ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

“Mun Yi Nasarar Yakar ‘Yan Bindiga”, Gwamna Lawal Ya Shaida Wa Bankin Duniya

by Sulaiman
2 years ago
Gwamna lawal

Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal ya shaida wa Bankin Duniya cewa sannu a hankali, gwamnatinsa na samun nasara a kan ta’addanci a duk faɗin jihar. 

 

A Juma’ar da ta gabata ne gwamnan ya kai wata ziyara ofishin Bankin na Duniya

ADVERTISEMENT
  • Ba Laifi A Binciki Gwamnatin Mahaifina, Amma A Yi Da Zuciya Ɗaya  – Bello El-Rufai
  • An Kaddamar Da Atisayen Soja Kan Teku Mai Taken “Zaman Lafiya-2025”

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris ya sanya wa hannu, ya bayyana cewa tattaunawar da ta gudana tsakanin gwamnan da jami’an Bankin Duniyar, ta mayar da hankali ne wajen ci gaban fannonin ilimi, lafiya, noma da ɗumamar yanayi.

 

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Sanarwar ta kuma bayyana cewa wannan ziyara ta gwamnan, za ta ƙarfafa haɗin gwiwa tsakanin gwamnatin jihar Zamfara da Bankin na Duniya.

 

Cikin jawabin sa a wurin, Gwamna Dauda Lawal ya jaddada ƙudirin gwamnatin sa na ƙarfafa dangantakar ta Bankin Duniyar.

 

“Ina so in fara da nuna godiya ta ga Bankin Duniya game da tallafin da ya ke bayarwa a jihar mu. Mun jingina da manufofin Bankin Duniya wajen inganta rayuwar al’ummar mu kawar da talauci da ci gaban ayyukan inganta rayuwa.

 

“Muna sane da ƙalubalen da muka fuskanta, wanda ya shafi gudanar da ayyukan ci gaba a jihar Zamfara, musamman waɗanda suka samu matsala wajen aiwatarwa, sakamakon yanayin da aka shiga. Amma, lallai babu shakka muna samun ci gaba wajen magance matsalolin, lamurra na komawa daidai.

 

“Mun ɗauki ƙwararan matakai wajen magance matsalolin tsaron ta hanyar ƙara yawan ’yan sintiri da tsare-tsare don daƙile barazanar.

 

“Gwamnatinmu ta duƙufa wajen tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyi ta hanyar samar da isassun kayan aiki da tallafi ga jami’an tsaro domin wanzar da zaman lafiya da kwanciyar hankali.”

 

Gwamna Lawal ya bai wa ma’aikatan Bankin Duniya tabbacin kare lafiyarsu a yayin ziyarar su, da suka haɗa da amintattun masauki, sufuri, da hanyoyin sadarwa mai kyau.

 

Gwamna Lawal ya bai wa ma’aikatan Bankin Duniya tabbacin kare lafiyarsu a yayin ziyarar su ta tallafi da sa ido a jihar Zamfara.

 

“Ina tabbatar wa Bankin Duniya cewa mun samar da hanyoyin da za a ci gaba da samar da tsaro don magance duk wata barazana da ta kunno kai da kuma tabbatar da kyakkyawan yanayi ga dukkan abokan hulɗar ci gaba.

 

“Mun daƙile hare-haren ‘yan bindiga a manyan titunanmu, ƙauyuka da garuruwanmu. A hankali muna samun nasara a yaƙin da muke yi da masu laifi, kuma rayuwa tana komawa daidai ga al’ummominmu. Wannan ya bayyana a cikin adadin al’amuran da ke faruwa a kullum da kuma yadda ake ƙara aiwatar da ayyuka cikin kwaciyar hankali a faɗin jihar Zamfara.

 

“Zan ƙarƙare da miƙa goron gayyatarmu ga Daraktan Ƙasa da ya ziyarci jihar Zamfara nan ba da daɗewa ba domin ganin an aiwatar da dukkan shirye-shiryen da Bankin Duniya ke tallafawa da kuma ƙoƙarin da muke yi na sauya yanayin jiharmu.”

 

Daraktan Bankin Duniya a Nijeriya, Dr. Ndiame Diop, ya yaba wa Gwamna Lawal bisa yadda ya kyautata yanayin jihar Zamfara.

 

“Na gamsu da tsarin da ka sanya. Ina taya ka murnar samun irin waɗannan nasarori a cikin ƙanƙanin lokaci.”

 

A yayin taron, Jagoran NG-CARES ya bayyana irin nasarorin da aka samu a cikin tsarin aiwatarwa a Zamfara. “Ba wai a sauran jihohin Nijeriya muke ɗaukar irin wannan tsari na Zamfara ba, har ma muna miƙa shi ga wasu ƙasashe domin aiwatarwa, dole ne in yaba wa gwamna da gwamnatin jihar kan ƙoƙarin da suke yi,” inji ta.

Gwamna lawal
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato
  • Sulaiman
    Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya
  • Sulaiman
    Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta
  • Sulaiman
    Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

MASU ALAKA

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

September 10, 2026
Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci
Manyan Labarai

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026
Gwamna lawal
Labarai

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Next Post
Atiku Ya Ziyarci Obasanjo A Abeokuta Domin Wata Ganawar Sirri 

Atiku Ya Ziyarci Obasanjo A Abeokuta Domin Wata Ganawar Sirri 

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

September 10, 2026
Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

September 10, 2026
Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

September 10, 2026
Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

September 10, 2026
Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026
Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

September 10, 2026
Gwamna lawal

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Gwamna lawal

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.