• English
  • Business News
Friday, October 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Muna Bin ‘Yan Bindiga Har Maboyarsu Mu Fatattake Su – Minista

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Yajin aiki

Gwamnatin Tarayya ta ce tana aiki ba dare ba rana don magance matsalolin tsaro da ake fama da ita a halin yanzu, ta hanyar yaki da rashin tsaro zuwa matsugunan masu aikata laifuka a fadin kasar nan.

Ministan ya ce a cikin makon da ya gabata, an kawar da ‘yan fashi, masu garkuwa da mutane da kuma ‘yan bindiga da dama, ko kuma aka kama su.

  • Jami’an Tsaro Sun Kama Ɗan Bindigar Da Ake Zargi Da Kashe Nabeeha
  • Zaben Cike Gurbin Makera: ‘Yan Takara Sun Yi Wa Liman Mubaya’a

Ministan yada labarai da wayar da kan jama’a Mohammed Idris Malagi ne ya bayyana haka a cikin wata sanarwa a Abuja.

“Ba zai yiwu a yi watsi da gaskiya a wannann lokaci na kalubalen da muka samu kanmu a matsayinmu na al’umma: illar hauhawar farashin kayayyaki a kan kasafin kudin mutane da na gida, da kuma barazanar tsaro a sassan kasar nan.

“Amma wannan wani bangare ne na labarin. Kamar yadda muhimman matakai daban-daban da gwamnatin tarayyar Nijeriya karkashin jagorancin Bola Ahmed Tinubu ke dauka na tunkarar duk wadannan kalubalen.
“Mun amince da aiki da kuma nauyin kulawar da Gwamnatin Tarayya ta rataya a wuyan kowane dan Najeriya, a tsakanin shekaru, jinsi, addini, kabila, da zamantakewa,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

Ranar Abinci Ta Duniya: NAWIA Ta Tallafawa Mata 114  Da Kayan Aikin Gona A Zamfara

Shugaban Ƙasa Zai Sake Nazari Kan Mutanen Da Aka Yi Wa Afuwa

Kashe-kashen Filato
Ministan ya ce hukumomin tsaro na taka tsan-tsan wajen tunkarar matsalolin da suka sake kunno kai a Jihar Filato da sauran yankunan da ke fama da rikici a daidai lokacin da shugaba Tinubu ya yi alkawarin samar da zaman lafiya a duk fadin kasar.

Ya kuma ba da tabbacin cewa za a gurfanar da masu aikata kisan-kiyashi da tashe-tashen hankula a wasu sassan kasar nan a Filato.

“Hakika rikicin da ya sake kunno kai a Jihar Filato abin takaici ne matuka, kuma muna ba da tabbacin cewa duk wadanda suka haddasa tashin hankali a can da kuma ko’ina a fadin kasar nan, an gurfanar da su a gaban kuliya. Za a yi adalci, kuma za a maido da zaman lafiya a dukkan al’ummomin da abin ya shafa.

“Muna jinjina wa jiga-jigan jami’an tsaro da na leken asiri wadanda ba sa barin wani abu don tabbatar da cewa muna cikin koshin lafiya a gidajenmu da kan manyan tituna, kuma masu aikata laifuka ba su da sararin shakar numfashi,” in ji Ministan.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

NAWIA
Labarai

Ranar Abinci Ta Duniya: NAWIA Ta Tallafawa Mata 114  Da Kayan Aikin Gona A Zamfara

October 16, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Shugaban Ƙasa Zai Sake Nazari Kan Mutanen Da Aka Yi Wa Afuwa

October 16, 2025
Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara
Labarai

Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

October 16, 2025
Next Post
Manzon Allah

Allah Ya Yi Rantsuwa Da Girman Darajar Manzon Allah S.A.W (1)

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika

Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika

October 16, 2025
NAWIA

Ranar Abinci Ta Duniya: NAWIA Ta Tallafawa Mata 114  Da Kayan Aikin Gona A Zamfara

October 16, 2025
Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa

Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa

October 16, 2025
Gaza

Wane Ci Gaba Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza Ta Haifar?

October 16, 2025
Tsohon Ɗan Wasan Dambe, Ricky Hatton Ya Rataye Kansa

Tsohon Ɗan Wasan Dambe, Ricky Hatton Ya Rataye Kansa

October 16, 2025
Alkaluman Jin Ra’ayi na CGTN Sun Shaida Amincewar Al’umma Da Karfin Tattalin Arzikin Kasar Sin

Alkaluman Jin Ra’ayi na CGTN Sun Shaida Amincewar Al’umma Da Karfin Tattalin Arzikin Kasar Sin

October 16, 2025
Masu Bincike Na Sin Sun Kera Wani Dan Karamin Mutum Mutumin Hannu Da Zai Taimaka Wajen Gwaje-wajen Kimiyya

Masu Bincike Na Sin Sun Kera Wani Dan Karamin Mutum Mutumin Hannu Da Zai Taimaka Wajen Gwaje-wajen Kimiyya

October 16, 2025
Tinubu

Shugaban Ƙasa Zai Sake Nazari Kan Mutanen Da Aka Yi Wa Afuwa

October 16, 2025
Xi Jinping Ya Yi Kira Da a Kara Horar Da Kwararrun Masana A Fannin Aikin Gona

Xi Jinping Ya Yi Kira Da a Kara Horar Da Kwararrun Masana A Fannin Aikin Gona

October 16, 2025
Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

October 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.