• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutane 8 Sun Mutu A Ruwa A Jihar Jigawa

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Mutane 8 Sun Mutu A Ruwa A Jihar Jigawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Akalla mutane takwas ne suka rasa rayukansu a sanadiyyar kifewar kwalekwale da kuma nutsewa a ruwa a kananan hukumomin Gwaram da Kaugama da ke Jihar Jigawa.

An ruwaito cewa mutum biyar dai sun rasu ne a kauyen Martaba da ke karamar hukumar Gwaram, inda aka samu nasarar ceto hudu daga cikinsu.

  • Magidanci Ya Nemi Matarsa Ta Biya Naira Miliyan 1.6 Kafin Ya Sake Ta A Kaduna
  • Rashin Kulawa Da Jama’a Ba Dimokuradiyya Ba Ce

A wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yansandan jihar, DSP Lawan Shi’isu Adam, ya cw kwale-kwalen ya kife da mutanen ne yayin da suke kan hanyarsu ta dawowa daga masallaci.

“Mutane hudu, da suka hada da wani mai shekara 60 mai suna Barkeji, sun tsira da rayukansu inda aka samu ceto su da ransu,” in ji kakakin.

Ya kuma ce a sanadiyyar gudunmawar da wasu masunta suka kai, an samu gawawwaki biyar da suka hada da wani dattijo mai suna Lukateru mai shekara 60 da Musa mai shekara 50 da Sale mai shekara 50 da Alhaji Shuaibu mai shekara 60 da Dogo mai shekara 50, dukkansu mazauna garin Darazau da ke Jihar Bauchi.

Labarai Masu Nasaba

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Ya kara da cewa, tuni an mika gawawwakin ga iyalai da ‘yan uwansu domin yi musu jana’iza.

A wani labarin kuma, wasu yara mata uku, sun rasu a sakamakon nutsewa a ruwa a kauyen Faskarau da ke garin Ja’e a karamar hukumar Kaugaman a Jihar Jigawa.

Yaran sun hada da Maryam Salisu mai shekara 10 da Bahayura Lawan, ita mai shekara 10 da kuma Lawisa Sule mai shekara takwas a duniya.

A wata sanarwa da kakakin hukumar tsaro ta NSCDC, CSC Adamu Shehu, ya fitar a ranar Litinin, ya ce lamarin ya faru ne da misalin karfe 11:00 na safiyar Litinin, yayin da suka je wanki a rafi.

Ya ce an kai gawarwakinsu babban asibitin Kaugama, inda likita ya tabbatar da rasuwarsu.

Bincike ya nuna cewar, yaran, bayan sun gama wankin nasu ne suka yanke shawarar yin wanka, lamarin da ya jawo rasa rayukansu.

Mazauna yankin sun tabbatar da cewar shekaru 20 da suka gabata, an taba samun irin wannan iftila’in inda yara uku mata suka rasu.

Tuni aka yi musu jana’iza kamar yadda addinin Musulunci ya tanada bayan mika gawarwakinsu ga iyalansu.

A nasa bangaren, babban kwamandan rundunar ta NSCDC a jihar, Musa Alhaji Mala, ya jajanta wa iyalan mamatan, gami da jan hankalin iyaye da su kula wajen tura yara rafi, musamman a wannan lokacin da ake fama da ambaliyar ruwa a fadin Jihar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AjaliGawaKwale-KwaleMutuwaNCDSRadiWankaWankiYara
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Soma Shari’ar Matashin Da Ya Yi Sanadin Yanke Kafar Wata Yarinya A Sakkwato 

Next Post

Ruwan Sama Ya Kashe Mutane 5, Ya Lalata Gidaje 3,813 A Katsina

Related

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

17 hours ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

1 day ago
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

2 days ago
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi
Manyan Labarai

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

2 days ago
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

2 days ago
Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

2 days ago
Next Post
Ruwan Sama Ya Kashe Mutane 5, Ya Lalata Gidaje 3,813 A Katsina

Ruwan Sama Ya Kashe Mutane 5, Ya Lalata Gidaje 3,813 A Katsina

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.