• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutum 10 Sun Rasu, Da Dama Sun Jikkata A Wani Sabon Hari A Kudancin Kaduna

by Sadiq
2 years ago
in Da ɗumi-ɗuminsa
0
Mutum 10 Sun Rasu, Da Dama Sun Jikkata A Wani Sabon Hari A Kudancin Kaduna
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wani sabon harin da aka kai unguwar Langson da ke karamar hukumar Zango Kataf a jihar Kaduna, an tabbatar da mutuwar mutane akalla 10 tare da jikkata wasu da dama.

Harin wanda aka ce ya faru ne a daren ranar Talata har zuwa wayewar safiyar Laraba, an ce ya faru ne duk da dokar hana fita ta sa’o’i 24 da aka kafa bayan harin da aka kai a makon jiya da ya yi sanadin mutuwar mutane 17.

  • ‘Yan Takaran Gwamna 8 Sun Mara Wa Gwamnan Gombe Baya
  • EFCC Ta Damke ‘Yan Damfara 21 A Abuja

A halin da ake ciki kuma, shugabannin kungiyar ci gaban al’ummar Atyap (ACDA), wadanda suka tabbatar da harin na baya-bayan nan, sun nuna rashin amincewa da jami’an tsaron da aka tura yankin domin kare rayuka da dukiyoyinsu.

Shugaban ACDA na kasa, Mista Sam Achie, ya ce, “’Yansandan tsaro da aka tura Kudancin Kaduna ba su ba mu kariya, domin an dade ana kashe-kashe ba tare da la’akari da hakan ba, amma gwamnati ta yi shiru.

Achie, wanda ya bayyana hakan a wurin da aka kai harin a lokacin da ya kai ziyara, ya jaddada cewa shiru da gwamnatin jihar Kaduna ta yi kan ci gaba da kai hare-hare a yankin abin damuwa ne.

Labarai Masu Nasaba

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

Gobara Ta Tashi A Barikin Sojoji A Borno, Bama-bamai Sun Fashe

Don haka ya bukaci gwamnati dauki matakin kawo karshen hare-haren.

Shugaban ACDA na kasa, ya yabawa rundunar MOPOL da ke yankin Langson, wanda aka ce sun fatattaki maharan, yayin da ya yi kira ga jama’a da su ci gaba da kasancewa cikin shiri domin kare kan su da dukiyoyinsu daga azzalumai.

Ya bayyana cewa wadanda suka jikkata a harin na samun kulawa a wasu asibitocin yankin.

A nasa bangaren, shugaban karamar hukumar Zango Kataf, Mista Francis Sani, wanda shi ma ya tabbatar da faruwar harin, ya roki gwamnatin jihar da ta kara tura jami’an tsaro zuwa karamar hukumar Zango Kataf, domin kare rayuka da dukiyoyin jama’a a yankin.

LEADERSHIP ta tattaro, cewar maharan sun mamaye al’ummar garin ne da misalin karfe 9 na daren ranar Talata, inda suka yi ta harbe-harbe inda suka kashe jama’a, tare da raunata wasu, tare da yin awon gaba da wani mai shago a yankin, kafin daga bisani MOPOL suka fatattake su.

Kakakin rundunar Operation Safe Haven, Laftanar Kanar I.S. Takwa, bai amsa waya ba don jin ta bakinsa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KadunaKisaMaharaYan bindigaZangon Kataf
ShareTweetSendShare
Previous Post

Zaben Gwamnoni: INEC Ta Gargadi Jam’iyyun Siyasa Kan Tada Tarzoma

Next Post

Hatsarin Mota Sun Yi Ajalin Mutum 17, 17 Sun Jikkata A Bauchi

Related

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma
Da ɗumi-ɗuminsa

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

6 days ago
Gobara Ta Tashi A Barikin Sojoji A Borno, Bama-bamai Sun Fashe
Da ɗumi-ɗuminsa

Gobara Ta Tashi A Barikin Sojoji A Borno, Bama-bamai Sun Fashe

2 weeks ago
Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa N835 Kan Kowace Lita
Da ɗumi-ɗuminsa

Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa N835 Kan Kowace Lita

4 weeks ago
Fitaccen Malamin Musulunci Mai Da’awar Sunnah A Nijeriya, Dr. Idris Dutsen Tanshi Ya Rasu
Da ɗumi-ɗuminsa

Fitaccen Malamin Musulunci Mai Da’awar Sunnah A Nijeriya, Dr. Idris Dutsen Tanshi Ya Rasu

1 month ago
Ku Gafarce Ni, Na Yi Nadamar Tallata Tinubu Da Na Yi – Ɗanbilki Kwamanda
Da ɗumi-ɗuminsa

Ku Gafarce Ni, Na Yi Nadamar Tallata Tinubu Da Na Yi – Ɗanbilki Kwamanda

3 months ago
Umar Farouk Ibrahim (Sakataren Gwamnatin Kano)
Da ɗumi-ɗuminsa

Watanni 2 Da Sauke Baffa Bichi, An Nada Umar Farouk Mukamin Sakataren Gwamnatin Kano

3 months ago
Next Post
Hatsarin Mota Sun Yi Ajalin Mutum 17, 17 Sun Jikkata A Bauchi

Hatsarin Mota Sun Yi Ajalin Mutum 17, 17 Sun Jikkata A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.