• English
  • Business News
Tuesday, May 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Na Fi Rubuta Labarin Da Zai Nuna An Tsangwami Mutum – Zakiyya Dahir

by Bilkisu Tijjani
1 year ago
in Adabi
0
Zakiyya Dahir
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A tattaunawar shafin Adabi da marubuci ZAKIYYA M. DAHIR wadda aka fi sani da ZEE MD, ta bayyana wa masu karatu yadda ta sha gwagwarmayar fara rubutu da kuma irin rubutun da ta fi sha’awa wanda jigonsa yake kasancewa na tsangwamar mutum amma daga bisani kuma abin ya zama masa alheri. Akwai sauran abubuwa a cikin hirar tare da PRINCESS FATIMA ZAHRA MAZADU kamar haka:

Ko za ki fara da bayyana wa masu karatu cikakken sunanki tare da dan takaitaccen tarihinki?
Da farko dai sunana Zakiyya M. Dahir wacce aka fi sani da Zee MD. An haife ni a garin kano, nayi karatuna tun daga firamare har zuwa sakandare, daga nan na juya bangaren karatun islamiyya nayi saukar alkur’ani me girma tare da sauran littattafan Addini, daga nan kuma nayi aure.

Me ya ja hankalinki har ki ka fara rubutu?
A gaskiya abin da ya ja hankalina game da rubutu shi ne; ina son in isar da sakonnin da mutane za su amfana da shi, kuma Alhamdulillah nayi nasarar yin hakan.

Ya gwagwarmayar farawar ta kasance?
Alhamdulillah gwagwarmaya kam an sha ta sosai, don duk abin da za ka fara a rayuwa dole za ka fuskanci kalubale, musamman da farko tunda ba iyawa kayi ba, amman Alhamdulillah yanzu komai ya wuce.

Ya batun iyaye lokacin da ki ka fara sanar musu kina sha’awar fara rubutu, shin kin samu wani kalubale daga gare su ko kuwa?
A gaskiya ‘Yan uwana da iyayena da kuma jigona wato mijina, sun karfafa min gwuiwa akan rubutuna ban samu matsala dasu ba, koda yaushe tsakaninmu fatan alkairi ne da kuma addu’ar samun nassara.

Labarai Masu Nasaba

Marubutan Batsa Ku Ji Tsoron Allah -Emili

Dr. Maryam Yola Ta Zama Farfesa Mace Ta Farko Kan Magungunan Gargajiya Da Al’adun Hausa

Ya farkon fara rubutunki ya kasance?
Farkon fara rubutu na ban sha wahala ba saboda daman ina karatun littafi, sai dai ta bangaren yadda zan saita alkalamina wajen tantance harufan rubutu da kuma saka aya da alamar tambaya nasha wuya kafin na gano.

Kamar wanne bangare ki ka fi maida hankali akai wajen yin rubutun?
Na fi maida hankali akan rubuta labarin da zai nuna an tsangwami mutum, amman a karshe da ya yi hakuri sai hakurin ya yi masa amfani har ya zamo shi ne ake son a gani.

Daga lokacin da ki ka fara kawo i-yanzu kin rubuta labarai sun kai kamar guda nawa?
Daga lokacin dana fara rubutu zuwa yanzu na rubuta labarai sun kai goma, kuma ma sha Allah ba laifi sun samu karbuwa a zukatan Al’umma.

Ko za ki iya fadawa masu karatu sunayensu?
Na Rubuta littafai guda Tara ; Makircin cikin gida, ‘Yar kishiya, ‘Yar Hannu, Mawakiya, Ni Bora ce, Rayuwa Biyu, Nafi k’arfin Talaka, Atare muka taso, Bazawara ce, yanzu kuma ina rubuta ‘Zawarcin Aliya’

Cikin labarun da kika rubuta ko akwai wanda kika buga?
Har yanzu ban buga labari ba, sai dai in Allah ya nufa nan gaba ina sa ran bugawa.

Wanne ne ya zamo bakandamiyarki cikin rubutun da ki ka yi?
Duk littattafaina Ina sonsu, amman wanda ya zamo bakandamiya ta shi ne ‘Akwai Kura’.

