• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Muna Fama Da Taɓarɓarewar Tattalin Arziƙi Da Wutar Lantarki – Gwamnonin Arewa Da Sarakuna

by Sulaiman
7 months ago
in Manyan Labarai
0
Muna Fama Da Taɓarɓarewar Tattalin Arziƙi Da Wutar Lantarki – Gwamnonin Arewa Da Sarakuna
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Arewa ce ta fi fama da matsalar taɓarɓarewar tattalin arziki a Nijeriya, kamar yadda gwamnoni da sarakunan yankin suka bayyana a ranar Litinin 28 ga watan Oktoba.

 

Sun bayyana haka ne a yayin taron gaggawa na gwamnonin jihohin Arewa (NSGF) da sarakunan gargajiya da aka yi a Gidan Gwamnatin Kaduna (Sir. Kashim Ibrahim House) don magance matsalolin da yankin ke fuskanta.

  • Bangarorin Masana’antu Da Kasuwancin Kasar Sin Sun Bayyana Adawa Da Matakan Kariyar Ciniki Da Kasar Amurka Ta Dauka
  • APC Ce Za Ta Lashe Zaɓen Gwamnan Ondo – Ganduje

Taron ya samu halartar Gwamnonin Arewa daban-daban da sarakunan gargajiya karkashin jagorancin Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar III da babban hafsan hafsoshin tsaro, Janar Christopher Musa.

 

Labarai Masu Nasaba

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

Da yake jawabi a yayin taron, shugaban kungiyar kuma Gwamnan Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya ce a matsayinsu na shugabannin Arewa, dole ne Gwamnonin su dauki matakan rage radadin talauci da mafi yawancin mazauna yankin ke fama da shi ta hanyar wanzar da shirye-shiryen walwalar jama’a, tallafawa kanana da matsakaitan masana’antu da kuma nemo masu saka hannun jari zuwa yankin.

 

ArewaYa yi kira da a samar da cikakken garambawul a dukkanin cibiyoyi, yana mai cewa, a halin yanzu suna ci gaba da yin kwaskwarima a manufofi da tsare-tsaren NSGF domin karfafa ayyukan kungiyar, wanda zai ba ta damar magance kalubalen da ake fuskanta yadda ya kamata.

 

Kungiyar ta yi kira ga Gwamnatin Tarayya da Hukumomin da abin ya shafa da su gaggauta magance matsalar wutar lantarki da ke addabar yawancin Jihohin Arewa sakamakon lalata turakun layin wutar lantarki da bata-gari suka yi.

 

Kungiyar ta amince cewa, Arewacin Nijeriya yana da dimbin albarkatun noma, wanda idan aka yi amfani da shi yadda yakamata, zai rage yunwa da bunkasar tattalin arziki. Don cimma wannan buri, kungiyar ta kuduri aniyar bayar da tallafin da ya dace ga manoma, da suka hada da samar da kudade, dabarun noman zamani da ababen more rayuwa kamar tituna da samar da ruwa don noman rani. Ba wai kawai a kalli noma a matsayin hanyar ciyar da al’ummarmu ba, har ma a matsayin hanyar samar da masana’antu da samar da ayyukan yi a fadin yankin. Za a iya cimma hakan ta hanyar sake farfado da masana’antun tufafi a Arewa

 

Sarkin Musulmi kuma Shugaban Majalisar Sarakunan Gargajiya ta Arewa, Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar III ya ce, yankin bai rasa wani rahoto ko mafita ba kan kalubalen da yake fuskanta, sai dai rashin aiwatar da shawarwarin da aka bayar kan magance kalubalen da aka gano.

Arewa

Sarkin Musulmi ya umarci shugabannin yankin da su marawa shirin gwamnatin tarayya baya na magance matsalar Almajirci da yaran da ba sa zuwa makaranta.

 

Babban hafsan hafsoshin tsaron Nijeriya, Janar Christopher Musa, wanda ya yi jawabi a wurin taron NSGF, ya ce dakarun sojin suna aiki tukuru domin magance matsalar rashin tsaro da ke addabar yankin Arewa da ma sauran sassan kasar nan.

 

Musa ya yabawa gwamnonin Arewa da sarakunan gargajiya bisa goyon baya da hadin kai da suke bayarwa don magance matsalolin tsaro da suka addabi yankin Arewa.

 

A karshe, kungiyar NSGF ta yabawa mai girma shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu da babban kwamandan rundunar sojojin tarayyar Nijeriya, Janar Christopher Musa bisa shirin kawo sauyi a bangaren kiwon dabbobi tare da amincewa da bayar da duk wani abu da ake bukata wajen tabbatar da nasarar gwamnatin tarayya wajen shirin bunkasa kiwon.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kalubalen wutar lantarki a arewaKungiyar Gwamnonin arewaYan bindiga a Arewa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Sanya Kamfanoninta Cikin Jerin Wadanda Ba Za A Sayarwa Kayayyaki Ba

Next Post

Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Gyara Wutar Lantarkin Arewa Cikin Gaggawa

Related

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte
Manyan Labarai

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

3 hours ago
Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?
Manyan Labarai

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

4 hours ago
Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar
Manyan Labarai

Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

18 hours ago
Wata Mata Ta Kashe Dan Hayar Da Ke Gidanta A Ondo
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban APC A Ondo, Sun Nemi N100m

21 hours ago
Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027
Siyasa

Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027

1 day ago
Nijeriya Ta Biya Dukkanin Bashin IMF Na COVID-19
Manyan Labarai

Nijeriya Ta Biya Dukkanin Bashin IMF Na COVID-19

1 day ago
Next Post
Tinubu Ya Nemi Jihohi Su Dakatar Da Karbar Haraji A Kan Masu Safarar Kayan Abinci

Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Gyara Wutar Lantarkin Arewa Cikin Gaggawa

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

May 14, 2025
Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

May 14, 2025
Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

May 14, 2025
Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

May 14, 2025
Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

May 13, 2025
Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

May 13, 2025
Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

May 13, 2025
Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

May 13, 2025
Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

May 13, 2025
Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

May 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.