ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

“Mun Yi Nasarar Yakar ‘Yan Bindiga”, Gwamna Lawal Ya Shaida Wa Bankin Duniya

by Sulaiman
1 year ago
Gwamna lawal

Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal ya shaida wa Bankin Duniya cewa sannu a hankali, gwamnatinsa na samun nasara a kan ta’addanci a duk faɗin jihar. 

 

A Juma’ar da ta gabata ne gwamnan ya kai wata ziyara ofishin Bankin na Duniya

ADVERTISEMENT
  • Ba Laifi A Binciki Gwamnatin Mahaifina, Amma A Yi Da Zuciya Ɗaya  – Bello El-Rufai
  • An Kaddamar Da Atisayen Soja Kan Teku Mai Taken “Zaman Lafiya-2025”

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris ya sanya wa hannu, ya bayyana cewa tattaunawar da ta gudana tsakanin gwamnan da jami’an Bankin Duniyar, ta mayar da hankali ne wajen ci gaban fannonin ilimi, lafiya, noma da ɗumamar yanayi.

 

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Sanarwar ta kuma bayyana cewa wannan ziyara ta gwamnan, za ta ƙarfafa haɗin gwiwa tsakanin gwamnatin jihar Zamfara da Bankin na Duniya.

 

Cikin jawabin sa a wurin, Gwamna Dauda Lawal ya jaddada ƙudirin gwamnatin sa na ƙarfafa dangantakar ta Bankin Duniyar.

 

“Ina so in fara da nuna godiya ta ga Bankin Duniya game da tallafin da ya ke bayarwa a jihar mu. Mun jingina da manufofin Bankin Duniya wajen inganta rayuwar al’ummar mu kawar da talauci da ci gaban ayyukan inganta rayuwa.

 

“Muna sane da ƙalubalen da muka fuskanta, wanda ya shafi gudanar da ayyukan ci gaba a jihar Zamfara, musamman waɗanda suka samu matsala wajen aiwatarwa, sakamakon yanayin da aka shiga. Amma, lallai babu shakka muna samun ci gaba wajen magance matsalolin, lamurra na komawa daidai.

 

“Mun ɗauki ƙwararan matakai wajen magance matsalolin tsaron ta hanyar ƙara yawan ’yan sintiri da tsare-tsare don daƙile barazanar.

 

“Gwamnatinmu ta duƙufa wajen tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyi ta hanyar samar da isassun kayan aiki da tallafi ga jami’an tsaro domin wanzar da zaman lafiya da kwanciyar hankali.”

 

Gwamna Lawal ya bai wa ma’aikatan Bankin Duniya tabbacin kare lafiyarsu a yayin ziyarar su, da suka haɗa da amintattun masauki, sufuri, da hanyoyin sadarwa mai kyau.

 

Gwamna Lawal ya bai wa ma’aikatan Bankin Duniya tabbacin kare lafiyarsu a yayin ziyarar su ta tallafi da sa ido a jihar Zamfara.

 

“Ina tabbatar wa Bankin Duniya cewa mun samar da hanyoyin da za a ci gaba da samar da tsaro don magance duk wata barazana da ta kunno kai da kuma tabbatar da kyakkyawan yanayi ga dukkan abokan hulɗar ci gaba.

 

“Mun daƙile hare-haren ‘yan bindiga a manyan titunanmu, ƙauyuka da garuruwanmu. A hankali muna samun nasara a yaƙin da muke yi da masu laifi, kuma rayuwa tana komawa daidai ga al’ummominmu. Wannan ya bayyana a cikin adadin al’amuran da ke faruwa a kullum da kuma yadda ake ƙara aiwatar da ayyuka cikin kwaciyar hankali a faɗin jihar Zamfara.

 

“Zan ƙarƙare da miƙa goron gayyatarmu ga Daraktan Ƙasa da ya ziyarci jihar Zamfara nan ba da daɗewa ba domin ganin an aiwatar da dukkan shirye-shiryen da Bankin Duniya ke tallafawa da kuma ƙoƙarin da muke yi na sauya yanayin jiharmu.”

 

Daraktan Bankin Duniya a Nijeriya, Dr. Ndiame Diop, ya yaba wa Gwamna Lawal bisa yadda ya kyautata yanayin jihar Zamfara.

 

“Na gamsu da tsarin da ka sanya. Ina taya ka murnar samun irin waɗannan nasarori a cikin ƙanƙanin lokaci.”

 

A yayin taron, Jagoran NG-CARES ya bayyana irin nasarorin da aka samu a cikin tsarin aiwatarwa a Zamfara. “Ba wai a sauran jihohin Nijeriya muke ɗaukar irin wannan tsari na Zamfara ba, har ma muna miƙa shi ga wasu ƙasashe domin aiwatarwa, dole ne in yaba wa gwamna da gwamnatin jihar kan ƙoƙarin da suke yi,” inji ta.

Gwamna lawal
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu
  • Sulaiman
    Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS
  • Sulaiman
    An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara
Tsaro

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026
Manyan Labarai

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano
Labarai

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
Next Post
Atiku Ya Ziyarci Obasanjo A Abeokuta Domin Wata Ganawar Sirri 

Atiku Ya Ziyarci Obasanjo A Abeokuta Domin Wata Ganawar Sirri 

LABARAI MASU NASABA

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

June 25, 2026
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

June 25, 2026
Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.