ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
Tuggar

A wani lokaci (har ma har zuwa wannan lokacin) a Nijeriya, kalmar “Japa” jin ta abin takaici ne da radadi. Ita ce taken mafarki da kungiyar mawaka masu tsattsauran ra’ayi ke azama.

Ga mutane da yawa, shaida ce da ke alamta samun tabin hankali, hijira ce mai ban tsoro ga mutanen da ke mafi kyawun zuciya.

  • Darajar Cinikayyar Waje Ta Sin Ta Karu Da Kaso Shida Bisa Dari A Afirilu
  • Tsaro Ya Inganta A Zamfara, In Ji Gwamna Lawal Yayin Tattakin Zaman Lafiya Na Tarihi A Jihar

Likitoci sun gudu daga asibitocin da suka cika makil da marasa lafiya. Injiniyoyin ma sun fice domin yin aiki a masana’antu da kamfanonin kasashen waje. Ma’aikatan jinya, masu fikira, masu kaifin basirar kirkira, da masana sun yi ta fita, ba don suna so ba, a’a sai don ba su da wani zabi.

ADVERTISEMENT

Amma idan za a iya ba da wannan labarin ta wata fuska daban, me zai faru idan “japa” ba yana nufin hasara ba?

Me zai faru idan aka yi hijira, lokacin da aka tsara ta kuma da sanin kasa, ya zama babban makamin siyasar kasashen waje mafi girma a Nijeriya?

LABARAI MASU NASABA

Ko Yakin Iran Zai Kawo Karshen Kawancen Amurka Da Kasashen Larabawa?

Yadda Sauya Shekar ‘Yan Siyasa Ta Sauya Fasalin Majalisar Dokokin Kasa

Wannan shi ne babban abin alfahari da Ministan Harkokin Waje, Ambasada Yusuf Maitama Tuggar ke jagoranta. A yayin tattaunawar manyan jami’an biyu a Berlin tare da ministan harkokin wajen Jamus Johann Wadephul, Tuggar ya nuna bajinta. “Ba manufar Nijeriya bace ta fitar da mutane zuwa wasu kasashen waje ba, sai don nuna gwanayenta,” in ji shi, tare da sake sanya haske a manufinta.

A cikin shekarun baya-bayan nan, yawan al’ummar Nijeriya sun kasance ana sanya su a matsayin wadanda ke cikin rikici, miliyoyin matasa marasa aikin yi, masu karatun digiri, da kwararru an nuna musu halin ko-in-kula.

Amma Tuggar, gogaggen jami’in diflomasiyya kuma mai tunani na Afirka, yana ganin abin da mutane da yawa ke watsi da shi dama ce. Ana ganin sama da mutum miliyan 220 da muke da su a yau ana hasashen za su kai miliyan 400 nan da shekarar 2050, don haka Nijeriya ba kawai mai daukar nauyin al’umma bace, ita ce ma’adanin jari-hujja baki daya.

Sabanin haka, Jamus da yawancin Tarayyar Turai suna tsufa da wuri. Tattalin arzikinsu na karuwa, amma yawansu yana raguwa

Kwararrun ma’aikata suna cikin karancin wadata. Vangaren kiwon lafiya ya tabarbare. Masana’antu suna bukatar a karfafe su da kwarewar dijital.

To a nan akwa al’amari mai ban sha’awa: Nijeriya na da hazaka. Turai kuma na da bukata. Amma maimakon a yi asarar wannan wannan hadin gwiwa ta hanyar yanke kauna da yin hijira ba bisa ka’ida ba, Tuggar ya ba da shawarar yin doka, da tsarin hadin gwiwa, wacce za a rika yin hijrar akan tsari.

Wadephul, a nasa bangaren, wannan shawara ba wai ta kasance karbabbiya bace, ai bayan haka abar sha’ace a bayyane

A nasa jawabin, ya jaddada ingancin zurfafa hadin gwiwa tsakanin Nijeriya da Jamus a fannonin da suka hada da kasuwanci zuwa makamashi, da kuma yadda ake tafiyar da ayyuka na hazaka. “Akwai manyan damammaki a hadin gwiwa cikin ma’adanai masu mahimmanci, canjin makamashi, da hadin gwiwar kamfanoni masu zaman kansu,” in ji shi.

Jamus ba ta sanya Nijeriya cikin masu ba da taimako ga masu karba, ko mai taimako ga marasa galihu. Madadin haka, wannan hadin gwiwa ne da zai zama na masu daidaita kasashen da za su daidata bukatun juna da mutunta juna. Tuggar da Wadephul sun binciko hanyoyin zurfafa alaka ta hanyar koyar da sana’o’i, inganta kwarewa, da kirkirar hanyoyin kaura da ke mutunta ikon mallaka da samun dama.

Hadin gwiwar makamashi tsakanin Jamus da Nijeriya, wanda aka fara a 2008 kuma aka karfafa shi a 2021 tare da kafa ofishin hydrogen a Abuja, wani abin koyi ne na yadda kasashen biyu za su iya samar da darajar kayan. Yanzu dai, makasudin yin haka shi ne a sake dawo da irin wannan hadin gwiwa, karfafawa matasa, da sanya hannun jari na kasashen biyu.

