ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Na Fi Rubuta Labarin Da Zai Nuna An Tsangwami Mutum – Zakiyya Dahir

by Bilkisu Tijjani
2 years ago
Zakiyya Dahir

A tattaunawar shafin Adabi da marubuci ZAKIYYA M. DAHIR wadda aka fi sani da ZEE MD, ta bayyana wa masu karatu yadda ta sha gwagwarmayar fara rubutu da kuma irin rubutun da ta fi sha’awa wanda jigonsa yake kasancewa na tsangwamar mutum amma daga bisani kuma abin ya zama masa alheri. Akwai sauran abubuwa a cikin hirar tare da PRINCESS FATIMA ZAHRA MAZADU kamar haka:

Ko za ki fara da bayyana wa masu karatu cikakken sunanki tare da dan takaitaccen tarihinki?
Da farko dai sunana Zakiyya M. Dahir wacce aka fi sani da Zee MD. An haife ni a garin kano, nayi karatuna tun daga firamare har zuwa sakandare, daga nan na juya bangaren karatun islamiyya nayi saukar alkur’ani me girma tare da sauran littattafan Addini, daga nan kuma nayi aure.

Me ya ja hankalinki har ki ka fara rubutu?
A gaskiya abin da ya ja hankalina game da rubutu shi ne; ina son in isar da sakonnin da mutane za su amfana da shi, kuma Alhamdulillah nayi nasarar yin hakan.

ADVERTISEMENT

Ya gwagwarmayar farawar ta kasance?
Alhamdulillah gwagwarmaya kam an sha ta sosai, don duk abin da za ka fara a rayuwa dole za ka fuskanci kalubale, musamman da farko tunda ba iyawa kayi ba, amman Alhamdulillah yanzu komai ya wuce.

Ya batun iyaye lokacin da ki ka fara sanar musu kina sha’awar fara rubutu, shin kin samu wani kalubale daga gare su ko kuwa?
A gaskiya ‘Yan uwana da iyayena da kuma jigona wato mijina, sun karfafa min gwuiwa akan rubutuna ban samu matsala dasu ba, koda yaushe tsakaninmu fatan alkairi ne da kuma addu’ar samun nassara.

LABARAI MASU NASABA

Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta

EFCC Ta Kama Mutum 11 Masu Hakar Ma’adanai Ba Bisa Ka’ida Ba A Kwara

Ya farkon fara rubutunki ya kasance?
Farkon fara rubutu na ban sha wahala ba saboda daman ina karatun littafi, sai dai ta bangaren yadda zan saita alkalamina wajen tantance harufan rubutu da kuma saka aya da alamar tambaya nasha wuya kafin na gano.

Kamar wanne bangare ki ka fi maida hankali akai wajen yin rubutun?
Na fi maida hankali akan rubuta labarin da zai nuna an tsangwami mutum, amman a karshe da ya yi hakuri sai hakurin ya yi masa amfani har ya zamo shi ne ake son a gani.

Daga lokacin da ki ka fara kawo i-yanzu kin rubuta labarai sun kai kamar guda nawa?
Daga lokacin dana fara rubutu zuwa yanzu na rubuta labarai sun kai goma, kuma ma sha Allah ba laifi sun samu karbuwa a zukatan Al’umma.

Ko za ki iya fadawa masu karatu sunayensu?
Na Rubuta littafai guda Tara ; Makircin cikin gida, ‘Yar kishiya, ‘Yar Hannu, Mawakiya, Ni Bora ce, Rayuwa Biyu, Nafi k’arfin Talaka, Atare muka taso, Bazawara ce, yanzu kuma ina rubuta ‘Zawarcin Aliya’

Cikin labarun da kika rubuta ko akwai wanda kika buga?
Har yanzu ban buga labari ba, sai dai in Allah ya nufa nan gaba ina sa ran bugawa.

Wanne ne ya zamo bakandamiyarki cikin rubutun da ki ka yi?
Duk littattafaina Ina sonsu, amman wanda ya zamo bakandamiya ta shi ne ‘Akwai Kura’.

Wanne labari ne rubutunsa ya fi baki wuya?
Littafin ‘Rayuwa Biyu’ gaskiya ya ban wuya dan sai da na ji kamar ma na hakura saboda wuya, sai kuma dai na jajirce har nayi nassarar kammalashi, shi ne a ciki littattafaina ya zo da sabon salo shiyasa na sha wuyar sa.

Zakiyya Dahir
Bilkisu Tijjani
+ postsBio
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Nasihar Da Ya Dace Dukkan Iyaye Su Yi Wa ‘Yaƴansu Yayin  Aure?
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Abin Da Yake Kashe Matanmu Na Hausawa
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Kafin Ki Nemi Saki, Nemi Amsar Waɗannan Tambayoyi Da Kanki
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Ko Kin San… Cututtukan Da Man Ridi Ke Warkarwa?

MASU ALAKA

Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta
Adabi

Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta

May 31, 2026
Zambar Kudi: Kotu Ta Tasa Keyar Dillalin Gidaje Zuwa Gidan Kaso
Adabi

EFCC Ta Kama Mutum 11 Masu Hakar Ma’adanai Ba Bisa Ka’ida Ba A Kwara

February 6, 2026
CGI Babandede Mai Ritaya A Mizanin Kyawawan Halaye Da Kwazon Aiki
Adabi

CGI Babandede Mai Ritaya A Mizanin Kyawawan Halaye Da Kwazon Aiki

January 30, 2026
Next Post
Adadin Kudin Musaya Da Sin Ta Adana Ya Kai Dala Biliyan 3238 A Karshen Bara

Adadin Kudin Musaya Da Sin Ta Adana Ya Kai Dala Biliyan 3238 A Karshen Bara

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.