• English
  • Business News
Sunday, November 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutane 62 Sun Kuɓuta A Wani Hari Da NAF Ta Kai Wa ‘Yan Bindiga A Katsina

by Sulaiman
3 months ago
NAF

Rundunar sojin sama ta Nijeriya (NAF) ta kai wani hari kan wata rundunar ‘yan bindiga da ta yi kaurin suna a karamar hukumar Danmusa ta jihar Katsina, inda mutane 62 da aka yi garkuwa da su suka yi nasarar tserewa.

 

Sansanin wanda yake a Jigawa Sawai, ya kasance mafakar fitaccen shugaban ‘yan bindigar nan, Muhammadu Fulani, wanda ya addabi al’umomin Matazu, Kankia, Dutsinma a Katsina da sauran sassan jihar Kano.

  • Filato Ta Tsakiya Ta Amince Da Tazarcen Mutfwang A 2027
  • APC Ta Lashe Zaɓen Cike Gurbi Na Garki/Babura A Jigawa

Hare-haren da aka kai ranar Asabar da karfe 5:10 na yamma, ya tilastawa ‘yan bindigar tserewa daga maboyarsu inda dimbin wadanda aka yi garkuwa da su, suka tsere.

 

LABARAI MASU NASABA

Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka

An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano

A wata sanarwa da kwamishinan tsaron cikin gida da harkokin cikin gida na Katsina, Dakta Nasir Mu’azu ya sanyawa hannu, ta bayyana cewa wadanda suka samu kubuta sun kai kimanin mutane 62 bayan da ‘yan bindigar suka tsere saboda harin da jirgin ya kai musu.

 

Ya yi bayanin cewa, yawancin wadanda suka kubuta, an sace su ne daga kauyen Sayaya yayin wani harin da aka kai da daddare a ranar Litinin, 11 ga Agusta, 2025.

 

Mu’azu ya kara da cewa, a halin yanzu 12 daga cikin wadanda suka kubuta, ana kula da lafiyarsu a babban asibitin Matazu, yayin da 16 kuma ke cibiyar lafiya fa rundunar sojoji ta ‘Forward Operating Base (FOB)’ da ke Kaiga Malamai domin samun kulawar lafiya ta matakin farko.

 

 

Gwamna Dikko Umaru Radda ya yaba wa kokarin jami’an tsaro tare da jaddada aniyar gwamnati na kawo karshen ‘yan bindiga a jihar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka
Manyan Labarai

Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka

November 2, 2025
Yaya Da Kani Sun Mutu A Cikin Ramin Masai A Kano
Manyan Labarai

An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano

November 2, 2025
Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima
Manyan Labarai

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

November 1, 2025
Next Post
Ministan Yaɗa Labarai Ya Taya Janar Babangida Murnar Cika Shekaru 84

Ministan Yaɗa Labarai Ya Taya Janar Babangida Murnar Cika Shekaru 84

LABARAI MASU NASABA

An Bude Sabon Babin Huldar Sin Da Koriya Ta Kudu

An Bude Sabon Babin Huldar Sin Da Koriya Ta Kudu

November 2, 2025
Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?

Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?

November 2, 2025
A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?

A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?

November 2, 2025
Maganin Nankarwa (3)

Maganin Nankarwa (3)

November 2, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Dalilin Da Ya Sa Hukumar NIWA Ta Fara Gyaran Hanyoyin Ruwa A Jihar Legas

November 2, 2025
Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka

Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka

November 2, 2025
Barazanar Amurka Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya: Tinubu Da Trump Za Su Gana Kwanan Nan — Bwala

Barazanar Amurka Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya: Tinubu Da Trump Za Su Gana Kwanan Nan — Bwala

November 2, 2025
Yaya Da Kani Sun Mutu A Cikin Ramin Masai A Kano

An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano

November 2, 2025
Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

November 2, 2025
Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

November 1, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.