• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Na Fi Rubuta Labarin Da Zai Nuna An Tsangwami Mutum – Zakiyya Dahir

byBilkisu Tijjani
2 years ago
Zakiyya Dahir

A tattaunawar shafin Adabi da marubuci ZAKIYYA M. DAHIR wadda aka fi sani da ZEE MD, ta bayyana wa masu karatu yadda ta sha gwagwarmayar fara rubutu da kuma irin rubutun da ta fi sha’awa wanda jigonsa yake kasancewa na tsangwamar mutum amma daga bisani kuma abin ya zama masa alheri. Akwai sauran abubuwa a cikin hirar tare da PRINCESS FATIMA ZAHRA MAZADU kamar haka:

Ko za ki fara da bayyana wa masu karatu cikakken sunanki tare da dan takaitaccen tarihinki?
Da farko dai sunana Zakiyya M. Dahir wacce aka fi sani da Zee MD. An haife ni a garin kano, nayi karatuna tun daga firamare har zuwa sakandare, daga nan na juya bangaren karatun islamiyya nayi saukar alkur’ani me girma tare da sauran littattafan Addini, daga nan kuma nayi aure.

Me ya ja hankalinki har ki ka fara rubutu?
A gaskiya abin da ya ja hankalina game da rubutu shi ne; ina son in isar da sakonnin da mutane za su amfana da shi, kuma Alhamdulillah nayi nasarar yin hakan.

Ya gwagwarmayar farawar ta kasance?
Alhamdulillah gwagwarmaya kam an sha ta sosai, don duk abin da za ka fara a rayuwa dole za ka fuskanci kalubale, musamman da farko tunda ba iyawa kayi ba, amman Alhamdulillah yanzu komai ya wuce.

Ya batun iyaye lokacin da ki ka fara sanar musu kina sha’awar fara rubutu, shin kin samu wani kalubale daga gare su ko kuwa?
A gaskiya ‘Yan uwana da iyayena da kuma jigona wato mijina, sun karfafa min gwuiwa akan rubutuna ban samu matsala dasu ba, koda yaushe tsakaninmu fatan alkairi ne da kuma addu’ar samun nassara.

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Littafin Baba Zube Na 5 (Gwamnati)

Marubutan Batsa Ku Ji Tsoron Allah -Emili

Ya farkon fara rubutunki ya kasance?
Farkon fara rubutu na ban sha wahala ba saboda daman ina karatun littafi, sai dai ta bangaren yadda zan saita alkalamina wajen tantance harufan rubutu da kuma saka aya da alamar tambaya nasha wuya kafin na gano.

Kamar wanne bangare ki ka fi maida hankali akai wajen yin rubutun?
Na fi maida hankali akan rubuta labarin da zai nuna an tsangwami mutum, amman a karshe da ya yi hakuri sai hakurin ya yi masa amfani har ya zamo shi ne ake son a gani.

Daga lokacin da ki ka fara kawo i-yanzu kin rubuta labarai sun kai kamar guda nawa?
Daga lokacin dana fara rubutu zuwa yanzu na rubuta labarai sun kai goma, kuma ma sha Allah ba laifi sun samu karbuwa a zukatan Al’umma.

Ko za ki iya fadawa masu karatu sunayensu?
Na Rubuta littafai guda Tara ; Makircin cikin gida, ‘Yar kishiya, ‘Yar Hannu, Mawakiya, Ni Bora ce, Rayuwa Biyu, Nafi k’arfin Talaka, Atare muka taso, Bazawara ce, yanzu kuma ina rubuta ‘Zawarcin Aliya’

Cikin labarun da kika rubuta ko akwai wanda kika buga?
Har yanzu ban buga labari ba, sai dai in Allah ya nufa nan gaba ina sa ran bugawa.

Wanne ne ya zamo bakandamiyarki cikin rubutun da ki ka yi?
Duk littattafaina Ina sonsu, amman wanda ya zamo bakandamiya ta shi ne ‘Akwai Kura’.

Wanne labari ne rubutunsa ya fi baki wuya?
Littafin ‘Rayuwa Biyu’ gaskiya ya ban wuya dan sai da na ji kamar ma na hakura saboda wuya, sai kuma dai na jajirce har nayi nassarar kammalashi, shi ne a ciki littattafaina ya zo da sabon salo shiyasa na sha wuyar sa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Nazari Kan Littafin Baba Zube Na 5 (Gwamnati)
Adabi

Nazari Kan Littafin Baba Zube Na 5 (Gwamnati)

September 26, 2025
Marubutan Batsa Ku Ji Tsoron Allah -Emili
Adabi

Marubutan Batsa Ku Ji Tsoron Allah -Emili

April 19, 2025
Dr. Maryam Yola Ta Zama Farfesa Mace Ta Farko Kan Magungunan Gargajiya Da Al’adun Hausa
Al'adu

Dr. Maryam Yola Ta Zama Farfesa Mace Ta Farko Kan Magungunan Gargajiya Da Al’adun Hausa

December 30, 2024
Next Post
Adadin Kudin Musaya Da Sin Ta Adana Ya Kai Dala Biliyan 3238 A Karshen Bara

Adadin Kudin Musaya Da Sin Ta Adana Ya Kai Dala Biliyan 3238 A Karshen Bara

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version