• English
  • Business News
Saturday, July 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutum 900 Kacal Aka Gano Cikin 15,000 Da Suka Bace A Arewa Maso Gabas – ICRC

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
ICRC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwamitin agaji ta ‘Red Cross’ na kasa da kasa (ICRC) ya bayyana cewar kusan fararen hula 900 ne kawai ana gano a shekarar 2022 daga cikin mutum 15,000 da aka bada rahoton bacewarsu sakamakon aikace-aikacen ‘yan ta’addan Boko Haram a jihar Borno da wasu sassan arewa maso gabas daga 2015 zuwa yanzu.

ICRC ta kara da cewa ta yi rijistan sama da mutum dubu 23,000 da suka bace a fadin Nijeriya sakamakon rikice-rikice.

  • Ba Za Mu Sake Lamuntar Kumbiya-kumbiyar Da Ake Tafkawa Wurin Fasfo Ba – Ministan Cikin Gida

Jagorar tawagar kariya da alaka da iyalai ta ICRC, Lillian Dube, ce ta shaida hakan a ranar Alhamis a bikin tunawa da mutanen da suka bace da ya gudana a Ngarannam, tsohowar sansanin ‘yan Boko Haram da ke Maiduguri, babbar birnin jihar Borno.

“A shekarar 2022, ICRC ta samu nasarar gano mutum 900 da suka bace tare da maidasu ga iyalansu.

“ICRC na shirya taron tunawa da wadanda suka bace ne domin nuna goyon baya ga iyalan mutanen da suka bace. Mun yi rijistan mutanen da suka bace su 15,000 a jihar Borno da jihohin da suke arewa maso gabas. Zai kuma iya kasancewa akwai wasu mutane da yawan gaske da su ma sun bace amma ba a samu shigar da su cikin rijista ba. Mutane da yawa a cikinsu an rabasu da iyalansu ne a 2015,” Dube ta shaida.

Labarai Masu Nasaba

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

Shi kuma jami’in kiwon lafiyar kwakwalwa na ofishin ICRC a Maiduguri, Ahmed Kyari, ya ce, an ware ranar 30 ga watan Agustan 2023 domin tunawa da wadanda suka bace a rikice-rikice, ya kara da cewa, ta’addancin ‘yan Boko Haram ya shafi mutane da daman gaske a Borno.

Shi kuma a nasa jawabin, jagoran tawagar ICRC a Maiduguri, Mr Serge Zogg, ya mika sakon alhinunsu ga mutanen da aka raba da ‘yan uwa na tsawon lokaci.

Ta ce, ICRC ta kasance mai taimakon jama’a da agaji domin kare rayuka da mutuncin wadanda hare-hare ke shafa tare da sanar musu da tallafin da suke bukata.

Shettima Mohammed, wanda ya rasa ‘yar uwansa shekara 11 da suka wuce a rikicin Boko Haram, ya ce, har yanzu wannan rashin na sanya shi cikin dimuwa, ya ce, duk lokaci da aka bude kofar gidansa, gani yake kamar ‘yar uwansa ce ta dawo.

Ita ma Fatima Bunu Malik, da ta rasa kawunta a rikicin Boko Haram shekaru takwas da suka wuce a karamar hukumar Kukawa, ta misalta cewa matar kawun nata ta shiga matukar rashin hankali wacce ta rasu kwanakin baya, yanzu haka ‘ya’yansu guda uku duk sun zama marayu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Shin Salah Zai Iya Barin Liverpool Zuwa Gobe? 

Next Post

Xi Ya Yabawa Abotar Sin Da Amurka A Cikin Amsar Wasika Zuwa Ga Jikan Janar Joseph Stilwell

Related

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai
Ra'ayi Riga

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

12 hours ago
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a
Rahotonni

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

13 hours ago
Illar Kakaba Wa Majalisa Ta 10 Shugabanni Ga Gwamnatin Tinubu – Dattawan Arewa
Labarai

Majalisar Tarayya Ta Karrama NPA Da Kyautar Gaskiya Da Riƙon Amana Ta 2025

15 hours ago
Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Mutum 2 Da AK-47 A Taraba

16 hours ago
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Labarai

Amurka Ta Rage Wa’adin Bizar ‘Yan Nijeriya Zuwa Wata Uku

17 hours ago
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna
Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna

18 hours ago
Next Post
Xi

Xi Ya Yabawa Abotar Sin Da Amurka A Cikin Amsar Wasika Zuwa Ga Jikan Janar Joseph Stilwell

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

July 12, 2025
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

July 11, 2025
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

July 11, 2025
Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

July 11, 2025
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

July 11, 2025
“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

July 11, 2025
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

July 11, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

July 11, 2025
Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

July 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.