• English
  • Business News
Saturday, September 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

“Mun Yi Nasarar Yakar ‘Yan Bindiga”, Gwamna Lawal Ya Shaida Wa Bankin Duniya

by Sulaiman
7 months ago
in Labarai
0
“Mun Yi Nasarar Yakar ‘Yan Bindiga”, Gwamna Lawal Ya Shaida Wa Bankin Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal ya shaida wa Bankin Duniya cewa sannu a hankali, gwamnatinsa na samun nasara a kan ta’addanci a duk faɗin jihar. 

 

A Juma’ar da ta gabata ne gwamnan ya kai wata ziyara ofishin Bankin na Duniya

  • Ba Laifi A Binciki Gwamnatin Mahaifina, Amma A Yi Da Zuciya Ɗaya  – Bello El-Rufai
  • An Kaddamar Da Atisayen Soja Kan Teku Mai Taken “Zaman Lafiya-2025”

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris ya sanya wa hannu, ya bayyana cewa tattaunawar da ta gudana tsakanin gwamnan da jami’an Bankin Duniyar, ta mayar da hankali ne wajen ci gaban fannonin ilimi, lafiya, noma da ɗumamar yanayi.

 

Labarai Masu Nasaba

Ilimi Shi Ne Matakin Nasarar Rayuwar Duniya Da Lahira – Yerima Shettima

NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai

Sanarwar ta kuma bayyana cewa wannan ziyara ta gwamnan, za ta ƙarfafa haɗin gwiwa tsakanin gwamnatin jihar Zamfara da Bankin na Duniya.

 

Cikin jawabin sa a wurin, Gwamna Dauda Lawal ya jaddada ƙudirin gwamnatin sa na ƙarfafa dangantakar ta Bankin Duniyar.

 

“Ina so in fara da nuna godiya ta ga Bankin Duniya game da tallafin da ya ke bayarwa a jihar mu. Mun jingina da manufofin Bankin Duniya wajen inganta rayuwar al’ummar mu kawar da talauci da ci gaban ayyukan inganta rayuwa.

 

“Muna sane da ƙalubalen da muka fuskanta, wanda ya shafi gudanar da ayyukan ci gaba a jihar Zamfara, musamman waɗanda suka samu matsala wajen aiwatarwa, sakamakon yanayin da aka shiga. Amma, lallai babu shakka muna samun ci gaba wajen magance matsalolin, lamurra na komawa daidai.

 

“Mun ɗauki ƙwararan matakai wajen magance matsalolin tsaron ta hanyar ƙara yawan ’yan sintiri da tsare-tsare don daƙile barazanar.

 

“Gwamnatinmu ta duƙufa wajen tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyi ta hanyar samar da isassun kayan aiki da tallafi ga jami’an tsaro domin wanzar da zaman lafiya da kwanciyar hankali.”

 

Gwamna Lawal ya bai wa ma’aikatan Bankin Duniya tabbacin kare lafiyarsu a yayin ziyarar su, da suka haɗa da amintattun masauki, sufuri, da hanyoyin sadarwa mai kyau.

 

Gwamna Lawal ya bai wa ma’aikatan Bankin Duniya tabbacin kare lafiyarsu a yayin ziyarar su ta tallafi da sa ido a jihar Zamfara.

 

“Ina tabbatar wa Bankin Duniya cewa mun samar da hanyoyin da za a ci gaba da samar da tsaro don magance duk wata barazana da ta kunno kai da kuma tabbatar da kyakkyawan yanayi ga dukkan abokan hulɗar ci gaba.

 

“Mun daƙile hare-haren ‘yan bindiga a manyan titunanmu, ƙauyuka da garuruwanmu. A hankali muna samun nasara a yaƙin da muke yi da masu laifi, kuma rayuwa tana komawa daidai ga al’ummominmu. Wannan ya bayyana a cikin adadin al’amuran da ke faruwa a kullum da kuma yadda ake ƙara aiwatar da ayyuka cikin kwaciyar hankali a faɗin jihar Zamfara.

