• English
  • Business News
Saturday, September 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

by Abubakar Abba and Sulaiman
3 weeks ago
in Noma Da Kiwo
0
Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar Masu Shuke-shuken Kayan Lambu ta Kasa (POFON) ta bayyana cewa, tana bukatar karin hekta 500,000, domin noman kwakwar manja.

Har ila yau, ta sanar da cewa; tana da wannan bukata ce, domin kara bunkasa noman kwakwar manjan tare da samar da wadatuwarta, duba da karin bukatar da ake da ita a fadin kasar baki-daya.

  • NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai
  • Ana Ci Gaba Da Caccakar El-rufai Kan Kalamansa Game Da Tsaron Kasa

Shugaban kungiyar na kasa, Mista Emmanuel Ibru, ya bayyana hakan ne a hirar da aka yi da shi, kan batun yadda kungiyar za ta samar da wadatacciyar kwakwar manjan a Nijeriya da kuma batun daidata farashinta a daukacin fadin kasar.

Shugaban ya bayyana cewa, kungiyar za kuma ta daidai ta farashin kwakwar, har zuwa karshen shekarara; hatta a cikin kowace kakar noma a kasar.

“A daukacin Nahiyar Afirka, Nijeriya ce kan gaba wajen noman kwakwar manja, sannan kuma ita ce ta biyar a noman kwakwar manjan a dukkanin fadin duniya,” in ji Ibru.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi

Dalilin Gwamnatin Tarayya Da Hukumar FAO Na Zuba Dala Biliyan 3.14 A Fannin Noma

Ya kara da cewa, saboda haka; akwai bukatar a kara yawan hektar noman kwakwar manjar zuwa hekta akalla 500,000, domin cike gibin bukatar da ake da ita a kasar nan tare kuma da kara bunkasa nomanta a Nijeriya baki-daya.

Shugaban ya ci gaba da cewa, har yanzu a Nijeriya ana ci gaba da fuskantar samun gibi wajen samar da kwakwar, sai dai ya bayyana cewa; sama da shekara 10 zuwa shekara 15 kungiyar ta POFON ta yi namijin kokari, wajen kara yawan noman kwakwar a daukacin fadin kasar.

A cewarsa, manyan gonaki a kasar da ke nomanta kamar irin su, Presco da kuma Okomu sun kara dage damtse wajen zuba hannun jari da kuma kara fadada gonakin noman kwakwar manjan kwarai da gaske.

Haka zalika, shugaban ya bayyana cewa; wasu sabbin gonaki kamar irin su Dufil, Saro Africa da sauransu, sun shiga Jihar Edo tare da zuba hannun jari a fannin na noman kwakwar.

“Saro Africa, ta samar da hekta 20,000 a Jihar Edo, Wilmar ta mallaki hektar noman kwakwar ta PZ Wilmar, inda yanzu yake kokarin sake noma wasu hektocin guda 8,500, wanda hakan zai bai wa gonar damar hekta guda 50,000 a cikin kasar.

“Gonakin JB, su ma sun kara zuba hannun jarinsu a Jihar Kuros Ribas, inda a yanzu suke kan kara samar da wasu hekta guda 10,000, ta noman kwakwar manjan a Jihar Ondo,” a cewar shugaban.

Ya ci gaba da cewa, akwai kuma wata gonar ta noman kwakwar manjan da ke ci gaba da kara zuba hannun jarinsu.

“Kimanin shekaru takwas da suka gabata, jimillar gundarin manjan da ake samarwa a kasar, a wannan yankin ake samar da shi wanda ya kai daga tan 900,000 zuwa tan miliyan daya,“ in ji shugaban.

“Ya zuwa yanzu, mun samu nasarar kara yawansa zuwa kimanin daga miliyan 1.4 zuwa miliyan 1.5, wanda hakan ya nuna cewa; ya kai kashi 50 na manjan da aka sarrafa,” in ji Ibru.

Koda-yake dai, shugaban ya sanar da cewa; ana ci gaba da samun gibi a samar da kwakwar manjan a kasar, amma kungiyar na kan yin aiki da wasu hukumomin gwamnati, domin samar da wani jadawalin kara bunkasa fannin a kasar nan da kuma kara zuba kudi a bangaren.

