ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Sauya Sheka Zuwa APC Ba Zai Taimaki Tinuba Yin Tazarce Ba – Jam’iyyar ADC

by Yusuf Shuaibu
6 months ago
APC

Jam’iyyar hadaka ta ADC ta bayyana cewa sauyin sheka na gwamnonin da sauran ‘yan siyasar da aka zaba zuwa jam’iyyar APC ba zai iya tabbatar da tazarcen Shugaban kasa Bola Tinubu zuwa Aso Rock a zaben 2027 ba.

A yayin da yake yin hira ta musamman ga manema labarai a taron masu ruwa da tsaki na jam’iyya a ranar Asabar a Yola, shugaban jam’iyyar ADC reshen Jihar Adamawa, Shehu Yohanna, ya ce ‘yan siyasa da ke komawa jam’iyyar APC mai mulki suna shiga cikin bautar siyasa.

  • Wang Yi Ya Zanta Da Ministocin Wajen Cambodia Da Thailand 
  • Kifi Na Ganin Ka Mai Jar Koma!

Ya ce jam’iyyar ta riga ta yanke shawarar bai wa tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar takarar shugaban kasa, sannan Peter Obi a matsayin mataimakin dan takarar shugaban kasa a zaben 2027.

ADVERTISEMENT

“APC na jan ‘yan siyasa masu matukar bukata da marasa muhimmanci cikin jam’iyyarsu, suna neman jama’a marasa amfani da marasa muhimmanci wadanda ba su da amfani a lokacin zaben 2027.

“Gwamnonin da ke barin jam’iyyarsu zuwa APC su ne wadanda suka gaza matuka kuma suna kokarin dawowa don samun wa’adinsu na biyu.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

“Sauran gwamnonin da suka sauya sheka da mambobin majalisar dokokin kasa sune wadanda ke kokarin tsere wa hukuncin hukumar yaki da cin hanci da rashawa. Ka tuna lokacin da tsohon shugaban jam’iyyar APC, Sanata Adams Oshiomhole, ya ce, ‘an yi maku gafara idan kuka shiga APC.

“Wannan na nufin sun rasa tasirin siyasa a cikin jam’iyyunsu da jihohinsu. Kuri’u ba sa tare gwamnonin, amma suna tare da talakawa,” in ji Yohanna.

Dangane da zaben cike gurbi na majalisar karamar hukumar Ganye, ya ce, “Zaben cike gurbin majalisar na karamar hukumar Ganye na nuni ga Shugaba Tinubu cewa ya tara mutane marasa amfani a APC. An tura jami’an tsaro sama da 6,000 zuwa Ganye tare da ministoci daga jihohi daban-daban, duk da haka APC ta samu nasara da kuri’u 96, wannan abin kunya ne.

“Idan a shekarar 2023 APC ta lashe wannan kujerar da kuri’u sama da 4,000 kuma a shekarar 2025 APC ta lashe da kuri’u 96 kawai, hakan na nufin jam’iyyar ta rasa tasirinta a Nijeriya,” in ji shi.

Yohanna ya bayyana cewa Atiku ne kawai dan takara da ke da karfin doke APC a zaben shugaban kasa na 2027.

“Manufofin gwamnatin yanzu na yin kamfen ne wajen kalubalantar dawowar Tinubu. Ta yaya za mu ci gaba idan gwamnati ta ce mutum daya zai iya cire kudi na naira 500,000 a mako daya kawai, kuma kungiyoyin kasuwanci su kuma naira 10,000,000 a mako? Tinubu ya jawo koma baya ga kasar nan,” in ji shi.

Ya yi kira ga mambobin ADC su yi rajistar katin zabe, yana cewa hakan shi ne mabudin cire Shugaba Tinubu daga ofis.

“Wadanda ke sa ran yin magudi a zaben 2027 za su ji kunya lokacin da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa ta fitar da sakamakon zabe,” in ji shi.

Yohanna ya yi kira ga ‘yan Nijeriya su kare kuri’unsu ta hayar da shari’a ta taada don amfanin dimokuradiyya, yana gargadin cewa tsarin jam’iyya guda zai sanya dimokuradiyya a cikin mawuyacin hali.

Bisa ga zaben kananan hukumomi na Jihar Adamawa, ya tabbatar wa mambobin jam’iyya cewa ADC za ta lashe dukkan kujerun shugabancin kananan hukumomi 21 da dukkan mazabun da ke jihar baki daya.

APC
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Next Post
Sin Ta Bukaci Japan Da Ta Kauracewa Kalubalantar Ginshikin Dokar Kasa Da Kasa 

Sin Ta Bukaci Japan Da Ta Kauracewa Kalubalantar Ginshikin Dokar Kasa Da Kasa 

LABARAI MASU NASABA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.