ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Na Fi Rubuta Labarin Da Zai Nuna An Tsangwami Mutum – Zakiyya Dahir

by Bilkisu Tijjani
2 years ago
Zakiyya Dahir

A tattaunawar shafin Adabi da marubuci ZAKIYYA M. DAHIR wadda aka fi sani da ZEE MD, ta bayyana wa masu karatu yadda ta sha gwagwarmayar fara rubutu da kuma irin rubutun da ta fi sha’awa wanda jigonsa yake kasancewa na tsangwamar mutum amma daga bisani kuma abin ya zama masa alheri. Akwai sauran abubuwa a cikin hirar tare da PRINCESS FATIMA ZAHRA MAZADU kamar haka:

Ko za ki fara da bayyana wa masu karatu cikakken sunanki tare da dan takaitaccen tarihinki?
Da farko dai sunana Zakiyya M. Dahir wacce aka fi sani da Zee MD. An haife ni a garin kano, nayi karatuna tun daga firamare har zuwa sakandare, daga nan na juya bangaren karatun islamiyya nayi saukar alkur’ani me girma tare da sauran littattafan Addini, daga nan kuma nayi aure.

Me ya ja hankalinki har ki ka fara rubutu?
A gaskiya abin da ya ja hankalina game da rubutu shi ne; ina son in isar da sakonnin da mutane za su amfana da shi, kuma Alhamdulillah nayi nasarar yin hakan.

ADVERTISEMENT

Ya gwagwarmayar farawar ta kasance?
Alhamdulillah gwagwarmaya kam an sha ta sosai, don duk abin da za ka fara a rayuwa dole za ka fuskanci kalubale, musamman da farko tunda ba iyawa kayi ba, amman Alhamdulillah yanzu komai ya wuce.

Ya batun iyaye lokacin da ki ka fara sanar musu kina sha’awar fara rubutu, shin kin samu wani kalubale daga gare su ko kuwa?
A gaskiya ‘Yan uwana da iyayena da kuma jigona wato mijina, sun karfafa min gwuiwa akan rubutuna ban samu matsala dasu ba, koda yaushe tsakaninmu fatan alkairi ne da kuma addu’ar samun nassara.

LABARAI MASU NASABA

Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta

EFCC Ta Kama Mutum 11 Masu Hakar Ma’adanai Ba Bisa Ka’ida Ba A Kwara

Ya farkon fara rubutunki ya kasance?
Farkon fara rubutu na ban sha wahala ba saboda daman ina karatun littafi, sai dai ta bangaren yadda zan saita alkalamina wajen tantance harufan rubutu da kuma saka aya da alamar tambaya nasha wuya kafin na gano.

Kamar wanne bangare ki ka fi maida hankali akai wajen yin rubutun?
Na fi maida hankali akan rubuta labarin da zai nuna an tsangwami mutum, amman a karshe da ya yi hakuri sai hakurin ya yi masa amfani har ya zamo shi ne ake son a gani.

Daga lokacin da ki ka fara kawo i-yanzu kin rubuta labarai sun kai kamar guda nawa?
Daga lokacin dana fara rubutu zuwa yanzu na rubuta labarai sun kai goma, kuma ma sha Allah ba laifi sun samu karbuwa a zukatan Al’umma.

Ko za ki iya fadawa masu karatu sunayensu?
Na Rubuta littafai guda Tara ; Makircin cikin gida, ‘Yar kishiya, ‘Yar Hannu, Mawakiya, Ni Bora ce, Rayuwa Biyu, Nafi k’arfin Talaka, Atare muka taso, Bazawara ce, yanzu kuma ina rubuta ‘Zawarcin Aliya’

Cikin labarun da kika rubuta ko akwai wanda kika buga?
Har yanzu ban buga labari ba, sai dai in Allah ya nufa nan gaba ina sa ran bugawa.

Wanne ne ya zamo bakandamiyarki cikin rubutun da ki ka yi?
Duk littattafaina Ina sonsu, amman wanda ya zamo bakandamiya ta shi ne ‘Akwai Kura’.

Wanne labari ne rubutunsa ya fi baki wuya?
Littafin ‘Rayuwa Biyu’ gaskiya ya ban wuya dan sai da na ji kamar ma na hakura saboda wuya, sai kuma dai na jajirce har nayi nassarar kammalashi, shi ne a ciki littattafaina ya zo da sabon salo shiyasa na sha wuyar sa.

Zakiyya Dahir
Bilkisu Tijjani
+ postsBio
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Yadda Ake Wainar Masara Da Miyar Yaji
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Hanyoyin Hada Humra Mai Kamshi
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Yadda Ake Miyar Margi Da Kifin Tarwad
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    A Matsayinki Na Mace, Kada Ki Yi Wasa Da Wadannan Abubuwa

MASU ALAKA

Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta
Adabi

Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta

May 31, 2026
Zambar Kudi: Kotu Ta Tasa Keyar Dillalin Gidaje Zuwa Gidan Kaso
Adabi

EFCC Ta Kama Mutum 11 Masu Hakar Ma’adanai Ba Bisa Ka’ida Ba A Kwara

February 6, 2026
CGI Babandede Mai Ritaya A Mizanin Kyawawan Halaye Da Kwazon Aiki
Adabi

CGI Babandede Mai Ritaya A Mizanin Kyawawan Halaye Da Kwazon Aiki

January 30, 2026
Next Post
Adadin Kudin Musaya Da Sin Ta Adana Ya Kai Dala Biliyan 3238 A Karshen Bara

Adadin Kudin Musaya Da Sin Ta Adana Ya Kai Dala Biliyan 3238 A Karshen Bara

LABARAI MASU NASABA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.