• English
  • Business News
Sunday, August 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Muna Fama Da Taɓarɓarewar Tattalin Arziƙi Da Wutar Lantarki – Gwamnonin Arewa Da Sarakuna

by Sulaiman
10 months ago
in Manyan Labarai
0
Muna Fama Da Taɓarɓarewar Tattalin Arziƙi Da Wutar Lantarki – Gwamnonin Arewa Da Sarakuna
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Arewa ce ta fi fama da matsalar taɓarɓarewar tattalin arziki a Nijeriya, kamar yadda gwamnoni da sarakunan yankin suka bayyana a ranar Litinin 28 ga watan Oktoba.

 

Sun bayyana haka ne a yayin taron gaggawa na gwamnonin jihohin Arewa (NSGF) da sarakunan gargajiya da aka yi a Gidan Gwamnatin Kaduna (Sir. Kashim Ibrahim House) don magance matsalolin da yankin ke fuskanta.

  • Bangarorin Masana’antu Da Kasuwancin Kasar Sin Sun Bayyana Adawa Da Matakan Kariyar Ciniki Da Kasar Amurka Ta Dauka
  • APC Ce Za Ta Lashe Zaɓen Gwamnan Ondo – Ganduje

Taron ya samu halartar Gwamnonin Arewa daban-daban da sarakunan gargajiya karkashin jagorancin Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar III da babban hafsan hafsoshin tsaro, Janar Christopher Musa.

 

Labarai Masu Nasaba

Ƴansanda Sun Kama Makashin Wani Ɗan Jarida A Abuja Bayan Shekara Ɗaya

Yadda Wasu Jihohi Suka Yi Watsi Da Gine-ginensu Da Ke Legas

Da yake jawabi a yayin taron, shugaban kungiyar kuma Gwamnan Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya ce a matsayinsu na shugabannin Arewa, dole ne Gwamnonin su dauki matakan rage radadin talauci da mafi yawancin mazauna yankin ke fama da shi ta hanyar wanzar da shirye-shiryen walwalar jama’a, tallafawa kanana da matsakaitan masana’antu da kuma nemo masu saka hannun jari zuwa yankin.

 

ArewaYa yi kira da a samar da cikakken garambawul a dukkanin cibiyoyi, yana mai cewa, a halin yanzu suna ci gaba da yin kwaskwarima a manufofi da tsare-tsaren NSGF domin karfafa ayyukan kungiyar, wanda zai ba ta damar magance kalubalen da ake fuskanta yadda ya kamata.

 

Kungiyar ta yi kira ga Gwamnatin Tarayya da Hukumomin da abin ya shafa da su gaggauta magance matsalar wutar lantarki da ke addabar yawancin Jihohin Arewa sakamakon lalata turakun layin wutar lantarki da bata-gari suka yi.

 

Kungiyar ta amince cewa, Arewacin Nijeriya yana da dimbin albarkatun noma, wanda idan aka yi amfani da shi yadda yakamata, zai rage yunwa da bunkasar tattalin arziki. Don cimma wannan buri, kungiyar ta kuduri aniyar bayar da tallafin da ya dace ga manoma, da suka hada da samar da kudade, dabarun noman zamani da ababen more rayuwa kamar tituna da samar da ruwa don noman rani. Ba wai kawai a kalli noma a matsayin hanyar ciyar da al’ummarmu ba, har ma a matsayin hanyar samar da masana’antu da samar da ayyukan yi a fadin yankin. Za a iya cimma hakan ta hanyar sake farfado da masana’antun tufafi a Arewa

 

Sarkin Musulmi kuma Shugaban Majalisar Sarakunan Gargajiya ta Arewa, Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar III ya ce, yankin bai rasa wani rahoto ko mafita ba kan kalubalen da yake fuskanta, sai dai rashin aiwatar da shawarwarin da aka bayar kan magance kalubalen da aka gano.

Arewa

Sarkin Musulmi ya umarci shugabannin yankin da su marawa shirin gwamnatin tarayya baya na magance matsalar Almajirci da yaran da ba sa zuwa makaranta.

 

Babban hafsan hafsoshin tsaron Nijeriya, Janar Christopher Musa, wanda ya yi jawabi a wurin taron NSGF, ya ce dakarun sojin suna aiki tukuru domin magance matsalar rashin tsaro da ke addabar yankin Arewa da ma sauran sassan kasar nan.

