• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Muna Fama Da Taɓarɓarewar Tattalin Arziƙi Da Wutar Lantarki – Gwamnonin Arewa Da Sarakuna

by Sulaiman
11 months ago
in Manyan Labarai
0
Muna Fama Da Taɓarɓarewar Tattalin Arziƙi Da Wutar Lantarki – Gwamnonin Arewa Da Sarakuna
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Arewa ce ta fi fama da matsalar taɓarɓarewar tattalin arziki a Nijeriya, kamar yadda gwamnoni da sarakunan yankin suka bayyana a ranar Litinin 28 ga watan Oktoba.

 

Sun bayyana haka ne a yayin taron gaggawa na gwamnonin jihohin Arewa (NSGF) da sarakunan gargajiya da aka yi a Gidan Gwamnatin Kaduna (Sir. Kashim Ibrahim House) don magance matsalolin da yankin ke fuskanta.

  • Bangarorin Masana’antu Da Kasuwancin Kasar Sin Sun Bayyana Adawa Da Matakan Kariyar Ciniki Da Kasar Amurka Ta Dauka
  • APC Ce Za Ta Lashe Zaɓen Gwamnan Ondo – Ganduje

Taron ya samu halartar Gwamnonin Arewa daban-daban da sarakunan gargajiya karkashin jagorancin Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar III da babban hafsan hafsoshin tsaro, Janar Christopher Musa.

 

Labarai Masu Nasaba

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Da yake jawabi a yayin taron, shugaban kungiyar kuma Gwamnan Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya ce a matsayinsu na shugabannin Arewa, dole ne Gwamnonin su dauki matakan rage radadin talauci da mafi yawancin mazauna yankin ke fama da shi ta hanyar wanzar da shirye-shiryen walwalar jama’a, tallafawa kanana da matsakaitan masana’antu da kuma nemo masu saka hannun jari zuwa yankin.

 

ArewaYa yi kira da a samar da cikakken garambawul a dukkanin cibiyoyi, yana mai cewa, a halin yanzu suna ci gaba da yin kwaskwarima a manufofi da tsare-tsaren NSGF domin karfafa ayyukan kungiyar, wanda zai ba ta damar magance kalubalen da ake fuskanta yadda ya kamata.

 

Kungiyar ta yi kira ga Gwamnatin Tarayya da Hukumomin da abin ya shafa da su gaggauta magance matsalar wutar lantarki da ke addabar yawancin Jihohin Arewa sakamakon lalata turakun layin wutar lantarki da bata-gari suka yi.

 

Kungiyar ta amince cewa, Arewacin Nijeriya yana da dimbin albarkatun noma, wanda idan aka yi amfani da shi yadda yakamata, zai rage yunwa da bunkasar tattalin arziki. Don cimma wannan buri, kungiyar ta kuduri aniyar bayar da tallafin da ya dace ga manoma, da suka hada da samar da kudade, dabarun noman zamani da ababen more rayuwa kamar tituna da samar da ruwa don noman rani. Ba wai kawai a kalli noma a matsayin hanyar ciyar da al’ummarmu ba, har ma a matsayin hanyar samar da masana’antu da samar da ayyukan yi a fadin yankin. Za a iya cimma hakan ta hanyar sake farfado da masana’antun tufafi a Arewa

 

Sarkin Musulmi kuma Shugaban Majalisar Sarakunan Gargajiya ta Arewa, Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar III ya ce, yankin bai rasa wani rahoto ko mafita ba kan kalubalen da yake fuskanta, sai dai rashin aiwatar da shawarwarin da aka bayar kan magance kalubalen da aka gano.

Arewa

Sarkin Musulmi ya umarci shugabannin yankin da su marawa shirin gwamnatin tarayya baya na magance matsalar Almajirci da yaran da ba sa zuwa makaranta.

 

Babban hafsan hafsoshin tsaron Nijeriya, Janar Christopher Musa, wanda ya yi jawabi a wurin taron NSGF, ya ce dakarun sojin suna aiki tukuru domin magance matsalar rashin tsaro da ke addabar yankin Arewa da ma sauran sassan kasar nan.

 

Musa ya yabawa gwamnonin Arewa da sarakunan gargajiya bisa goyon baya da hadin kai da suke bayarwa don magance matsalolin tsaro da suka addabi yankin Arewa.

 

A karshe, kungiyar NSGF ta yabawa mai girma shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu da babban kwamandan rundunar sojojin tarayyar Nijeriya, Janar Christopher Musa bisa shirin kawo sauyi a bangaren kiwon dabbobi tare da amincewa da bayar da duk wani abu da ake bukata wajen tabbatar da nasarar gwamnatin tarayya wajen shirin bunkasa kiwon.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kalubalen wutar lantarki a arewaKungiyar Gwamnonin arewaYan bindiga a Arewa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Sanya Kamfanoninta Cikin Jerin Wadanda Ba Za A Sayarwa Kayayyaki Ba

Next Post

Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Gyara Wutar Lantarkin Arewa Cikin Gaggawa

Related

Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Manyan Labarai

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

5 hours ago
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram
Manyan Labarai

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

17 hours ago
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

19 hours ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Tinubu Zai Ziyarci Jos Domin Halartar Jana’izar Mahaifiyar Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa

2 days ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

PENGASSAN Ta Yi Watsi Da Tayin Dangote Na Biyan Ma’aikata Albashin Shekaru 5 Ba Tare Da Yin Aiki Ba

2 days ago
NAFDAC Ta Rufe Manyan Shaguna 2 Na Ƴan China A Abuja
Manyan Labarai

NAFDAC Ta Rufe Manyan Shaguna 2 Na Ƴan China A Abuja

2 days ago
Next Post
Tinubu Ya Nemi Jihohi Su Dakatar Da Karbar Haraji A Kan Masu Safarar Kayan Abinci

Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Gyara Wutar Lantarkin Arewa Cikin Gaggawa

LABARAI MASU NASABA

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

October 5, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

October 5, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

October 5, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.