Akalla fasinjoji 17 aka kubutar a ranar Litinin bayan da wani jirgin ruwa ya kife daura da gadar ‘Third Mainland Bridge’ da ke Jihar Legas.
Jirgin na ‘yan kasuwa mallakar kamfanin Fazma ya kife ne, bayan ya taso daga tashar Ikorodu da misalin karfe 6:45 na safiyar ranar kafin ya isa zuwa yankin Ebute Ero.
- BUK Ta Kori Dalibai 27, Ta Dakatar Da 8 Kan Satar Jarabawa
- Za Mu Lashe Zaben Shugaban Kasa Da Tazarar Kuri’a Miliyan 3 —NNPP
A cikin sanarwar da Hukumar Agajin Gaggawa ta jihar, ta fitar ta bayyana cewa, jirgin ruwan ya kife ne da misalin karfe 7 na safiyar Litinin.
A cewar hukumar ta LASWA, an samu nasarar kubutar da daukacin fasinjojin tare da ma’aikatan jirgin.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp