A yau Asabar, wani mummunan haɗari ya afku yayin da wasu daga cikin tawagar Jihar Kano, da ke dawowa daga gasar Wasannin ƙasa ta 2024, wacce aka gudanar a Jihar Ogun, suka yi haɗari a hanyar dawowarsu kusa da ƙaramar hukumar Kura a Jihar Kano.
Lamarin ya shafi motar da ta ɗauki a ƙalla ‘yan wasa da jami’ai 35, wacce ta faɗa ƙasan wata gada yayin tafiya. Wannan ya haifar da asarar rayuka da dama, yayin da wasu daga cikin matafiyan suka samu raunuka daban-daban.
- ‘Yansanda Sun Kama Mutane 41 Da Ake Zargi Da Kisan DPO A Kano
- Kwararraun Likitocin Tiyata 6 Ne Kacal Suka Rage A Kano – Farfesa Sani
Shaidu sun tabbatar da cewa an sami mummunar asara a wurin haɗarin, yayin da aka garzaya da waɗanda suka jikkata zuwa Asibitin Kura don samun kulawar gaggawa. A halin yanzu, hukumomi ba su fitar da sanarwar a hukumance ba game da adadin waɗanda suka rasu ko kuma dalilin haɗarin ba.
LEADERSHIP ta ruwaito cewa tawagar Kano ta samu lambar zinariya 29 a gasar Wasannin Kasa ta 22 da aka kammala ranar Juma’a, 29 ga Mayu, 2025.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp