• English
  • Business News
Friday, September 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutum 900 Kacal Aka Gano Cikin 15,000 Da Suka Bace A Arewa Maso Gabas – ICRC

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
ICRC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwamitin agaji ta ‘Red Cross’ na kasa da kasa (ICRC) ya bayyana cewar kusan fararen hula 900 ne kawai ana gano a shekarar 2022 daga cikin mutum 15,000 da aka bada rahoton bacewarsu sakamakon aikace-aikacen ‘yan ta’addan Boko Haram a jihar Borno da wasu sassan arewa maso gabas daga 2015 zuwa yanzu.

ICRC ta kara da cewa ta yi rijistan sama da mutum dubu 23,000 da suka bace a fadin Nijeriya sakamakon rikice-rikice.

  • Ba Za Mu Sake Lamuntar Kumbiya-kumbiyar Da Ake Tafkawa Wurin Fasfo Ba – Ministan Cikin Gida

Jagorar tawagar kariya da alaka da iyalai ta ICRC, Lillian Dube, ce ta shaida hakan a ranar Alhamis a bikin tunawa da mutanen da suka bace da ya gudana a Ngarannam, tsohowar sansanin ‘yan Boko Haram da ke Maiduguri, babbar birnin jihar Borno.

“A shekarar 2022, ICRC ta samu nasarar gano mutum 900 da suka bace tare da maidasu ga iyalansu.

“ICRC na shirya taron tunawa da wadanda suka bace ne domin nuna goyon baya ga iyalan mutanen da suka bace. Mun yi rijistan mutanen da suka bace su 15,000 a jihar Borno da jihohin da suke arewa maso gabas. Zai kuma iya kasancewa akwai wasu mutane da yawan gaske da su ma sun bace amma ba a samu shigar da su cikin rijista ba. Mutane da yawa a cikinsu an rabasu da iyalansu ne a 2015,” Dube ta shaida.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata

Shi kuma jami’in kiwon lafiyar kwakwalwa na ofishin ICRC a Maiduguri, Ahmed Kyari, ya ce, an ware ranar 30 ga watan Agustan 2023 domin tunawa da wadanda suka bace a rikice-rikice, ya kara da cewa, ta’addancin ‘yan Boko Haram ya shafi mutane da daman gaske a Borno.

Shi kuma a nasa jawabin, jagoran tawagar ICRC a Maiduguri, Mr Serge Zogg, ya mika sakon alhinunsu ga mutanen da aka raba da ‘yan uwa na tsawon lokaci.

Ta ce, ICRC ta kasance mai taimakon jama’a da agaji domin kare rayuka da mutuncin wadanda hare-hare ke shafa tare da sanar musu da tallafin da suke bukata.

Shettima Mohammed, wanda ya rasa ‘yar uwansa shekara 11 da suka wuce a rikicin Boko Haram, ya ce, har yanzu wannan rashin na sanya shi cikin dimuwa, ya ce, duk lokaci da aka bude kofar gidansa, gani yake kamar ‘yar uwansa ce ta dawo.

Ita ma Fatima Bunu Malik, da ta rasa kawunta a rikicin Boko Haram shekaru takwas da suka wuce a karamar hukumar Kukawa, ta misalta cewa matar kawun nata ta shiga matukar rashin hankali wacce ta rasu kwanakin baya, yanzu haka ‘ya’yansu guda uku duk sun zama marayu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Shin Salah Zai Iya Barin Liverpool Zuwa Gobe? 

Next Post

Xi Ya Yabawa Abotar Sin Da Amurka A Cikin Amsar Wasika Zuwa Ga Jikan Janar Joseph Stilwell

Related

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano
Manyan Labarai

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

33 minutes ago
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata
Labarai

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata

1 hour ago
Ahlul Faidhati Mai Diwani Group
Rahotonni

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

2 hours ago
Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur
Manyan Labarai

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur

2 hours ago
Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya
Manyan Labarai

Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya

3 hours ago
Nijeriya Na Shirin Samun Jarin Dala Biliyan 60 A Fannin Gas – Shugaban NNPCL
Manyan Labarai

Nijeriya Na Shirin Samun Jarin Dala Biliyan 60 A Fannin Gas – Shugaban NNPCL

5 hours ago
Next Post
Xi

Xi Ya Yabawa Abotar Sin Da Amurka A Cikin Amsar Wasika Zuwa Ga Jikan Janar Joseph Stilwell

LABARAI MASU NASABA

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

September 12, 2025
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata

September 12, 2025
Ahlul Faidhati Mai Diwani Group

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

September 12, 2025
Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur

September 12, 2025
Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya

Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya

September 12, 2025
Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack

Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack

September 12, 2025
Gwamnonin Arewa Sun Amince Da Kafa Ƴansandan Jihohi: Ko Hakan Zai Yi Tasiri Ga Sha’anin Tsaro?

Gwamnonin Arewa Sun Amince Da Kafa Ƴansandan Jihohi: Ko Hakan Zai Yi Tasiri Ga Sha’anin Tsaro?

September 12, 2025
Nijeriya Na Shirin Samun Jarin Dala Biliyan 60 A Fannin Gas – Shugaban NNPCL

Nijeriya Na Shirin Samun Jarin Dala Biliyan 60 A Fannin Gas – Shugaban NNPCL

September 12, 2025
Yadda Tinubu Ya Shawo Kan Gwamnonin Arewa Wajen Amincewa Da Kafa Ƴansandan Jihohi

Yadda Tinubu Ya Shawo Kan Gwamnonin Arewa Wajen Amincewa Da Kafa Ƴansandan Jihohi

September 12, 2025
Rashin Wutar Lantarki: Masana Sun Nuna Damuwa Kan Asarar Dala Biliyan 29 Da Ƙananan Masana’antu Ke Yi

Rashin Wutar Lantarki: Masana Sun Nuna Damuwa Kan Asarar Dala Biliyan 29 Da Ƙananan Masana’antu Ke Yi

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.