 

“Zan ƙarƙare da miƙa goron gayyatarmu ga Daraktan Ƙasa da ya ziyarci jihar Zamfara nan ba da daɗewa ba domin ganin an aiwatar da dukkan shirye-shiryen da Bankin Duniya ke tallafawa da kuma ƙoƙarin da muke yi na sauya yanayin jiharmu.”

 

Daraktan Bankin Duniya a Nijeriya, Dr. Ndiame Diop, ya yaba wa Gwamna Lawal bisa yadda ya kyautata yanayin jihar Zamfara.

 

“Na gamsu da tsarin da ka sanya. Ina taya ka murnar samun irin waɗannan nasarori a cikin ƙanƙanin lokaci.”

 

A yayin taron, Jagoran NG-CARES ya bayyana irin nasarorin da aka samu a cikin tsarin aiwatarwa a Zamfara. “Ba wai a sauran jihohin Nijeriya muke ɗaukar irin wannan tsari na Zamfara ba, har ma muna miƙa shi ga wasu ƙasashe domin aiwatarwa, dole ne in yaba wa gwamna da gwamnatin jihar kan ƙoƙarin da suke yi,” inji ta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Fashi Da Makami Sun Kashe Limamin Coci A Gombe

Next Post

Atiku Ya Ziyarci Obasanjo A Abeokuta Domin Wata Ganawar Sirri 

Related

Labarai

Ilimi Shi Ne Matakin Nasarar Rayuwar Duniya Da Lahira – Yerima Shettima

3 hours ago
NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai
Manyan Labarai

NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai

3 hours ago
Maulidi: Gwamnan Zamfara Ya Taya Al’ummar Musulmi Murna, Ya Buƙaci A Dage Da Addu’o’in Samun Zaman Lafiya
Labarai

Maulidi: Gwamnan Zamfara Ya Taya Al’ummar Musulmi Murna, Ya Buƙaci A Dage Da Addu’o’in Samun Zaman Lafiya

6 hours ago
Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 
Labarai

Ana Ci Gaba Da Caccakar El-rufai Kan Kalamansa Game Da Tsaron Kasa

15 hours ago
Yadda Al’ummar Da Ke Zaune Da ‘Yan Bindiga Ke Rayuwa A Zamfara
Labarai

Duk Da Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ana Ci Gaba Da Kai Hare-hare Wasu Yankunan Zamfara

16 hours ago
Ban Yi Kuskure Wajen Zaben Kashim A Matsayin Mataimaki Ba – Tinubu
Labarai

Ban Yi Kuskure Wajen Zaben Kashim A Matsayin Mataimaki Ba – Tinubu

17 hours ago
Next Post
Atiku Ya Ziyarci Obasanjo A Abeokuta Domin Wata Ganawar Sirri 

Atiku Ya Ziyarci Obasanjo A Abeokuta Domin Wata Ganawar Sirri 

LABARAI MASU NASABA

A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

Kungiyoyi Da Abokan Arziki Na Ci Gaba Da Taya Dantsoho Murna

September 6, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

September 6, 2025
Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

September 6, 2025

Ilimi Shi Ne Matakin Nasarar Rayuwar Duniya Da Lahira – Yerima Shettima

September 6, 2025
NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai

NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai

September 6, 2025
Maulidi: Gwamnan Zamfara Ya Taya Al’ummar Musulmi Murna, Ya Buƙaci A Dage Da Addu’o’in Samun Zaman Lafiya

Maulidi: Gwamnan Zamfara Ya Taya Al’ummar Musulmi Murna, Ya Buƙaci A Dage Da Addu’o’in Samun Zaman Lafiya

September 6, 2025
Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

September 5, 2025
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

September 5, 2025
Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping

Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping

September 5, 2025
Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 

Ana Ci Gaba Da Caccakar El-rufai Kan Kalamansa Game Da Tsaron Kasa

September 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.