• English
  • Business News
Saturday, October 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutane 8 Sun Mutu A Ruwa A Jihar Jigawa

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Mutane 8 Sun Mutu A Ruwa A Jihar Jigawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Akalla mutane takwas ne suka rasa rayukansu a sanadiyyar kifewar kwalekwale da kuma nutsewa a ruwa a kananan hukumomin Gwaram da Kaugama da ke Jihar Jigawa.

An ruwaito cewa mutum biyar dai sun rasu ne a kauyen Martaba da ke karamar hukumar Gwaram, inda aka samu nasarar ceto hudu daga cikinsu.

  • Magidanci Ya Nemi Matarsa Ta Biya Naira Miliyan 1.6 Kafin Ya Sake Ta A Kaduna
  • Rashin Kulawa Da Jama’a Ba Dimokuradiyya Ba Ce

A wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yansandan jihar, DSP Lawan Shi’isu Adam, ya cw kwale-kwalen ya kife da mutanen ne yayin da suke kan hanyarsu ta dawowa daga masallaci.

“Mutane hudu, da suka hada da wani mai shekara 60 mai suna Barkeji, sun tsira da rayukansu inda aka samu ceto su da ransu,” in ji kakakin.

Ya kuma ce a sanadiyyar gudunmawar da wasu masunta suka kai, an samu gawawwaki biyar da suka hada da wani dattijo mai suna Lukateru mai shekara 60 da Musa mai shekara 50 da Sale mai shekara 50 da Alhaji Shuaibu mai shekara 60 da Dogo mai shekara 50, dukkansu mazauna garin Darazau da ke Jihar Bauchi.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Zai Ziyarci Jos Domin Halartar Jana’izar Mahaifiyar Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa

PENGASSAN Ta Yi Watsi Da Tayin Dangote Na Biyan Ma’aikata Albashin Shekaru 5 Ba Tare Da Yin Aiki Ba

Ya kara da cewa, tuni an mika gawawwakin ga iyalai da ‘yan uwansu domin yi musu jana’iza.

A wani labarin kuma, wasu yara mata uku, sun rasu a sakamakon nutsewa a ruwa a kauyen Faskarau da ke garin Ja’e a karamar hukumar Kaugaman a Jihar Jigawa.

Yaran sun hada da Maryam Salisu mai shekara 10 da Bahayura Lawan, ita mai shekara 10 da kuma Lawisa Sule mai shekara takwas a duniya.

A wata sanarwa da kakakin hukumar tsaro ta NSCDC, CSC Adamu Shehu, ya fitar a ranar Litinin, ya ce lamarin ya faru ne da misalin karfe 11:00 na safiyar Litinin, yayin da suka je wanki a rafi.

Ya ce an kai gawarwakinsu babban asibitin Kaugama, inda likita ya tabbatar da rasuwarsu.

Bincike ya nuna cewar, yaran, bayan sun gama wankin nasu ne suka yanke shawarar yin wanka, lamarin da ya jawo rasa rayukansu.

Mazauna yankin sun tabbatar da cewar shekaru 20 da suka gabata, an taba samun irin wannan iftila’in inda yara uku mata suka rasu.

Tuni aka yi musu jana’iza kamar yadda addinin Musulunci ya tanada bayan mika gawarwakinsu ga iyalansu.

A nasa bangaren, babban kwamandan rundunar ta NSCDC a jihar, Musa Alhaji Mala, ya jajanta wa iyalan mamatan, gami da jan hankalin iyaye da su kula wajen tura yara rafi, musamman a wannan lokacin da ake fama da ambaliyar ruwa a fadin Jihar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AjaliGawaKwale-KwaleMutuwaNCDSRadiWankaWankiYara
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Soma Shari’ar Matashin Da Ya Yi Sanadin Yanke Kafar Wata Yarinya A Sakkwato 

Next Post

Ruwan Sama Ya Kashe Mutane 5, Ya Lalata Gidaje 3,813 A Katsina

Related

Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Tinubu Zai Ziyarci Jos Domin Halartar Jana’izar Mahaifiyar Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa

13 hours ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

PENGASSAN Ta Yi Watsi Da Tayin Dangote Na Biyan Ma’aikata Albashin Shekaru 5 Ba Tare Da Yin Aiki Ba

20 hours ago
NAFDAC Ta Rufe Manyan Shaguna 2 Na Ƴan China A Abuja
Manyan Labarai

NAFDAC Ta Rufe Manyan Shaguna 2 Na Ƴan China A Abuja

20 hours ago
Nijeriya A Shekara 65: Kwan-gaba Kwan-baya A Sha’anin Tsaro Da Siyasa Da Zamantakewa
Manyan Labarai

Nijeriya A Shekara 65: Kwan-gaba Kwan-baya A Sha’anin Tsaro Da Siyasa Da Zamantakewa

1 day ago
Katsina Za Ta Ɗauki Nauyin Karatun Mahaddata Alƙur’ani – Gwamna Radda
Manyan Labarai

Ina Aka Kwana Batun Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Dazukan Jihar Katsina?

1 day ago
Dubban Matasan Kano Sun Yi Zanga-zangar Lumana Domin Goyon Bayan CP AI Bakori
Manyan Labarai

Dubban Matasan Kano Sun Yi Zanga-zangar Lumana Domin Goyon Bayan CP AI Bakori

2 days ago
Next Post
Ruwan Sama Ya Kashe Mutane 5, Ya Lalata Gidaje 3,813 A Katsina

Ruwan Sama Ya Kashe Mutane 5, Ya Lalata Gidaje 3,813 A Katsina

LABARAI MASU NASABA

Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato

Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato

October 4, 2025
Jami’ar Ibadan Ta Bude Sashen Karatu A Gida Ta Intanet

Jami’ar Ibadan Ta Bude Sashen Karatu A Gida Ta Intanet

October 4, 2025
Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

October 4, 2025
Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

October 4, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

October 4, 2025
Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

October 3, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Tinubu Zai Ziyarci Jos Domin Halartar Jana’izar Mahaifiyar Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa

October 3, 2025
MDD Ta Yi Alƙawarin Tallafa Wa Gidauniyar Malala Mai Rajin Inganta Ilimin ‘Ya’ya Mata

MDD Ta Yi Alƙawarin Tallafa Wa Gidauniyar Malala Mai Rajin Inganta Ilimin ‘Ya’ya Mata

October 3, 2025
Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

October 3, 2025
Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo

Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo

October 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.