 

Musa ya yabawa gwamnonin Arewa da sarakunan gargajiya bisa goyon baya da hadin kai da suke bayarwa don magance matsalolin tsaro da suka addabi yankin Arewa.

 

A karshe, kungiyar NSGF ta yabawa mai girma shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu da babban kwamandan rundunar sojojin tarayyar Nijeriya, Janar Christopher Musa bisa shirin kawo sauyi a bangaren kiwon dabbobi tare da amincewa da bayar da duk wani abu da ake bukata wajen tabbatar da nasarar gwamnatin tarayya wajen shirin bunkasa kiwon.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kalubalen wutar lantarki a arewaKungiyar Gwamnonin arewaYan bindiga a Arewa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Sanya Kamfanoninta Cikin Jerin Wadanda Ba Za A Sayarwa Kayayyaki Ba

Next Post

Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Gyara Wutar Lantarkin Arewa Cikin Gaggawa

Related

Ƴansanda Sun Kama Makashin Wani Ɗan Jarida A Abuja Bayan Shekara Ɗaya
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kama Makashin Wani Ɗan Jarida A Abuja Bayan Shekara Ɗaya

2 hours ago
Yadda Wasu Jihohi Suka Yi Watsi Da Gine-ginensu Da Ke Legas
Manyan Labarai

Yadda Wasu Jihohi Suka Yi Watsi Da Gine-ginensu Da Ke Legas

7 hours ago
Gwamna Abba Ya Bai Wa Dalibai 1,130 Kayan Aikin Sana’o’in Hannu
Manyan Labarai

Gwamna Abba Ya Bai Wa Dalibai 1,130 Kayan Aikin Sana’o’in Hannu

9 hours ago
ADC Ta Yi Allah-wadai Da Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM A Neja
Manyan Labarai

An Maka Gwamnatin Neja Da NBC A Kotu Kan Barazanar Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM

12 hours ago
NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja
Manyan Labarai

NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja

15 hours ago
An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja
Manyan Labarai

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

1 day ago
Next Post
Tinubu Ya Nemi Jihohi Su Dakatar Da Karbar Haraji A Kan Masu Safarar Kayan Abinci

Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Gyara Wutar Lantarkin Arewa Cikin Gaggawa

LABARAI MASU NASABA

Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu

Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu

August 10, 2025
Ƴansanda Sun Kama Makashin Wani Ɗan Jarida A Abuja Bayan Shekara Ɗaya

Ƴansanda Sun Kama Makashin Wani Ɗan Jarida A Abuja Bayan Shekara Ɗaya

August 10, 2025
Fa’ida Da Muhimmancin Tattalin Lokaci Ga Ɗan’adam

Fa’ida Da Muhimmancin Tattalin Lokaci Ga Ɗan’adam

August 10, 2025
INEC Ta Gargaɗi Ƴan Siyasa Kan Azarɓaɓin Yaƙin Neman Zaɓen 2027

INEC Ta Gargaɗi Ƴan Siyasa Kan Azarɓaɓin Yaƙin Neman Zaɓen 2027

August 10, 2025
Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya

Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya

August 10, 2025
Harin Ƴan Bindiga Ya Yi Sanadin Kashe Ɗansanda Da Wasu Mutane 4 A Kwara

Harin Ƴan Bindiga Ya Yi Sanadin Kashe Ɗansanda Da Wasu Mutane 4 A Kwara

August 10, 2025
Yadda Wasu Jihohi Suka Yi Watsi Da Gine-ginensu Da Ke Legas

Yadda Wasu Jihohi Suka Yi Watsi Da Gine-ginensu Da Ke Legas

August 10, 2025
Yadda Jinkirin Tabbatar Da ‘Yancin Cin Gashin Kai Ke Cutar Da Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi

Yadda Jinkirin Tabbatar Da ‘Yancin Cin Gashin Kai Ke Cutar Da Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi

August 10, 2025
Gwamna Abba Ya Bai Wa Dalibai 1,130 Kayan Aikin Sana’o’in Hannu

Gwamna Abba Ya Bai Wa Dalibai 1,130 Kayan Aikin Sana’o’in Hannu

August 10, 2025
NDLEA Ta Kama Fasto Bisa Laifin Safarar Miyagun Kwayoyi A Legas 

NDLEA Ta Kama Fasto Bisa Laifin Safarar Miyagun Kwayoyi A Legas 

August 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.