ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutum 900 Kacal Aka Gano Cikin 15,000 Da Suka Bace A Arewa Maso Gabas – ICRC

by Khalid Idris Doya
3 years ago
ICRC

Kwamitin agaji ta ‘Red Cross’ na kasa da kasa (ICRC) ya bayyana cewar kusan fararen hula 900 ne kawai ana gano a shekarar 2022 daga cikin mutum 15,000 da aka bada rahoton bacewarsu sakamakon aikace-aikacen ‘yan ta’addan Boko Haram a jihar Borno da wasu sassan arewa maso gabas daga 2015 zuwa yanzu.

ICRC ta kara da cewa ta yi rijistan sama da mutum dubu 23,000 da suka bace a fadin Nijeriya sakamakon rikice-rikice.

  • Ba Za Mu Sake Lamuntar Kumbiya-kumbiyar Da Ake Tafkawa Wurin Fasfo Ba – Ministan Cikin Gida

Jagorar tawagar kariya da alaka da iyalai ta ICRC, Lillian Dube, ce ta shaida hakan a ranar Alhamis a bikin tunawa da mutanen da suka bace da ya gudana a Ngarannam, tsohowar sansanin ‘yan Boko Haram da ke Maiduguri, babbar birnin jihar Borno.

ADVERTISEMENT

“A shekarar 2022, ICRC ta samu nasarar gano mutum 900 da suka bace tare da maidasu ga iyalansu.

“ICRC na shirya taron tunawa da wadanda suka bace ne domin nuna goyon baya ga iyalan mutanen da suka bace. Mun yi rijistan mutanen da suka bace su 15,000 a jihar Borno da jihohin da suke arewa maso gabas. Zai kuma iya kasancewa akwai wasu mutane da yawan gaske da su ma sun bace amma ba a samu shigar da su cikin rijista ba. Mutane da yawa a cikinsu an rabasu da iyalansu ne a 2015,” Dube ta shaida.

LABARAI MASU NASABA

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Shi kuma jami’in kiwon lafiyar kwakwalwa na ofishin ICRC a Maiduguri, Ahmed Kyari, ya ce, an ware ranar 30 ga watan Agustan 2023 domin tunawa da wadanda suka bace a rikice-rikice, ya kara da cewa, ta’addancin ‘yan Boko Haram ya shafi mutane da daman gaske a Borno.

Shi kuma a nasa jawabin, jagoran tawagar ICRC a Maiduguri, Mr Serge Zogg, ya mika sakon alhinunsu ga mutanen da aka raba da ‘yan uwa na tsawon lokaci.

Ta ce, ICRC ta kasance mai taimakon jama’a da agaji domin kare rayuka da mutuncin wadanda hare-hare ke shafa tare da sanar musu da tallafin da suke bukata.

Shettima Mohammed, wanda ya rasa ‘yar uwansa shekara 11 da suka wuce a rikicin Boko Haram, ya ce, har yanzu wannan rashin na sanya shi cikin dimuwa, ya ce, duk lokaci da aka bude kofar gidansa, gani yake kamar ‘yar uwansa ce ta dawo.

Ita ma Fatima Bunu Malik, da ta rasa kawunta a rikicin Boko Haram shekaru takwas da suka wuce a karamar hukumar Kukawa, ta misalta cewa matar kawun nata ta shiga matukar rashin hankali wacce ta rasu kwanakin baya, yanzu haka ‘ya’yansu guda uku duk sun zama marayu.

ICRC
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ‘Yansanda Sun Cafke Tsoho Mai Shekara 70 Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 8 Fyaɗe A Bauchi

MASU ALAKA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Next Post
Xi

Xi Ya Yabawa Abotar Sin Da Amurka A Cikin Amsar Wasika Zuwa Ga Jikan Janar Joseph Stilwell

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.