ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutane 8 Sun Mutu A Ruwa A Jihar Jigawa

by Sadiq
4 years ago
Ruwa

Akalla mutane takwas ne suka rasa rayukansu a sanadiyyar kifewar kwalekwale da kuma nutsewa a ruwa a kananan hukumomin Gwaram da Kaugama da ke Jihar Jigawa.

An ruwaito cewa mutum biyar dai sun rasu ne a kauyen Martaba da ke karamar hukumar Gwaram, inda aka samu nasarar ceto hudu daga cikinsu.

  • Magidanci Ya Nemi Matarsa Ta Biya Naira Miliyan 1.6 Kafin Ya Sake Ta A Kaduna
  • Rashin Kulawa Da Jama’a Ba Dimokuradiyya Ba Ce

A wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yansandan jihar, DSP Lawan Shi’isu Adam, ya cw kwale-kwalen ya kife da mutanen ne yayin da suke kan hanyarsu ta dawowa daga masallaci.

ADVERTISEMENT

“Mutane hudu, da suka hada da wani mai shekara 60 mai suna Barkeji, sun tsira da rayukansu inda aka samu ceto su da ransu,” in ji kakakin.

Ya kuma ce a sanadiyyar gudunmawar da wasu masunta suka kai, an samu gawawwaki biyar da suka hada da wani dattijo mai suna Lukateru mai shekara 60 da Musa mai shekara 50 da Sale mai shekara 50 da Alhaji Shuaibu mai shekara 60 da Dogo mai shekara 50, dukkansu mazauna garin Darazau da ke Jihar Bauchi.

LABARAI MASU NASABA

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

Ya kara da cewa, tuni an mika gawawwakin ga iyalai da ‘yan uwansu domin yi musu jana’iza.

A wani labarin kuma, wasu yara mata uku, sun rasu a sakamakon nutsewa a ruwa a kauyen Faskarau da ke garin Ja’e a karamar hukumar Kaugaman a Jihar Jigawa.

Yaran sun hada da Maryam Salisu mai shekara 10 da Bahayura Lawan, ita mai shekara 10 da kuma Lawisa Sule mai shekara takwas a duniya.

A wata sanarwa da kakakin hukumar tsaro ta NSCDC, CSC Adamu Shehu, ya fitar a ranar Litinin, ya ce lamarin ya faru ne da misalin karfe 11:00 na safiyar Litinin, yayin da suka je wanki a rafi.

Ya ce an kai gawarwakinsu babban asibitin Kaugama, inda likita ya tabbatar da rasuwarsu.

Bincike ya nuna cewar, yaran, bayan sun gama wankin nasu ne suka yanke shawarar yin wanka, lamarin da ya jawo rasa rayukansu.

Mazauna yankin sun tabbatar da cewar shekaru 20 da suka gabata, an taba samun irin wannan iftila’in inda yara uku mata suka rasu.

Tuni aka yi musu jana’iza kamar yadda addinin Musulunci ya tanada bayan mika gawarwakinsu ga iyalansu.

A nasa bangaren, babban kwamandan rundunar ta NSCDC a jihar, Musa Alhaji Mala, ya jajanta wa iyalan mamatan, gami da jan hankalin iyaye da su kula wajen tura yara rafi, musamman a wannan lokacin da ake fama da ambaliyar ruwa a fadin Jihar.

MASU ALAKA

Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje
Manyan Labarai

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Next Post
Ruwan Sama Ya Kashe Mutane 5, Ya Lalata Gidaje 3,813 A Katsina

Ruwan Sama Ya Kashe Mutane 5, Ya Lalata Gidaje 3,813 A Katsina

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.