Ya yi nuni da cewa, jadawalin, ba wai kawai manyan masu noman kwakwar manjan ba ne, hatta su ma kananan monoma a fannin, za su yi matukar amfana.

Da yake yin tsokaci kan tsadar manjan a fadin wannan kasa, Ibru ya bayyana cewa; kungiyar na ci gaba da yin kokari wajen daidaita farashinsa kwarai da gaske.

“A wannan kasa da muke ciki, sau biyu ake yin noman kwakwar manja a shekara, yadda idan aka girbe ta da yawa, farashin nata ke raguwa daga baya kuma farashin ya kara tashi,“ a cewar shugaban.

Haka zalika, ya sanar da cewa; ‘ya’yan kungiyarmu na matukar kokari wajen ganin sun daidata farashin manjan a fadin kasar baki-daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa

Next Post

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi

3 hours ago
Dalilin Gwamnatin Tarayya Da Hukumar FAO Na Zuba Dala Biliyan 3.14 A Fannin Noma
Noma Da Kiwo

Dalilin Gwamnatin Tarayya Da Hukumar FAO Na Zuba Dala Biliyan 3.14 A Fannin Noma

4 hours ago
Gwamnatin Kogi Ta Yi Haɗin Gwuiwa Don Fara Fitar Da Amfanin Gona
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Kogi Ta Yi Haɗin Gwuiwa Don Fara Fitar Da Amfanin Gona

20 hours ago
Nijeriya Na Asarar Dala Biliyan 10.5 Sakamakon Rashin Cin Gajiyar Kashin Dabbobi
Noma Da Kiwo

Nijeriya Na Asarar Dala Biliyan 10.5 Sakamakon Rashin Cin Gajiyar Kashin Dabbobi

7 days ago
Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

3 weeks ago
Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

1 month ago
Next Post
Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Wakilai Za Ta Sasanta Dangote Da NUPENG

Majalisar Wakilai Za Ta Sasanta Dangote Da NUPENG

September 27, 2025
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance

NDLEA Ta Farmaki Masu Safarar Muggan Kwayoyi A Sassan Nijeriya

September 27, 2025
Majalisar Shura ta Kano Za Ta Binciki Zargin Batanci Ga Annabi Kan Malam Triumph

Majalisar Shura ta Kano Za Ta Binciki Zargin Batanci Ga Annabi Kan Malam Triumph

September 27, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Mutum Hudu Kan Satar Taransifoma A Makaranatar Kebbi

‘Yansanda Sun Cafke Mutum Hudu Kan Satar Taransifoma A Makaranatar Kebbi

September 27, 2025
Tinubu Zai Gana Da Manyan Ƴan Kasuwa, Zai Ƙaddamar Da Muhimman Aiyuka A Legas

Tinubu Zai Gana Da Manyan Ƴan Kasuwa, Zai Ƙaddamar Da Muhimman Aiyuka A Legas

September 27, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi

September 27, 2025
Sabon Farashin Jigilar Mahajjata A 2026, Ƴan Arewa N8.2m, Ƴan Kudu N8.5m

Sabon Farashin Jigilar Mahajjata A 2026, Ƴan Arewa N8.2m, Ƴan Kudu N8.5m

September 27, 2025
Dalilin Gwamnatin Tarayya Da Hukumar FAO Na Zuba Dala Biliyan 3.14 A Fannin Noma

Dalilin Gwamnatin Tarayya Da Hukumar FAO Na Zuba Dala Biliyan 3.14 A Fannin Noma

September 27, 2025
Yadda Na Kawo Karshen Yajin Aikin ASUU Cikin Kwana Daya – Jonathan

Lalacewar Tsarin Zabe Babbar Barazana Ce Ga Dorewar Dimokuradiyyar Afirka — Jonathan

September 27, 2025
Ana Fatan Majalisar Wakilan Amurka Za Ta Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Raya Hadin Gwiwar Sin Da Amurka

Ana Fatan Majalisar Wakilan Amurka Za Ta Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Raya Hadin Gwiwar Sin Da Amurka

September 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.