• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Na Samu Farin Ciki Sosai A Farkon Fara Rubutuna – Fauziyya

by Bilkisu Tijjani
1 year ago
in Adabi
0
Na Samu Farin Ciki Sosai A Farkon Fara Rubutuna – Fauziyya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shafin da ke zakulo muku fasihan marubuta manya da kanana. A yau ma shafin na tafe da fasihiyar marubuciyar littafin Hausa, wato FAUZIYYA USMAN. Inda ta bayyanawa masu karatu yadda ta tsinci kanta a fannin rubutu. Ga dai tattaunawar tare da FATIMA ZAHRA MAZADU Kamar haka:

Ya sunan Malamar?

Sunana Fauziya Usman

 

Ko za ki fadawa masu karatu dan takaitaccen tarihinki?

Labarai Masu Nasaba

Marubutan Batsa Ku Ji Tsoron Allah -Emili

Dr. Maryam Yola Ta Zama Farfesa Mace Ta Farko Kan Magungunan Gargajiya Da Al’adun Hausa

Ni ‘yar Jihar Zamfara ce ina zaune a garin Gusau, a nan na yi dukka karatu na kuma har yanzu ina cikinta.

 

Me ya ja hankalinki har ki ka fara rubutu?

To gaskiya ba zan ce ga wani abin da ya ja hankali na ba, kwatsam na samu kaina a cikin rubutun littafi.

 

Wanne irin labari ki ka fi maida hankali a kai wajen rubutawa?

Gaskiya ni ko ina, ina tabawa to ba wani wanda na fi maida hankali.

 

Ya farkon fara rubutun ya kasance?

Gaskiya na samu farin ciki sosai saboda ban samu wani kalubale ba.

 

Ya gwagwarmayar farawar ya kasance?

Gaskiya ba wata gwagwarmaya dana samu a kai.

 

Ya batun iyaye lokacin da ki ka fara sanar musu kina son fara rubutu, shin kin fuskanci wani kalubale daga gare su?

Abin shi ne ko da na fara rubutu na yi aure, sannan kuma mujina ya karfafamin tare da bani kwarin guiwa sosai.

 

Daga lokacin da ki ka fara, kawo iyanzu kin rubuta labari sun kai kamar guda nawa?

Gaskiya Alhamdulillah na rubuta littattafai da dama wadanda yawansu zai kai 30.

 

Wanne littafi ne ya zamo bakandamiyarki cikin littattafan da ki ka rubuta?

Muma ‘Ya’ya ne.

 

Wanne labari ne ya fi baki wahala lokacin da ki ke rubutawa, kuma me ya sa?

Da’iman muna tare, saboda yana tare da kunci wanda har sai da ya saka ni zubar da kwalla.

 

Cikin labarin da ki ka rubuta akwai wanda ki ka buga ko ki ke sa ran bugawa?

Ba wanda na buga amma da akwai wadanda nake son na buga in sha Allah.

 

Ko akwai wani kalubale da ki ka taba fuskanta game da rubutu ko masu karatu?

Eh! na samu kalubale a littafin Da’iman muna tare da burin iyayenmu shi ne namu.

 

Wanne irin Nasarori ki ka samu game da rubutu?

To Alhamdu lillah na samu nasarori sosai, musamman tarin masoyan da nake da su, ko yaushe suna yi min fatan alkhairi hakan yana yi min dad’i sosai.

 

Ya kika dauki rubutu a wajenka?

Hmm rubutu babban al’amari ne wanda yake da matukar girma sosai, kamar dai yanda yake al’kalami ya fi takobi tabbas wannan gaskiya ne

 

Mene ne burinki na gaba game da rubutu?

Ina da burin zama babba kuma shahararriyar marubuciya, wacce mutane da dama za su santa sannan kuma su yi alfahari da ita.

 

Ko akwai wadda ta taba bata miki rai game da rubutunki ko aka yaba?

Eh duka a na samu.

 

Wanne abu ki ke tunawa ki ke jin dadi game da rubutunki?

Masoyan da nake da su musamman masu yi min fatan alkhairi.

 

Bayan rubutu kina wata sana’ar ne?

Eh ina yin sana’a da dama.

 

Ya ki ke iya hada sana’arki da rubutu?

Ko wannen su yana da lokacin dana bashi.

 

Kamar wanne lokaci ki ka fi jin dadin yin rubutu?

Gaskiya nafi jin dadin rubutu da dare.

 

Me za ki ce da makaranta labaranki?

Tsakanina da su sai godiya da kuma fatan alkhairi.

 

Gaida mutum biyar.

Ina gaida masoyiya ta Fatima Mazadu, Maryam Usman (Maman Amira), Firdausi Usman (Ummu Sadik), Zainab ‘yar gata, Umar Dalha.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AdabiAl'adu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Jagoranci Kaddamar Da Shirin Aiwatar Da “Tsarin Kunming-Montreal” A Taron Sauyin Yanayi Na MDD A Hukumance

Next Post

Kalubalen Koya Wa ‘Yan Mata Tsafta A Tsakanin Iyaye

Related

Marubutan Batsa Ku Ji Tsoron Allah -Emili
Adabi

Marubutan Batsa Ku Ji Tsoron Allah -Emili

2 months ago
Dr. Maryam Yola Ta Zama Farfesa Mace Ta Farko Kan Magungunan Gargajiya Da Al’adun Hausa
Al'adu

Dr. Maryam Yola Ta Zama Farfesa Mace Ta Farko Kan Magungunan Gargajiya Da Al’adun Hausa

5 months ago
Farfesa Zaynab Alkali: Mace Ta Farko Da Ta Zama Marubuciyar Littattafai Daga Arewacin Nijeriya
Adabi

Farfesa Zaynab Alkali: Mace Ta Farko Da Ta Zama Marubuciyar Littattafai Daga Arewacin Nijeriya

7 months ago
Na Fi Jin Dadin Rubutu In Na Gaji Tibis – Maryam Faruk
Adabi

Na Fi Jin Dadin Rubutu In Na Gaji Tibis – Maryam Faruk

7 months ago
Mahaifiyata Ce Ta Karfafe Ni Shiga Harkar Rubutu –Maryam Faruk
Adabi

Mahaifiyata Ce Ta Karfafe Ni Shiga Harkar Rubutu –Maryam Faruk

7 months ago
Yadda Malaminmu Na Hausa Ya Karfafa Min Kwarin Gwiwar Fara Rubutu – Salma Ahmad
Adabi

Yadda Malaminmu Na Hausa Ya Karfafa Min Kwarin Gwiwar Fara Rubutu – Salma Ahmad

9 months ago
Next Post
Kalubalen Koya Wa ‘Yan Mata Tsafta A Tsakanin Iyaye

Kalubalen Koya Wa ‘Yan Mata Tsafta A Tsakanin Iyaye

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Fauziyya

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.