A cikin manufofin waje na Tuggar, ba gwaninta bace a rika fita da kaya ta hanyar bazata ba, domin kadara ta kasa. Ya fahimci cewa idan kaura ba ta da tsari, to lallai kasashe sun yi hasara. Amma idan aka yi da kyakkwar niyya kuma ana yin mubaya’a, al’ummomi kasashe za su shigo ciki.

’Yan Najeriya kwararrun da ke aiki a Berlin, Hamburg, Munich, ko Frankfurt ba wai kawai suna cike gibin aiki bane, suna gina gadoji na kasashen waje, aika kudi, samun sabbin kwarewa, da fadada darajar Nijeriya a duniya.

Wannan ba maganar hijira ba ce kawai; wannan shi ne dabarun diflomasiyya.

Wannan tsarin ya kalubalanci ra’ayin da aka dade ana yi wanda Afirka ba ta da wani abin da za ta iya bayarwa. Akasin haka, Afirka, da Nijeriya musamman a shirye suke domin kerawa gami da ba wa duniya abin da ba ta da shi ko take rasawa.

Ayyukan Tuggar a Berlin sun fi ba da fifiko kan kiraye-kirayen girmamawa na bangarorin biyu, da suka kasance wani bangare na hangen nesa wajen sake mayar da Nijeriya a matsayin mai kwarin gwiwa, mai kwarewa wajen taka muhimmiyar rawa a fagen duniya. Har ila yau ya gana da ‘yan majalisar dokokin Jamus, da manyan jami’an raya kasa, da Farfesa Lanz Rolla, wanda shi ne mai hangen nesan da ya kafa taron tattaunawa na duniya na Berlin.

Dangane da jagorancinsa da kuma yadda Nijeriya ke tasowa, an gayyaci Tuggar a hukumance don yin jawabi a taron 2025 na Tattaunawar Duniya ta Berlin. Wannan gayyata kakkarfar alama ce.

Kuma hakan ya tabbatar da rawar da Nijeriya ta taka wajen tsara tattaunawar duniya game da mulki, da dorewa, da kuma yin hijira.

Shekaru da yawa, an yi magana game da Afirka a cikin da’irar duniya. Tuggar yana son Nijeriya ta kasance daya daga cikin masu fada a ji kuma masu jagoranci.

Lokaci ya yi da ‘yan Nijeriya a gida da waje za su daina kallon hijira a matsayin abin takaici. Ba koyaushe ne hijrar take zama tsrewa ake ba,. Wani lokaci, ana ficewa ne domin fadada ilimi. Wani lokaci, masu hijrar ba batu ne na watsar da kasarsu ba, a’a suna fita ne domin ciyar da ita kasar gaba.

Dole ne mu gina tsarin da zai ba matasa ‘yan Nijeriya kayan aiki ba kawai don yin gasa a duniya ba sai don yin nasara da alfahari, daukar su tare da girmamawa, da kuma danganta nasarar kansu ga ci gaban kasa.

Dan Nijeriya mazaunin kasar waje ai ba zama dan kasa ba. Kadara ce kawai ta ketare.

Don yin wannan aikin, dole ne gwamnati ta saka hannun jari a fannin ilimi, fasahar dijital, da horar da sana’o’i. Dole ne kuma ta sake fasalin ayyukan diflomasiyya don tallafa wa hanyoyin kaura na doka da kuma kare ‘yan kasa a kasashen waje daga cin zarafi da nuna wariya.

Amma bayan gwamnati, dole ne kowane dan Najeriya ya sake gyara tunaninsa. “Japa” ba shi ne abin kunya ba. A hannun shugabanni masu hangen nesa kamar Tuggar, ya zama dabara dabara ta hawa abin hawa mai mahimmanci ga kasa.

Kada mu yi la’akari da bin hanya daya. Mu horar da ingantattun tunani, mu samar da ginshikai masu karfi, domin gina Nijeriya a duniya wanda zai amfanar da kowa.

Nijeriya ba ta yi asarar mutanenta ba. Tana amfanuwa ta karkashin kasa.

Kuma yayin da wannan sabon babi ya bayyana-mai tushe cikin mutunci, da tsarin diflomasiyya – har yanzu muna iya gano cewa jiragen da a da suka kwashe mafarkinmu suna dawowa, ba kawai tare da fasinjoji ba, har ma da kyakkyawar manufa.

Tuggar
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

Tuggar
Rahotonni

Ko Yakin Iran Zai Kawo Karshen Kawancen Amurka Da Kasashen Larabawa?

May 17, 2026
Tuggar
Rahotonni

Yadda Sauya Shekar ‘Yan Siyasa Ta Sauya Fasalin Majalisar Dokokin Kasa

May 16, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Rahotonni

Almajiranci:Matsala Ko Maslaha

May 10, 2026
Next Post
Shugaba Tinubu Ya Aika Tawaga Zuwa Jihar Neja Kan Ambaliya Ruwa

Shugaba Tinubu Ya Aika Tawaga Zuwa Jihar Neja Kan Ambaliya Ruwa

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.