• English
  • Business News
Saturday, October 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Musabbabin Haramta Sana’ar Gwangwan A Jihar Borno

by Muhammad Maitela
2 years ago
Borno

A kokarin dakile yawan kai wa masu sana’ar tsoffin karafa farmakin da mayakan Boko Haram ke yi a jihar Borno, Gwamna Farfesa Babagana Zulum, ya kafa dokar haramta sana’ar a fadin jihar, har sai baba ta gani.

Gwamnatin jihar ta kara da cewa, kafa dokar ya zama dole domin kare rayukan masu sana’ar gwangwan, sakamakon hare-haren da `yan ta’addan Boko Haram ke kai musu a baya-bayan nan.

  • Cire Tallafin Mai: Za A Kara Farashin Burodi A Nijeriya
  • Kyakkyawar Alakar Sin Da Amurka Fa’ida ce Ga Duniya Baki Daya

A wata sanarwar manema labaru mai dauke da sa-hannun Mallam Isa Gusau, mai magana da yawun Gwamna Zulum, ya ce, “An kafa wannan dokar ce domin dakile farmakin da yan ta’addan Boko Haram ke kai wa masu wannan sana’ar a wasu kananan hukumomi da kuma hana satar dukiyar jama’a da ake yawan samu.”

Gusau ya kara da cewa, hakan ya zo ne sakamakon yadda wasu wadanda ba a san ko su waye ba, suna zuwa kauyukan da yan ta’addan Boko Haram suka tarwatsa, domin neman tsoffin karafa, inda Boko Haram ke yi musu kwanton bauna tare da kashe su.”

A cewar Gwamna Zulum “A cikin shekaru biyar da suka wuce, an kashe mutane da dama a lokacin da suke shiga kauyuka, a sana’ar gwangwan. Hakan ya sanya dole gwamnatin jihar Borno ta dauki matakin bincike kan matsalolin, al’amarin da ya tilasta kafa wannan dokar.” In ji Zulum.

LABARAI MASU NASABA

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

“Sannan kuma a wadannan wuraren, akwai dukiyoyin gwamnati, da na kamfanonin sadarwa. Wanda irin wadannan ayyuka na sana’ar gwangwan ke zama kalubale da kuma zagon kasa ga Gwamnatin Tarayya da na jihar Borno wajen kula da su. Saboda haka na bayar da umarnin hana sana’ar gwangwan ta karafa a dukkan kananan hukumomin jihar Borno 27.”

Bugu da kari, Gwamna Zulum ya bayyana cewa, wadannan masu sana’ar gwangwan sun yi kaurin suna wajen lalata dukiyoyin jama’a da na kamfanoni masu zaman kansu a mafi yawan kananan hukumomin da rikicin Boko Haram ya tilasta wa mazaunansu tserewa.

Gwamna Zulum ya kara da cewa gwamnatin jihar ta yi asarar kadarori na biliyoyin Naira a cikin shekaru biyar da suka gabata sakamakon ayyukan masu sana’ar gwangwan a jihar.

Gwamnan ya ce wannan dokar ta shafi duk wani nau’i na sana’ar tsoffin karafa wanda ba bisa ka’ida ba, wanda ya hada da wargazawa, tarawa, da kuma jigilar tsoffin karafan a fadin jihar.

Gwamna Zulum ya yi gargadin cewa gwamnatin jihar Borno za ta hada gwiwa da jami’an tsaro wajen aiwatar da dokar yadda ya kamata tare da zartar da hukunci mai tsauri ga duk wanda ya karya dokar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Mun Dakile Hari A Kano Da Ka Iya Zama Mafi Muni A Tarihin Nijeriya —Irabor
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

October 17, 2025
Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta
Tambarin Dimokuradiyya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

October 17, 2025
Next Post
Daidaita Farashin Canji Ya Fara Haifar Da Da Mai Ido A Nijeriya

Daidaita Farashin Canji Ya Fara Haifar Da Da Mai Ido A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

October 24, 2025
Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

October 24, 2025
Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

October 24, 2025
An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 24, 2025

Gwamnatin Katsina Ta Ƙara Samar Da Dakarun Tsaro 200 Domin Maganace Ta’addanci

October 24, 2025
Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa

Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa

October 24, 2025
Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

October 24, 2025
An Shirya Harba Kumbon Shenzhou-21 A Kwanan Nan

An Shirya Harba Kumbon Shenzhou-21 A Kwanan Nan

October 24, 2025
Shugaba Xi Ya Jagoranci Zaman Jin Ra’ayoyin Wadanda Ba ‘Yan JKS Ba Game Da Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15 

Shugaba Xi Ya Jagoranci Zaman Jin Ra’ayoyin Wadanda Ba ‘Yan JKS Ba Game Da Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15 

October 24, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Wa Sarakuna Ba Zai Rage Musu Iko Ba A Shirinsa Na Ƙirƙirar Sabbin Masarautu

Gwamnan Bauchi Ya Naɗa Yayansa A Matsayin Sabon Sarkin Duguri

October 24, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.