ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, November 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutane 2 Sun Mutu, An Ceto 5 Yayin Da Gini Ya Rufta A Abuja

by Sadiq
3 years ago
Abuja

Mazauna yankin Kubwa da ke babban birnin tarayya, Abuja sun shiga firgici bayan da wani bene mai hawa biyu ya ruguje wanda ya yi sanadin mutuwar mutum biyu tare da jikkata wasu.

Ginin wanda ake kan gina shi ya ruguje ne a titin Hamza Abdullahi da ke kan titin Gado Nasco.

  • Abin Da Ya Sa Ba A Son Yin Wanka In Ana Ruwa Da Walkiya A Birtaniya
  • Zulum Ya Ba Da Umarnin Bude Ofishin NNPP Da Aka Rufe A Borno

Jami’an Hukumar Bada Agajin Gaggawa ta Kasa (NEMA) na ta aikin ceto wadanda lamarin ya rutsa da su.

ADVERTISEMENT

A cewar NEMA, mutane shida ne lamarin ya rutsa da su.

A cikin wata sanarwa da kakakin hukumar, Manzo Ezekiel, ya fitar, ya ce NEMA ta sanar da faruwar lamarin da misalin karfe 1:00 na rana, inda nan take ta tattara wadanda suka kai daukin gaggawa, wadanda suka hada da hukumar bayar da agajin gaggawa ta Abuja, hukumar kashe gobara, jami’an tsaron farin kaya da kuma ‘yansanda zuwa wurin.

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Yanke Wa Mutum 4 Hukuncin Kisa Kan Kashe Wani Makanike A Kano

Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci

Darakta-Janar na Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Babban Birnin Tarayya Abuja (FEMA), Alhaji Abbas Idris, ya sanar a jiya cewa mutane biyu da suka makale a ginin da ya ruguje a Kubwa da ke wajen birnin Abuja, sun mutu.

Alhaji Idriss, ya ce aikin ceto a wurin da ya rufta ya zo karshe tare da ceto mutane biyar da ransu; uku da suka samu raunuka daban-daban yayin da mutane biyu ba su samu raunuka ba.

A halin da ake ciki, karamar ministar babban birnin tarayya Abuja, Dakta Ramatu Tijjani Aliyu, ta jajanta wa iyalan wadanda ginin Kubwa ya shafa.

Hafeez Olayinka, daya daga cikin wadanda aka ceto daga ginin da ya rufta, ya ce ya shafe sa’o’i a cikin tarko.

Olayinka, wanda ya koma inda lamarin ya faru bayan an yi masa jinya a asibiti, ya shaida wa manema labarai cewa ya isa wurin ginin da ya ruguje ne a ranar Litinin.

“Ni da wasu mun makale tun daren Alhamis. Da misalin karfe 11:30 na dare ranar Alhamis.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kotu Ta Yanke Wa Mutum 4 Hukuncin Kisa Kan Kashe Wani Makanike A Kano
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Mutum 4 Hukuncin Kisa Kan Kashe Wani Makanike A Kano

November 14, 2025
Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci
Manyan Labarai

Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci

November 14, 2025
Jan Aikin Da Ke Gaban Manyan Hafsoshin Tsaron Nijeriya
Manyan Labarai

Jan Aikin Da Ke Gaban Manyan Hafsoshin Tsaron Nijeriya

November 14, 2025
Next Post
Za A Hana ‘Yan Kasar Waje Sayen Amfanin Gona Kai-tsaye A Gonaki

Za A Hana 'Yan Kasar Waje Sayen Amfanin Gona Kai-tsaye A Gonaki

LABARAI MASU NASABA

Editoci Sun Yi Gargadi Kan Rushewar Kafofin Yada Labarai Sakamakon Matsin Tattalin Arziki

Editoci Sun Yi Gargadi Kan Rushewar Kafofin Yada Labarai Sakamakon Matsin Tattalin Arziki

November 14, 2025
Kotu Ta Yanke Wa Mutum 4 Hukuncin Kisa Kan Kashe Wani Makanike A Kano

Kotu Ta Yanke Wa Mutum 4 Hukuncin Kisa Kan Kashe Wani Makanike A Kano

November 14, 2025
Abin Da Ya Sa NPA Ta Yi Hadaka Da ‘Snake Island Port’ -Dakta Dantsoho

Abin Da Ya Sa NPA Ta Yi Hadaka Da ‘Snake Island Port’ -Dakta Dantsoho

November 14, 2025
Shugaban NPA Ya Bukaci A Yi Hadaka Domin Cin Gajiyar Albarkatun Fannin Sufurin Afirka

Shugaban NPA Ya Bukaci A Yi Hadaka Domin Cin Gajiyar Albarkatun Fannin Sufurin Afirka

November 14, 2025
Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci

Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci

November 14, 2025
Jan Aikin Da Ke Gaban Manyan Hafsoshin Tsaron Nijeriya

Jan Aikin Da Ke Gaban Manyan Hafsoshin Tsaron Nijeriya

November 14, 2025
Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

November 13, 2025
Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

November 13, 2025
Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

November 13, 2025
Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya

Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya

November 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.