ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, November 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Musabbabin Haramta Sana’ar Gwangwan A Jihar Borno

by Muhammad Maitela
2 years ago
Borno

A kokarin dakile yawan kai wa masu sana’ar tsoffin karafa farmakin da mayakan Boko Haram ke yi a jihar Borno, Gwamna Farfesa Babagana Zulum, ya kafa dokar haramta sana’ar a fadin jihar, har sai baba ta gani.

Gwamnatin jihar ta kara da cewa, kafa dokar ya zama dole domin kare rayukan masu sana’ar gwangwan, sakamakon hare-haren da `yan ta’addan Boko Haram ke kai musu a baya-bayan nan.

  • Cire Tallafin Mai: Za A Kara Farashin Burodi A Nijeriya
  • Kyakkyawar Alakar Sin Da Amurka Fa’ida ce Ga Duniya Baki Daya

A wata sanarwar manema labaru mai dauke da sa-hannun Mallam Isa Gusau, mai magana da yawun Gwamna Zulum, ya ce, “An kafa wannan dokar ce domin dakile farmakin da yan ta’addan Boko Haram ke kai wa masu wannan sana’ar a wasu kananan hukumomi da kuma hana satar dukiyar jama’a da ake yawan samu.”

ADVERTISEMENT

Gusau ya kara da cewa, hakan ya zo ne sakamakon yadda wasu wadanda ba a san ko su waye ba, suna zuwa kauyukan da yan ta’addan Boko Haram suka tarwatsa, domin neman tsoffin karafa, inda Boko Haram ke yi musu kwanton bauna tare da kashe su.”

A cewar Gwamna Zulum “A cikin shekaru biyar da suka wuce, an kashe mutane da dama a lokacin da suke shiga kauyuka, a sana’ar gwangwan. Hakan ya sanya dole gwamnatin jihar Borno ta dauki matakin bincike kan matsalolin, al’amarin da ya tilasta kafa wannan dokar.” In ji Zulum.

LABARAI MASU NASABA

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje

ADC Ta Tsara Ka’idojin Da Shugabanninta Za Su Bi Don Tunkarar Zaben 2027

“Sannan kuma a wadannan wuraren, akwai dukiyoyin gwamnati, da na kamfanonin sadarwa. Wanda irin wadannan ayyuka na sana’ar gwangwan ke zama kalubale da kuma zagon kasa ga Gwamnatin Tarayya da na jihar Borno wajen kula da su. Saboda haka na bayar da umarnin hana sana’ar gwangwan ta karafa a dukkan kananan hukumomin jihar Borno 27.”

Bugu da kari, Gwamna Zulum ya bayyana cewa, wadannan masu sana’ar gwangwan sun yi kaurin suna wajen lalata dukiyoyin jama’a da na kamfanoni masu zaman kansu a mafi yawan kananan hukumomin da rikicin Boko Haram ya tilasta wa mazaunansu tserewa.

Gwamna Zulum ya kara da cewa gwamnatin jihar ta yi asarar kadarori na biliyoyin Naira a cikin shekaru biyar da suka gabata sakamakon ayyukan masu sana’ar gwangwan a jihar.

Gwamnan ya ce wannan dokar ta shafi duk wani nau’i na sana’ar tsoffin karafa wanda ba bisa ka’ida ba, wanda ya hada da wargazawa, tarawa, da kuma jigilar tsoffin karafan a fadin jihar.

Gwamna Zulum ya yi gargadin cewa gwamnatin jihar Borno za ta hada gwiwa da jami’an tsaro wajen aiwatar da dokar yadda ya kamata tare da zartar da hukunci mai tsauri ga duk wanda ya karya dokar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje
Rahotonni

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje

November 15, 2025
ADC Ta Tsara Ka’idojin Da Shugabanninta Za Su Bi Don Tunkarar Zaben 2027
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Tsara Ka’idojin Da Shugabanninta Za Su Bi Don Tunkarar Zaben 2027

November 14, 2025
Tambarin Dimokuradiyya

Rikicin PDP: Fiye Da Wakilai 3,000 Ne Za Su Raba Gardama A Babban Taron Jam’iyyar

November 14, 2025
Next Post
Daidaita Farashin Canji Ya Fara Haifar Da Da Mai Ido A Nijeriya

Daidaita Farashin Canji Ya Fara Haifar Da Da Mai Ido A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

November 15, 2025
Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

November 15, 2025
Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 

Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 

November 15, 2025
Za A Yi Gwanjon Rigunan Messi Na Gasar Kofin Duniya Ta 2022 Da Kudi Tsagwagwa

Ina Son Kasancewa Cikin Koshin Lafiya Kafin Buga Gasar Kofin Duniya Na Shekarar 2026 – Messi

November 15, 2025
Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci

Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci

November 15, 2025
Duk Niyyar Da Mutum Ya Shigo Da Ita Kannywood Ita Za Ta Bi Shi —HAUWA KUJAMA

Duk Niyyar Da Mutum Ya Shigo Da Ita Kannywood Ita Za Ta Bi Shi —HAUWA KUJAMA

November 15, 2025
Sin Ta Sha Alwashin Bunkasa Goyon Bayan Juna Tsakaninta Da Saliyo

Sin Ta Sha Alwashin Bunkasa Goyon Bayan Juna Tsakaninta Da Saliyo

November 15, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

November 15, 2025
An Gabatar Da Sabuwar Hanyar Raya Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakanin Sin Da Afirka

An Gabatar Da Sabuwar Hanyar Raya Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakanin Sin Da Afirka

November 15, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Yi Taka-tsantsan Da Batun Yankin Taiwan 

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Yi Taka-tsantsan Da Batun Yankin Taiwan 

November 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.