ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rashin Kulawa Da Jama’a Ba Dimokuradiyya Ba Ce

by CMG Hausa
4 years ago
Dimokuradiyya

Mutanen duniya na kallon kasar Amurka a matsayin wata babbar kasa, wadda ke kan gaba a fannin tattalin arziki, da na ingancin aikin likitanci.

Sai dai kasar ta fi shan kaye a fannin tinakar cutar COVID-19 a duniya, ganin yadda mutanen kasar miliyan 94.6 suka kamu da cutar, kana wasu miliyan 1.04 daga cikinsu suka mutu sakamakon cutar, inda suka kasance kimanin kashi 1 bisa kashi 6 na adadin duniya baki daya.

  • Sassauta Matakan Kandagarkin Cutar COVID-19 A Amurka Ya Haifar Da Mumunan Tasiri

Sai dai kasar ta sake gyaran manufarta a fannin tinkarar annobar COVID-19 a kwanan baya, inda ta fara dakatar da samar da na’urorin gwajin kwayoyin cuta kyauta daga ranar 2 ga watan Satumban da muke ciki, kana gwamnatin kasar za ta daina biyan kudin jinyar mutanen da suka kamu da cutar, da na yi wa mutanen kasar allurar rigakafi, maimakon haka za a dora nauyin kan kamfanonin ishora da jama’ar kasar.

ADVERTISEMENT

Duk da cewa kasar na ci gaba da fama da yanayi mai tsanani ta fuskar tinkarar cutar COVID-19.

An ce a makon da ya gabata, an samu karin mutane fiye da 85274 dake kamuwa da cutar COVID-19 da kimanin wasu 500 da suka mutu sakamakon cutar a kasar a kowace rana.

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

To, ina dalilin da ya sa kasar Amurka ke ci gaba da saukaka matakan tinkarar annoba, yayin da yanayin cutar ke kara tsananta a kasar?
Da farko, gwamnatin kasar Amurka na fama da matsalar karancin kudi.
Bayan barkewar annobar COVID-19, gwamnatin kasar Amurka ta sha cin bashi da yawa, don daukar matakan tinkarar annoba, da sa kaimi ga bunkasuwar tattalin arziki. Sai dai matakin ya haddasa hauhawar farashin kayayyaki, da ba jama’a wahalar zaman rayuwa.

Zuwa yanzu,gwamnatin Joe Biden na neman rage kudin da hukumomin kasar ke kashewa, da takaita hauhawar farashin kaya, lamarin da ya sa ake fama da karancin kudi a ayyuka daban daban, ciki har da aikin tinkarar annoba.

Na biyu, shi ne, gogayar da jam’iyyun siysan kasar Amurka suke yi ta hana zuba jari ga aikin kandagarkin yaduwar annoba. Bayan gwamnatin kasar ta ce ana fama da matsalar karancin kudi na tinkarar annoba, nan take su ‘yan majalissun da suka kasance ‘ya’yan jam’iyyar Republican ta kasar suka fara zargin White House da yin karya. Daga baya aka hana zuba karin jari ga aikin tinkarar annoba.

Sa’an nan dalili na uku wanda ya fi muhimmanci shi ne, a ganin wasu ‘yan siyasan kasar Amurka, aikin kare lafiyar jama’ar kasar ba shi da muhimmanci, idan an kwatanta shi da aikin kasar na neman yin babakere a duniya, da yada tunanin Dimokuradiya irin na kasar.

A watan Maris na bana, an zartas da kasafin kudi da darajarsa ta kai dalar Amurka triliyan 1.5 a majalissun dokokin kasar Amurka.

Sai dai a cikin kundin kasafin kudin, an soke shiri na dala biliyan 15.6 na tallafawa kokarin tinkarar cutar COVID-19 sakamakon sabanin ra’ayin da ake samu tsakanin jam’iyyun siyasa na kasar, kana a maimakonsa an zartas da kudin tallafi na dala biliyan 13.6 da za a ba kasar Ukraine.

Yanzu haka majalissun dokokin kasar Amurka sun riga sun amince da tallafi na dala biliyan 50 da ake neman baiwa kasar ta Ukraine.

Wannan ya nuna cewa, idan tana so, kasar Amurka za ta iya samun kudin da take bukata wajen tinkarar annoba. Sai dai a idanun ‘yan siyasan kasar, aikin yayyata tunanin Dimokuradiya irin na kasar Amurka ya fi muhimmanci.

Sanin kowa ne, kafin a ce wata kasa mai tsari na dimokuradiya ne, ya kamata a duba manufofinta na taimakawa kare moriyar jama’a.

Yadda kasar Amurka ta zuba kudi ga Ukraine, ya taimaki ‘yan siyasan kasar cimma burinsu na tabbatar da yin babakere a duniya, da fitar da tunanin Dimokuradiya irin na kasar Amurka. Haka kuma ya sa kamfanonin kera makamai na kasar cin riba sosai.

Sa’an nan bayan da gwamnatin kasar Amurka ta mika aikin kare jama’a daga annoba ga kasuwa, su kamfanonin samar da magunguna da masu ba da hidimar jinya za su samu makudan kudi. Sai dai an kasa kula da wasu.

Saboda har yanzu a kasar Amurka akwai kimanin mutane miliyan 30 da ba su iya sayen hidimar inshorar lafiya ba. Daina samar da hidimomi kyauta na nufin za a kyale lafiya da tsaron wadannan mutane marasa karfi. Ga ta nan dai, wata kasar da ta kasa kulawa da jama’arta, har ma tana so a dinga kallonta a matsayin mai jagorantar aikin raya dimokuradiya.

Yadda gwamnatin kasar Amurka ta kasa sauke nauyin dake bisa wuyanta na tinkarar annobar COVID-19 ya sa jama’ar kasar shan wahala sosai.

A sa’i daya kuma, ya sa mutanen duniya fahimtar cewa alkawarinta na kare dimokuradiya a duniya ba shi da gaskiya, saboda Rashin kulawa da jama’a ba dimokuradiya ba ce. (Bello Wang)

Dimokuradiyya
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa
Daga Birnin Sin

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Next Post
Da Dumi-dumi: Liz Truss Ce Sabuwar Fira Ministar Burtaniya

Da Dumi-dumi: Liz Truss Ce Sabuwar Fira Ministar Burtaniya

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.