ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mun Dandana Kudarmu A 2022, In Ji ‘Yan Kasuwa A Jihar Gombe

by Leadership Hausa
3 years ago
Gombe

A watan farko da shigowa sabuwar shekarar 2023 (wato janairu), ‘yan kasuwa a jihar Gombe, waiwaye suka yi a shekarar da ta gabace ta, wato 2022 inda da yawa sukayi kukan cewa, sun dandana kudar su a shekarar, saboda, hauhawar farashi a kan duk kayayyakin kasuwanci, musamman abinci da kayan masarufi da kuma rashin tsaro, suna mai kukan cewa ‘’kar Allah ya sake maimaita mana irin wannan masifa’’.

A wani zagaya, da ‘yan jarida suka yi a ranar Litinin din wannan makon, ta ji wasu da dama cikin yan kasuwa, manya da kanana, suna kukan cewa, ‘’gwamnatin Buhari ba ta’ yankasuwa ba ce, domin mu bamu taba fuskantar rayuwa kamr a karkashin mulkin shi (Buhari) ba’’.

  • Tsokaci Kan Dukan Da Wasu Maza Ke Wa Matansu
  • An Yi Gwanjon Rigar Da Pele Ya Buga Kofin Duniya Na Karshe Da Ita

Fitaccen dan kasuwan kayayyakin gini, kuma shugaban Sabham (Nig) Ltd, Gombe, Alhaji Sabo Adamu, ya ce, ai sake bada umurnin a bude kan iyakokin kasar bayan rufe su, na daya daga cikin abubuwan da suka jawo hauhawar farashi a Najeriya.

ADVERTISEMENT

‘’Don haka, Gwamnatin ta sake tunani a kan lamarin ta kuma bada unurni a rurrufe bodojin, saboda hakan zai sa ‘yan kasa su dukufa wajen bunkasa kayayyakin cikin gida, kaya da abinci su yawaita, kuma za’a samu saukin rayuwa’’ inji shi.

A hira da Babban Manajan sanannen kamfanin hada – hadar dilolin atamfofi da kayayyakin amfanin yau da kullum na maza da mata da yara, wato SAN HUSSEIN SUPER MARKETS Gombe, Alhaji Muhammad Umar Kawu, Shi nuna godiya ya yi ga Allah da shigowar sabuwar shekarar 2023 lami lafiya.

LABARAI MASU NASABA

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Dangane da tsadar rayuwa da ‘Yan Najeriya suke ta kuka a kai kuwa, sai Alhaji Muhammad Kawu yace, ‘‘mu koma ga Allah, duk da mun san irin halin da muka shiga sai adu’a, ita ce kawai mafita ‘’.

Sai ya shawarci ‘Yan Jihar ta Gombe, da ma ‘yan kasa baki daya, da su rinka yi wa Shugabanni Addu’a, maimakon aibantasu , yana kuma matukar hamdala da kamfanonin SAN HUSSEIN, da suka kara bunkasa  saboda sassautawa kwastomomin su farashin kayayyaki, ‘‘Don haka, ina fata ‘Yan kasuwa, takwarorin mu, su tausayawa talakokin mu wajen rage tsadar kayayyakin su saboda yin haka ce zai sa suga alheri da ci gaba a kasuwancin su’’.

Manajan kuma, sai ya yi fatan Allah Ya kawo wa Najeriya ci gaba a wannan sabon shekara ta 2023, da kuma adu’ar Allah Yasa zabubbuka masu zuwa, za’a yisu cikin lumana da kwanciyar hankali. Kusan kashi 75 cikin dari (75%) da aka zanta da su, sun dora laifin ne akan Gwamnatin Shugaba Buhari suna nanata cewar ‘’ kar Allah Ya sake maimaita mana’’.

Gombe
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
  • Leadership Hausa
    Ikirarin Cewa Sanata Abdul’aziz Yari Abubakar, Marafan Sokoto, Nauyi Ne Ga Jihar Zamfara Da Jam’iyyar APC Ba Ta Da Tushe
  • Leadership Hausa
    Nazarin Kisan Gillar Da ‘Yan Kato Da Gora Suka Yi Wa Wani Matashi A Biniwe

MASU ALAKA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Next Post
Benzema Ya Karya Tarihin Raul Gonzalez

Benzema Ya Karya Tarihin Raul Gonzalez

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.