• English
  • Business News
Tuesday, June 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Musabbabin Haramta Sana’ar Gwangwan A Jihar Borno

by Muhammad Maitela
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya, Rahotonni
0
Musabbabin Haramta Sana’ar Gwangwan A Jihar Borno
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kokarin dakile yawan kai wa masu sana’ar tsoffin karafa farmakin da mayakan Boko Haram ke yi a jihar Borno, Gwamna Farfesa Babagana Zulum, ya kafa dokar haramta sana’ar a fadin jihar, har sai baba ta gani.

Gwamnatin jihar ta kara da cewa, kafa dokar ya zama dole domin kare rayukan masu sana’ar gwangwan, sakamakon hare-haren da `yan ta’addan Boko Haram ke kai musu a baya-bayan nan.

  • Cire Tallafin Mai: Za A Kara Farashin Burodi A Nijeriya
  • Kyakkyawar Alakar Sin Da Amurka Fa’ida ce Ga Duniya Baki Daya

A wata sanarwar manema labaru mai dauke da sa-hannun Mallam Isa Gusau, mai magana da yawun Gwamna Zulum, ya ce, “An kafa wannan dokar ce domin dakile farmakin da yan ta’addan Boko Haram ke kai wa masu wannan sana’ar a wasu kananan hukumomi da kuma hana satar dukiyar jama’a da ake yawan samu.”

Gusau ya kara da cewa, hakan ya zo ne sakamakon yadda wasu wadanda ba a san ko su waye ba, suna zuwa kauyukan da yan ta’addan Boko Haram suka tarwatsa, domin neman tsoffin karafa, inda Boko Haram ke yi musu kwanton bauna tare da kashe su.”

A cewar Gwamna Zulum “A cikin shekaru biyar da suka wuce, an kashe mutane da dama a lokacin da suke shiga kauyuka, a sana’ar gwangwan. Hakan ya sanya dole gwamnatin jihar Borno ta dauki matakin bincike kan matsalolin, al’amarin da ya tilasta kafa wannan dokar.” In ji Zulum.

Labarai Masu Nasaba

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

“Sannan kuma a wadannan wuraren, akwai dukiyoyin gwamnati, da na kamfanonin sadarwa. Wanda irin wadannan ayyuka na sana’ar gwangwan ke zama kalubale da kuma zagon kasa ga Gwamnatin Tarayya da na jihar Borno wajen kula da su. Saboda haka na bayar da umarnin hana sana’ar gwangwan ta karafa a dukkan kananan hukumomin jihar Borno 27.”

Bugu da kari, Gwamna Zulum ya bayyana cewa, wadannan masu sana’ar gwangwan sun yi kaurin suna wajen lalata dukiyoyin jama’a da na kamfanoni masu zaman kansu a mafi yawan kananan hukumomin da rikicin Boko Haram ya tilasta wa mazaunansu tserewa.

Gwamna Zulum ya kara da cewa gwamnatin jihar ta yi asarar kadarori na biliyoyin Naira a cikin shekaru biyar da suka gabata sakamakon ayyukan masu sana’ar gwangwan a jihar.

Gwamnan ya ce wannan dokar ta shafi duk wani nau’i na sana’ar tsoffin karafa wanda ba bisa ka’ida ba, wanda ya hada da wargazawa, tarawa, da kuma jigilar tsoffin karafan a fadin jihar.

Gwamna Zulum ya yi gargadin cewa gwamnatin jihar Borno za ta hada gwiwa da jami’an tsaro wajen aiwatar da dokar yadda ya kamata tare da zartar da hukunci mai tsauri ga duk wanda ya karya dokar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BornoMaiduguriSana'ar GwangwanZulum
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ribadu Zai Shugabanci Taron LEADERSHIP Da NDLEA Kan Yaki Da Miyagun Kwayoyi

Next Post

Daidaita Farashin Canji Ya Fara Haifar Da Da Mai Ido A Nijeriya

Related

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
Rahotonni

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

3 days ago
Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi
Rahotonni

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

3 days ago
‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

3 days ago
Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar
Rahotonni

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

1 week ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

1 week ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

1 week ago
Next Post
Daidaita Farashin Canji Ya Fara Haifar Da Da Mai Ido A Nijeriya

Daidaita Farashin Canji Ya Fara Haifar Da Da Mai Ido A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

An Yi Balaguro Miliyan 657 A Tsakanin Yankunan Kasar Sin Lokacin Bikin Duanwu Na Bana

An Yi Balaguro Miliyan 657 A Tsakanin Yankunan Kasar Sin Lokacin Bikin Duanwu Na Bana

June 2, 2025
NAF Ta Kashe ‘Yan Bindiga Da Dama A Zamfara

Jiragen Yakin NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 20, ‘Yan Banga 2 A Zamfara

June 2, 2025
Ministan Tsaron Singapore: Sinawa Ne Za Su Iya Tantance Batun Taiwan

Ministan Tsaron Singapore: Sinawa Ne Za Su Iya Tantance Batun Taiwan

June 2, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranakun Hutu Domin Bukukuwan Sallah

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranakun Hutu Domin Bukukuwan Sallah

June 2, 2025
Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya

Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya

June 2, 2025
Malaman Jami’ar Gombe Sun Tsunduma Yajin Aikin Sai Baba-ta-gani 

Tsaro: ‘Yansanda Sun Kulle Tashar Dadin Kowa Da Sauransu A Gombe 

June 2, 2025
Mataimakin shugaban kasa

Shettima: Shekaru Biyu Na Mataimaki, Jagora Mai Hangen Nesa Da Kawo Sauyi Nagari

June 2, 2025

Alƙalai Da Lauyoyi Sun Yi Cirko A Gaban Kotu Bayan Fara Yajin Aikin Ma’aikatan Shari’a

June 2, 2025
Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

June 2, 2025
Za A Samu Mamakon Ruwan Sama Da Hazo Daga Litinin Zuwa Laraba A Nijeriya

Za A Samu Mamakon Ruwan Sama Da Hazo Daga Litinin Zuwa Laraba A Nijeriya

June 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.