• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutum 30 Sun Halaka Tare Da Sace Mutum 19 A Abuja

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Mutum 30 Sun Halaka Tare Da Sace Mutum 19 A Abuja
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Alhamis wasu masu garkuwa da mutane suka yi garkuwa da mutane 19 a yankin Bwari da ke cikin babban birnin tarayya Abuja.

Wannan lamarin na zuwa ne kasa da ‘yan kwanaki da mutuwar mutum 30 a sakamakon ruftawar masu hakar ma’adinai ta zama sababi a yankin Kuje da ke cikin birnin tarayya Abuja.

  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Abuja, Sun Yi Garkuwa Da Mutane 9
  • ‘Yan Bindiga Na Shirin Sake Kai Wa Jirgin Abuja Zuwa Kaduna Hari – DSS Ta Yi Gargadi

Ministan babban birnin tarayya l, Nyesom Wike, shi ne ya shaida hakan a lokacin da ke ganawa da shugabannin yankuna shida na Abuja.

Ministan wanda ya nuna mamakinsa da matakin, ya ce, zai gayyaci daraktan hukumar tsaron farin kaya na FCT, kwamishinan ‘yansanda don samun cikakken bayani game da garkuwar da kuma matakan da za a bi wajen kubutar da wadanda aka yi garkuwa da su din.

Wike ya bukaci shugabannin tsaro da suka samar da ‘yan sintiri a yankunan don su ke bibiyar ayyukan masu hakar ma’adinai, ya kara da cewa zai gana tare da takwaransa na ma’aikatar albarkatun kasa, Dele Alake, domin dakile hakar ma’adinai ta barauniyar hanya a birnin tarayya.

Labarai Masu Nasaba

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

Ministan Tsaro Ya Yi Gargadin Sake Dawowar Boko Haram Na Barazana Ga Nijeriya

Kazalika, karamar ministan birnin tarayya Abuja, Dakta Mariya Mahmoud, da babban sakataren hukumar bunkasa shiyyar birnin tarayya FCTA, Mr Olusade Adesola, sun nuna kwarin guiwarsu kan hukumar kula da birnin tarayya Abuja.

Da yake magana kan matsalolin da yankin Kwari ke fuskanta, shugaban yankin, Danladi Chiya, ya roki ministan da karamin ministan birnin tarayyar da su zo domin taimaka musu.

“Tun lokacin da muka ji labarin nadinku, muka ji dadi da fatan cewa matsaloli za su zo karshe.”

“Babban matsalarmu da ke fuskantar dukkanin yankunan shida na Abuja shi ne matsalar tsaro. Ko a yau (Alhamis) mutum 19 aka yi garkuwa da su a yankin Bwari. Yanzu nake samun labarin cewa mutanen yankin sun fi kwanaki shida a hannun masu garkuwa.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AbujaGarkuwaHakar Ma'adanaiHalakaKisaMutuwaWike
ShareTweetSendShare
Previous Post

Muna Bukatar Gudunmawar Addu’o’in ‘Yan Nijeriya Don Yaki Da Matsalar Tsaro — Badaru

Next Post

Gwamnan Gombe Ya Yaba Da Hukuncin Kotu Kan Tabbatar Da Nasarar Shugaba Tinubu

Related

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci
Rahotonni

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

9 minutes ago
Ministan Tsaro
Labarai

Ministan Tsaro Ya Yi Gargadin Sake Dawowar Boko Haram Na Barazana Ga Nijeriya

2 hours ago
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

3 hours ago
Ambaliyar Ruwa A Mokwa: Kauyuka 1,249 A Jihohi 30 Na Cikin Hadari — Gwamnatin Tarayya
Labarai

Ambaliyar Ruwa A Mokwa: Kauyuka 1,249 A Jihohi 30 Na Cikin Hadari — Gwamnatin Tarayya

4 hours ago
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi
Manyan Labarai

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

5 hours ago
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

5 hours ago
Next Post
Gwamnan Gombe Ya Yaba Da Hukuncin Kotu Kan Tabbatar Da Nasarar Shugaba Tinubu

Gwamnan Gombe Ya Yaba Da Hukuncin Kotu Kan Tabbatar Da Nasarar Shugaba Tinubu

LABARAI MASU NASABA

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

June 6, 2025
aure

Kar Ki Bari Naman Sallah Ya Kashe Miki Aure Yar’uwa

June 6, 2025
Ministan Tsaro

Ministan Tsaro Ya Yi Gargadin Sake Dawowar Boko Haram Na Barazana Ga Nijeriya

June 6, 2025
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

June 6, 2025
Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (3)

Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (3)

June 6, 2025
Ambaliyar Ruwa A Mokwa: Kauyuka 1,249 A Jihohi 30 Na Cikin Hadari — Gwamnatin Tarayya

Ambaliyar Ruwa A Mokwa: Kauyuka 1,249 A Jihohi 30 Na Cikin Hadari — Gwamnatin Tarayya

June 6, 2025
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

June 6, 2025
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

June 6, 2025
Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 6, 2025
Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.