Wanne labari ne rubutunsa ya fi baki wuya?
Littafin ‘Rayuwa Biyu’ gaskiya ya ban wuya dan sai da na ji kamar ma na hakura saboda wuya, sai kuma dai na jajirce har nayi nassarar kammalashi, shi ne a ciki littattafaina ya zo da sabon salo shiyasa na sha wuyar sa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Adon GariMa'aurataRayuwarsu 'yan mata
ShareTweetSendShare
Previous Post

Nijeriya Da Guinea Za Su Buga Wasan Sada Zumunta A Dubai

Next Post

Adadin Kudin Musaya Da Sin Ta Adana Ya Kai Dala Biliyan 3238 A Karshen Bara

Related

Marubutan Batsa Ku Ji Tsoron Allah -Emili
Adabi

Marubutan Batsa Ku Ji Tsoron Allah -Emili

3 weeks ago
Dr. Maryam Yola Ta Zama Farfesa Mace Ta Farko Kan Magungunan Gargajiya Da Al’adun Hausa
Al'adu

Dr. Maryam Yola Ta Zama Farfesa Mace Ta Farko Kan Magungunan Gargajiya Da Al’adun Hausa

4 months ago
Farfesa Zaynab Alkali: Mace Ta Farko Da Ta Zama Marubuciyar Littattafai Daga Arewacin Nijeriya
Adabi

Farfesa Zaynab Alkali: Mace Ta Farko Da Ta Zama Marubuciyar Littattafai Daga Arewacin Nijeriya

6 months ago
Na Fi Jin Dadin Rubutu In Na Gaji Tibis – Maryam Faruk
Adabi

Na Fi Jin Dadin Rubutu In Na Gaji Tibis – Maryam Faruk

6 months ago
Mahaifiyata Ce Ta Karfafe Ni Shiga Harkar Rubutu –Maryam Faruk
Adabi

Mahaifiyata Ce Ta Karfafe Ni Shiga Harkar Rubutu –Maryam Faruk

6 months ago
Yadda Malaminmu Na Hausa Ya Karfafa Min Kwarin Gwiwar Fara Rubutu – Salma Ahmad
Adabi

Yadda Malaminmu Na Hausa Ya Karfafa Min Kwarin Gwiwar Fara Rubutu – Salma Ahmad

8 months ago
Next Post
Adadin Kudin Musaya Da Sin Ta Adana Ya Kai Dala Biliyan 3238 A Karshen Bara

Adadin Kudin Musaya Da Sin Ta Adana Ya Kai Dala Biliyan 3238 A Karshen Bara

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Da Ake Iya Sarrafawa Daga Nesa

Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Da Ake Iya Sarrafawa Daga Nesa

May 12, 2025
Ƴan Ta’adda Sun Yi Garkuwa Da Tsohon Jami’in Shige Da Fice Da Fasinjoji 2 A Yobe

Ƴan Ta’adda Sun Yi Garkuwa Da Tsohon Jami’in Shige Da Fice Da Fasinjoji 2 A Yobe

May 12, 2025
He Lifeng Ya Gana Da Babbar Jami’ar WTO Ngozi Okonjo-Iweala

He Lifeng Ya Gana Da Babbar Jami’ar WTO Ngozi Okonjo-Iweala

May 12, 2025
Ma’aikatar Kasuwanci: Sanarwar Da Sin Da Amurka Suka Fitar Muhimmin Mataki Ne Na Warware Sabaninsu

Ma’aikatar Kasuwanci: Sanarwar Da Sin Da Amurka Suka Fitar Muhimmin Mataki Ne Na Warware Sabaninsu

May 12, 2025
Kaico: Wani Ƙani Ya Kashe Saurayin Yayarsa A Kano

Kaico: Wani Ƙani Ya Kashe Saurayin Yayarsa A Kano

May 12, 2025
Nazarin CGTN: Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Latin Amurka Na Kara Samun Karbuwa Tsakanin Jama’a

Nazarin CGTN: Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Latin Amurka Na Kara Samun Karbuwa Tsakanin Jama’a

May 12, 2025
Cutar Cholera Ta Ɓarke A Filato, Mutane 4 Sun Mutu

Cutar Cholera Ta Ɓarke A Filato, Mutane 4 Sun Mutu

May 12, 2025
Sanarwar Hadin Gwiwa Ta Bayan Taron Tattauna Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Sanarwar Hadin Gwiwa Ta Bayan Taron Tattauna Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

May 12, 2025
NNPP Ta Yi Asarar Ɗan Majalisa A Kano, Ya Koma APC

NNPP Ta Yi Asarar Ɗan Majalisa A Kano, Ya Koma APC

May 12, 2025
Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Matakan Cimma Nasarar Sassan Tsaron Kasa

Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Matakan Cimma Nasarar Sassan Tsaron Kasa

May 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.