ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Sauya Sheka Zuwa APC Ba Zai Taimaki Tinuba Yin Tazarce Ba – Jam’iyyar ADC

by Yusuf Shuaibu
7 months ago
APC

Jam’iyyar hadaka ta ADC ta bayyana cewa sauyin sheka na gwamnonin da sauran ‘yan siyasar da aka zaba zuwa jam’iyyar APC ba zai iya tabbatar da tazarcen Shugaban kasa Bola Tinubu zuwa Aso Rock a zaben 2027 ba.

A yayin da yake yin hira ta musamman ga manema labarai a taron masu ruwa da tsaki na jam’iyya a ranar Asabar a Yola, shugaban jam’iyyar ADC reshen Jihar Adamawa, Shehu Yohanna, ya ce ‘yan siyasa da ke komawa jam’iyyar APC mai mulki suna shiga cikin bautar siyasa.

  • Wang Yi Ya Zanta Da Ministocin Wajen Cambodia Da Thailand 
  • Kifi Na Ganin Ka Mai Jar Koma!

Ya ce jam’iyyar ta riga ta yanke shawarar bai wa tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar takarar shugaban kasa, sannan Peter Obi a matsayin mataimakin dan takarar shugaban kasa a zaben 2027.

ADVERTISEMENT

“APC na jan ‘yan siyasa masu matukar bukata da marasa muhimmanci cikin jam’iyyarsu, suna neman jama’a marasa amfani da marasa muhimmanci wadanda ba su da amfani a lokacin zaben 2027.

“Gwamnonin da ke barin jam’iyyarsu zuwa APC su ne wadanda suka gaza matuka kuma suna kokarin dawowa don samun wa’adinsu na biyu.

LABARAI MASU NASABA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

“Sauran gwamnonin da suka sauya sheka da mambobin majalisar dokokin kasa sune wadanda ke kokarin tsere wa hukuncin hukumar yaki da cin hanci da rashawa. Ka tuna lokacin da tsohon shugaban jam’iyyar APC, Sanata Adams Oshiomhole, ya ce, ‘an yi maku gafara idan kuka shiga APC.

“Wannan na nufin sun rasa tasirin siyasa a cikin jam’iyyunsu da jihohinsu. Kuri’u ba sa tare gwamnonin, amma suna tare da talakawa,” in ji Yohanna.

Dangane da zaben cike gurbi na majalisar karamar hukumar Ganye, ya ce, “Zaben cike gurbin majalisar na karamar hukumar Ganye na nuni ga Shugaba Tinubu cewa ya tara mutane marasa amfani a APC. An tura jami’an tsaro sama da 6,000 zuwa Ganye tare da ministoci daga jihohi daban-daban, duk da haka APC ta samu nasara da kuri’u 96, wannan abin kunya ne.

“Idan a shekarar 2023 APC ta lashe wannan kujerar da kuri’u sama da 4,000 kuma a shekarar 2025 APC ta lashe da kuri’u 96 kawai, hakan na nufin jam’iyyar ta rasa tasirinta a Nijeriya,” in ji shi.

Yohanna ya bayyana cewa Atiku ne kawai dan takara da ke da karfin doke APC a zaben shugaban kasa na 2027.

“Manufofin gwamnatin yanzu na yin kamfen ne wajen kalubalantar dawowar Tinubu. Ta yaya za mu ci gaba idan gwamnati ta ce mutum daya zai iya cire kudi na naira 500,000 a mako daya kawai, kuma kungiyoyin kasuwanci su kuma naira 10,000,000 a mako? Tinubu ya jawo koma baya ga kasar nan,” in ji shi.

Ya yi kira ga mambobin ADC su yi rajistar katin zabe, yana cewa hakan shi ne mabudin cire Shugaba Tinubu daga ofis.

“Wadanda ke sa ran yin magudi a zaben 2027 za su ji kunya lokacin da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa ta fitar da sakamakon zabe,” in ji shi.

Yohanna ya yi kira ga ‘yan Nijeriya su kare kuri’unsu ta hayar da shari’a ta taada don amfanin dimokuradiyya, yana gargadin cewa tsarin jam’iyya guda zai sanya dimokuradiyya a cikin mawuyacin hali.

Bisa ga zaben kananan hukumomi na Jihar Adamawa, ya tabbatar wa mambobin jam’iyya cewa ADC za ta lashe dukkan kujerun shugabancin kananan hukumomi 21 da dukkan mazabun da ke jihar baki daya.

APC
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

MASU ALAKA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026
Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
Tambarin Dimokuradiyya

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 11, 2026
makarfi
Tambarin Dimokuradiyya

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

June 26, 2026
Next Post
Sin Ta Bukaci Japan Da Ta Kauracewa Kalubalantar Ginshikin Dokar Kasa Da Kasa 

Sin Ta Bukaci Japan Da Ta Kauracewa Kalubalantar Ginshikin Dokar Kasa Da Kasa 

LABARAI MASU NASABA

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.