSSEIN SUPER MARKETS Gombe, Alhaji Muhammad Umar Kawu, Shi nuna godiya ya yi ga Allah da shigowar sabuwar shekarar 2023 lami lafiya.

Labarai Masu Nasaba

An Yanke Wa Wasu ‘Yan China 2 Hukuncin Daurin Shekaru 12 A Sakkwato

Zababben Gwamnan Katsina Ya Gana Da Buhari, Ya Ce Matsalar Tsaro Zai Fi Bai Wa Muhimmanci 

Dangane da tsadar rayuwa da ‘Yan Najeriya suke ta kuka a kai kuwa, sai Alhaji Muhammad Kawu yace, ‘‘mu koma ga Allah, duk da mun san irin halin da muka shiga sai adu’a, ita ce kawai mafita ‘’.

Sai ya shawarci ‘Yan Jihar ta Gombe, da ma ‘yan kasa baki daya, da su rinka yi wa Shugabanni Addu’a, maimakon aibantasu , yana kuma matukar hamdala da kamfanonin SAN HUSSEIN, da suka kara bunkasa  saboda sassautawa kwastomomin su farashin kayayyaki, ‘‘Don haka, ina fata ‘Yan kasuwa, takwarorin mu, su tausayawa talakokin mu wajen rage tsadar kayayyakin su saboda yin haka ce zai sa suga alheri da ci gaba a kasuwancin su’’.

Manajan kuma, sai ya yi fatan Allah Ya kawo wa Najeriya ci gaba a wannan sabon shekara ta 2023, da kuma adu’ar Allah Yasa zabubbuka masu zuwa, za’a yisu cikin lumana da kwanciyar hankali. Kusan kashi 75 cikin dari (75%) da aka zanta da su, sun dora laifin ne akan Gwamnatin Shugaba Buhari suna nanata cewar ‘’ kar Allah Ya sake maimaita mana’’.

Tags: 'Yan KasuwaGombe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ra’ayoyinku  A Kan Yarfen Da ‘Yan Takarar Shugabancin Kasa  Ke Yi Wa Junansu

Next Post

Benzema Ya Karya Tarihin Raul Gonzalez

Related

An Yanke Wa Wasu ‘Yan China 2 Hukuncin Daurin Shekaru 12 A Sakkwato
Labarai

An Yanke Wa Wasu ‘Yan China 2 Hukuncin Daurin Shekaru 12 A Sakkwato

8 hours ago
Zababben Gwamnan Katsina Ya Gana Da Buhari, Ya Ce Matsalar Tsaro Zai Fi Bai Wa Muhimmanci 
Labarai

Zababben Gwamnan Katsina Ya Gana Da Buhari, Ya Ce Matsalar Tsaro Zai Fi Bai Wa Muhimmanci 

9 hours ago
Mutum 14 Sun Shiga Hannun ‘Yan Sanda A Kano Kan Aikata Fashi Da Makami
Labarai

Mutum 14 Sun Shiga Hannun ‘Yan Sanda A Kano Kan Aikata Fashi Da Makami

10 hours ago
Ba Zan Tsoma Baki A Gwamnatin Abba Ba –Kwankwaso
Manyan Labarai

Ba Zan Tsoma Baki A Gwamnatin Abba Ba –Kwankwaso

11 hours ago
Har Yanzu Ni Ke Da Cikakken Iko A Matsayin Gwamnan Kano —Ganduje Ga Abba Gida-Gida
Manyan Labarai

Har Yanzu Ni Ke Da Cikakken Iko A Matsayin Gwamnan Kano —Ganduje Ga Abba Gida-Gida

12 hours ago
Elon Musk Ya Zarce Barack Obama Yawan Mabiya A Twitter
Manyan Labarai

Elon Musk Ya Zarce Barack Obama Yawan Mabiya A Twitter

13 hours ago
Next Post
Benzema Ya Karya Tarihin Raul Gonzalez

Benzema Ya Karya Tarihin Raul Gonzalez

LABARAI MASU NASABA

An Yanke Wa Wasu ‘Yan China 2 Hukuncin Daurin Shekaru 12 A Sakkwato

An Yanke Wa Wasu ‘Yan China 2 Hukuncin Daurin Shekaru 12 A Sakkwato

March 31, 2023
Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Irin Su Na Farko A Duniya

Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Irin Su Na Farko A Duniya

March 31, 2023
Zababben Gwamnan Katsina Ya Gana Da Buhari, Ya Ce Matsalar Tsaro Zai Fi Bai Wa Muhimmanci 

Zababben Gwamnan Katsina Ya Gana Da Buhari, Ya Ce Matsalar Tsaro Zai Fi Bai Wa Muhimmanci 

March 31, 2023
Kasar Sin Ta Bayar Da Shawarwari Dangane Da Yadda Za A Aiwatar Da Sanarwar Vienna Yadda Ya Kamata

Kasar Sin Ta Bayar Da Shawarwari Dangane Da Yadda Za A Aiwatar Da Sanarwar Vienna Yadda Ya Kamata

March 31, 2023
Mutum 14 Sun Shiga Hannun ‘Yan Sanda A Kano Kan Aikata Fashi Da Makami

Mutum 14 Sun Shiga Hannun ‘Yan Sanda A Kano Kan Aikata Fashi Da Makami

March 31, 2023
Ana Fatan A Hada Kai Wajen Shawo Kan Kalubalen Dake Addabar Duniya

Ana Fatan A Hada Kai Wajen Shawo Kan Kalubalen Dake Addabar Duniya

March 31, 2023
Ba Zan Tsoma Baki A Gwamnatin Abba Ba –Kwankwaso

Ba Zan Tsoma Baki A Gwamnatin Abba Ba –Kwankwaso

March 31, 2023
Taron Kolin Demokuradiyya Na Amurka Ya Shaidawa Duniya Ma’auni Biyu Da Amurka Ta Dauka Kan Batun Demokuradiyya

Taron Kolin Demokuradiyya Na Amurka Ya Shaidawa Duniya Ma’auni Biyu Da Amurka Ta Dauka Kan Batun Demokuradiyya

March 31, 2023
Har Yanzu Ni Ke Da Cikakken Iko A Matsayin Gwamnan Kano —Ganduje Ga Abba Gida-Gida

Har Yanzu Ni Ke Da Cikakken Iko A Matsayin Gwamnan Kano —Ganduje Ga Abba Gida-Gida

March 31, 2023
Boao: Kasar Sin Ta Karfafa Gwiwar Kasa Da Kasa

Boao: Kasar Sin Ta Karfafa Gwiwar Kasa Da Kasa

March 31, 2023
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.