• English
  • Business News
Saturday, October 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Muna Samun Nasarori A Yaki Da Gurbatattun Masana’antar Kannywood – Tijjani Asase

by Rabilu Sanusi Bena
1 year ago
Nasarori

Shugaban kwamitin tsaftace ayyukan ‘yan masana’antar kannywood wanda hukumar tace fina-finai da dab’i ta Jahar Kano ta kafa domin tabbatar da ana bin dokokinta sau da kafa Tijjani Asase ya bayyana cewa kwamitinsu ya samu nasarori da dama tun bayan kafa shi da aka yi.

Asase ya jaddada cewar daga cikin nasarorin da wannan kwamiti da yake jagoranta ya samu akwai rufe guraren da ake shirya fina-finai ba bisa ka’ida ba har guda 3 tare da kama Daraktoci 2 da sauran ma’aikata da jaruman masana’antar ta kannywood har 32 wanda a cewarsa hakan wata babbar nasara ce ga masana’antar ta kannywood.

  • Kamfani Ya Maka Bankin Globus A Kotu A Kan Karya Yarjejeniyar Bashi
  • Lallai A Hukunta Waɗanda Suka Kai Mamaya Ofishin NLC – TUC

Malam Tijjani Asase ya bayyana hakan ne ga Shugaban Hukumar tace fina-finai da Dab’i ta Jahar Kano Alh Abba El-mustapha yayin da kwamitin yake bayyana wani bangare na rahoton wasu daga cikin nasarorin aiyukan da suka samu tun bayan nada su a matsayin shuwagabanni.

Da yake nasa jawabin Alh Abba El-mustapha ya jinjinawa shugaban kwamitin tare da membobinsa duba da yadda suka jajirce wajen sauke nauyin da hukumar ta dora musu duba da cancantarsu tare da kishin da suke da shi na ganin hukumar da masana’antar ta kannywood sun sami ci gaba mai dorewa.

Alhaji Abba El-mustapha ya jaddada cewa ba’a kafa kwamitin dan a ciwa kowa mutunci ba face tsaftacewa tareda fito da kima da daraja ta masana’antar kannywood a idon Duniya inda ya kara da cewa manufar kafa kwamitin ita ce tabbatar da ana bin doka da ka’ida a masana’antar kannywood sau da kafa tare da bin duk wata hanya da ake ganin masana’antar za ta samu cigaba da kuma cire gurbatattu da cikinsu wadanda suke janyo wa masana’antar zagi ta yadda zata yi gogayya da sauran takwarorinta na Nijeriya dama duniya baki daya.

LABARAI MASU NASABA

Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad 

Me Ya Sa Jaruman Masana’antar Kannywood Ke Auren Sirri?

Abba El-mustapha ya tabbatar da cewa tuni lokaci ya kure da wasu zasu ringa amfani da sunan masana’antar ta kannywood suna abinda bai kamata ba domin cimma kudurorin kashin kansu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad 
Nishadi

Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad 

October 11, 2025
Me Ya Sa Jaruman Masana’antar Kannywood Ke Auren Sirri?
Nishadi

Me Ya Sa Jaruman Masana’antar Kannywood Ke Auren Sirri?

October 11, 2025
Kotu Ta Aike Da Ɗan TikTok Gidan Gyaran Hali Kan Bidiyon Batsa A Kano
Nishadi

Kotu Ta Aike Da Ɗan TikTok Gidan Gyaran Hali Kan Bidiyon Batsa A Kano

October 6, 2025
Next Post
Me Ya Fi Damun Matasan Nijeriya A Wannan Zamanin?

Me Ya Fi Damun Matasan Nijeriya A Wannan Zamanin?

LABARAI MASU NASABA

Radda

Gwamnan Katsina Ya Bukaci Al’umma Su Hada Hannu Da Gwamnati Wajen Kawar Da Matsalar Tsaro

October 18, 2025
Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi

Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi

October 18, 2025
IMF

Fitar Da Kudi Ta Haramtacciyar Hanya Na Kara Dagula Matsalar Tattalin Arziki – IMF

October 18, 2025
majalisar kasa

Majalisar Wakilai Ta Gayyaci CBN Da Bankuna Kan Cire Wa Kwastomomi Kudi Ba Dalili

October 18, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Matashi Ya Kashe Ɗan Acaɓa Don Neman Kuɗin Auren Mace Ta Uku A Bauchi

October 17, 2025
katsina

Tawagar Bankin Duniya Ta Gana Da Gwamnan Katsina Kan Mayar Da ‘Yan Gudun Hijira Muhallinsu

October 17, 2025
Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

October 17, 2025
Akwai Bukatar Al’umma Ta San Aikin Da Asusun Tallafa Wa Manyan Makarantu (TETFUND) Ya Yi  – Masari

Akwai Bukatar Al’umma Ta San Aikin Da Asusun Tallafa Wa Manyan Makarantu (TETFUND) Ya Yi  – Masari

October 17, 2025
Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO

Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO

October 17, 2025
Abduljabbar

Hukumar Gidan Yarin Kano Ta Tabbatar Da Dauke Abduljabbar Zuwa Abuja

October 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.