ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Sauya Sheka Zuwa APC Ba Zai Taimaki Tinuba Yin Tazarce Ba – Jam’iyyar ADC

by Yusuf Shuaibu
9 months ago
APC

Jam’iyyar hadaka ta ADC ta bayyana cewa sauyin sheka na gwamnonin da sauran ‘yan siyasar da aka zaba zuwa jam’iyyar APC ba zai iya tabbatar da tazarcen Shugaban kasa Bola Tinubu zuwa Aso Rock a zaben 2027 ba.

A yayin da yake yin hira ta musamman ga manema labarai a taron masu ruwa da tsaki na jam’iyya a ranar Asabar a Yola, shugaban jam’iyyar ADC reshen Jihar Adamawa, Shehu Yohanna, ya ce ‘yan siyasa da ke komawa jam’iyyar APC mai mulki suna shiga cikin bautar siyasa.

  • Wang Yi Ya Zanta Da Ministocin Wajen Cambodia Da Thailand 
  • Kifi Na Ganin Ka Mai Jar Koma!

Ya ce jam’iyyar ta riga ta yanke shawarar bai wa tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar takarar shugaban kasa, sannan Peter Obi a matsayin mataimakin dan takarar shugaban kasa a zaben 2027.

ADVERTISEMENT

“APC na jan ‘yan siyasa masu matukar bukata da marasa muhimmanci cikin jam’iyyarsu, suna neman jama’a marasa amfani da marasa muhimmanci wadanda ba su da amfani a lokacin zaben 2027.

“Gwamnonin da ke barin jam’iyyarsu zuwa APC su ne wadanda suka gaza matuka kuma suna kokarin dawowa don samun wa’adinsu na biyu.

LABARAI MASU NASABA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

“Sauran gwamnonin da suka sauya sheka da mambobin majalisar dokokin kasa sune wadanda ke kokarin tsere wa hukuncin hukumar yaki da cin hanci da rashawa. Ka tuna lokacin da tsohon shugaban jam’iyyar APC, Sanata Adams Oshiomhole, ya ce, ‘an yi maku gafara idan kuka shiga APC.

“Wannan na nufin sun rasa tasirin siyasa a cikin jam’iyyunsu da jihohinsu. Kuri’u ba sa tare gwamnonin, amma suna tare da talakawa,” in ji Yohanna.

Dangane da zaben cike gurbi na majalisar karamar hukumar Ganye, ya ce, “Zaben cike gurbin majalisar na karamar hukumar Ganye na nuni ga Shugaba Tinubu cewa ya tara mutane marasa amfani a APC. An tura jami’an tsaro sama da 6,000 zuwa Ganye tare da ministoci daga jihohi daban-daban, duk da haka APC ta samu nasara da kuri’u 96, wannan abin kunya ne.

“Idan a shekarar 2023 APC ta lashe wannan kujerar da kuri’u sama da 4,000 kuma a shekarar 2025 APC ta lashe da kuri’u 96 kawai, hakan na nufin jam’iyyar ta rasa tasirinta a Nijeriya,” in ji shi.

Yohanna ya bayyana cewa Atiku ne kawai dan takara da ke da karfin doke APC a zaben shugaban kasa na 2027.

“Manufofin gwamnatin yanzu na yin kamfen ne wajen kalubalantar dawowar Tinubu. Ta yaya za mu ci gaba idan gwamnati ta ce mutum daya zai iya cire kudi na naira 500,000 a mako daya kawai, kuma kungiyoyin kasuwanci su kuma naira 10,000,000 a mako? Tinubu ya jawo koma baya ga kasar nan,” in ji shi.

Ya yi kira ga mambobin ADC su yi rajistar katin zabe, yana cewa hakan shi ne mabudin cire Shugaba Tinubu daga ofis.

“Wadanda ke sa ran yin magudi a zaben 2027 za su ji kunya lokacin da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa ta fitar da sakamakon zabe,” in ji shi.

Yohanna ya yi kira ga ‘yan Nijeriya su kare kuri’unsu ta hayar da shari’a ta taada don amfanin dimokuradiyya, yana gargadin cewa tsarin jam’iyya guda zai sanya dimokuradiyya a cikin mawuyacin hali.

Bisa ga zaben kananan hukumomi na Jihar Adamawa, ya tabbatar wa mambobin jam’iyya cewa ADC za ta lashe dukkan kujerun shugabancin kananan hukumomi 21 da dukkan mazabun da ke jihar baki daya.

APC
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa

MASU ALAKA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
Tambarin Dimokuradiyya

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

September 5, 2026
Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

September 4, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027

August 28, 2026
Next Post
Sin Ta Bukaci Japan Da Ta Kauracewa Kalubalantar Ginshikin Dokar Kasa Da Kasa 

Sin Ta Bukaci Japan Da Ta Kauracewa Kalubalantar Ginshikin Dokar Kasa Da Kasa 

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.