• English
  • Business News
Wednesday, August 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutum 10 Sun Rasu, Da Dama Sun Jikkata A Wani Sabon Hari A Kudancin Kaduna

by Sadiq
2 years ago
in Da ɗumi-ɗuminsa
0
Mutum 10 Sun Rasu, Da Dama Sun Jikkata A Wani Sabon Hari A Kudancin Kaduna
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wani sabon harin da aka kai unguwar Langson da ke karamar hukumar Zango Kataf a jihar Kaduna, an tabbatar da mutuwar mutane akalla 10 tare da jikkata wasu da dama.

Harin wanda aka ce ya faru ne a daren ranar Talata har zuwa wayewar safiyar Laraba, an ce ya faru ne duk da dokar hana fita ta sa’o’i 24 da aka kafa bayan harin da aka kai a makon jiya da ya yi sanadin mutuwar mutane 17.

  • ‘Yan Takaran Gwamna 8 Sun Mara Wa Gwamnan Gombe Baya
  • EFCC Ta Damke ‘Yan Damfara 21 A Abuja

A halin da ake ciki kuma, shugabannin kungiyar ci gaban al’ummar Atyap (ACDA), wadanda suka tabbatar da harin na baya-bayan nan, sun nuna rashin amincewa da jami’an tsaron da aka tura yankin domin kare rayuka da dukiyoyinsu.

Shugaban ACDA na kasa, Mista Sam Achie, ya ce, “’Yansandan tsaro da aka tura Kudancin Kaduna ba su ba mu kariya, domin an dade ana kashe-kashe ba tare da la’akari da hakan ba, amma gwamnati ta yi shiru.

Achie, wanda ya bayyana hakan a wurin da aka kai harin a lokacin da ya kai ziyara, ya jaddada cewa shiru da gwamnatin jihar Kaduna ta yi kan ci gaba da kai hare-hare a yankin abin damuwa ne.

Labarai Masu Nasaba

Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

Don haka ya bukaci gwamnati dauki matakin kawo karshen hare-haren.

Shugaban ACDA na kasa, ya yabawa rundunar MOPOL da ke yankin Langson, wanda aka ce sun fatattaki maharan, yayin da ya yi kira ga jama’a da su ci gaba da kasancewa cikin shiri domin kare kan su da dukiyoyinsu daga azzalumai.

Ya bayyana cewa wadanda suka jikkata a harin na samun kulawa a wasu asibitocin yankin.

A nasa bangaren, shugaban karamar hukumar Zango Kataf, Mista Francis Sani, wanda shi ma ya tabbatar da faruwar harin, ya roki gwamnatin jihar da ta kara tura jami’an tsaro zuwa karamar hukumar Zango Kataf, domin kare rayuka da dukiyoyin jama’a a yankin.

LEADERSHIP ta tattaro, cewar maharan sun mamaye al’ummar garin ne da misalin karfe 9 na daren ranar Talata, inda suka yi ta harbe-harbe inda suka kashe jama’a, tare da raunata wasu, tare da yin awon gaba da wani mai shago a yankin, kafin daga bisani MOPOL suka fatattake su.

Kakakin rundunar Operation Safe Haven, Laftanar Kanar I.S. Takwa, bai amsa waya ba don jin ta bakinsa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KadunaKisaMaharaYan bindigaZangon Kataf
ShareTweetSendShare
Previous Post

Zaben Gwamnoni: INEC Ta Gargadi Jam’iyyun Siyasa Kan Tada Tarzoma

Next Post

Hatsarin Mota Sun Yi Ajalin Mutum 17, 17 Sun Jikkata A Bauchi

Related

Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano
Da ɗumi-ɗuminsa

Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

18 hours ago
Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 
Da ɗumi-ɗuminsa

Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

4 days ago
Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa
Da ɗumi-ɗuminsa

Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa

1 week ago
Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci
Da ɗumi-ɗuminsa

Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci

1 week ago
Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje
Da ɗumi-ɗuminsa

Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

1 week ago
Gwamnatin Sakkwato Ta Ƙaddamar Da Sababbin Motoci 30, Don Bunƙasa Sha’anin Sufuri A Jihar
Da ɗumi-ɗuminsa

Super Falcons Sun Iso Abuja Ɗauke Da Kofin WAFCON

1 week ago
Next Post
Hatsarin Mota Sun Yi Ajalin Mutum 17, 17 Sun Jikkata A Bauchi

Hatsarin Mota Sun Yi Ajalin Mutum 17, 17 Sun Jikkata A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Taya Nafisa, Rukayya, Hadiza Murnar Samun Nasarar Zama Gwanaye A Gasar Turanci Ta Duniya

Tinubu Ya Taya Nafisa, Rukayya, Hadiza Murnar Samun Nasarar Zama Gwanaye A Gasar Turanci Ta Duniya

August 6, 2025
Sin Ta Samar Da Yuan Biliyan Daya Domin Ayyukan Jin Kai Sakamakon Ibtila’in Ambaliyar Ruwa

Sin Ta Samar Da Yuan Biliyan Daya Domin Ayyukan Jin Kai Sakamakon Ibtila’in Ambaliyar Ruwa

August 6, 2025
Uwargidar Gwamnan Katsina Ta Nemi A Taimaka Wa Mata Wajen Yaƙi Da Ciwon Nono Da Na Mahaifa

Uwargidar Gwamnan Katsina Ta Nemi A Taimaka Wa Mata Wajen Yaƙi Da Ciwon Nono Da Na Mahaifa

August 6, 2025
Bello Turji Bai Yi Sulhu Da Kowa Ba – Guyawa Isa

Bello Turji Bai Yi Sulhu Da Kowa Ba – Guyawa Isa

August 6, 2025
Sojoji Sun Kama Mai Yi Wa Boko Haram Safarar Man Fetur A Borno

Sojoji Sun Kama Mai Yi Wa Boko Haram Safarar Man Fetur A Borno

August 6, 2025
Matar Marigayi MKO Abiola, Ta Rasu Tana Da Shekaru 82

Matar Marigayi MKO Abiola, Ta Rasu Tana Da Shekaru 82

August 6, 2025
Remi Tinubu Ta Bai Wa Waɗanda Ambaliya Ta Shafa A Neja Tallafin N1bn

Remi Tinubu Ta Bai Wa Waɗanda Ambaliya Ta Shafa A Neja Tallafin N1bn

August 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Farfaɗo Da Noman Dabino – Shettima

Gwamnatin Tarayya Za Ta Farfaɗo Da Noman Dabino – Shettima

August 6, 2025
Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

August 6, 2025
Hare-haren Boko Haram Da ‘Yan Bindiga Ya Ragu A Cikin Shekaru Biyu – Ribadu

Hare-haren Boko Haram Da ‘Yan Bindiga Ya Ragu A Cikin Shekaru Biyu – Ribadu

August 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.