• English
  • Business News
Tuesday, July 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Na Yi Mamakin Ganin Takardar Tuɓe Rawanina Na Sarautar Mujaddadin Bauchi – Sanata Buba

by Muhammad
11 months ago
in Labarai
0
Na Yi Mamakin Ganin Takardar Tuɓe Rawanina Na Sarautar Mujaddadin Bauchi – Sanata Buba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sanata Shehu Buba, wanda shi ne Shugaban Kwamitun Majalisar Dattijai kan tsaro da tattara bayanan sirri, ya ce ya ci karo da wani labari mai ban mamaki kan wata wasika mai ɗauke da kwanan watan 14 ga watan Augustan 2024.

Sanatan ya ce takardar mai ɗauke da sakon cewa Majalisar Masarautar Bauchi ta warware rawaninsa daga Sarautar Mujaddadin Bauchi a sakamakon zargin cin mutunci ko zagin Gwamnan jihar Bauchi a yayin wani gangamin yakin neman zabe a jihar.

  • Masarautar Bauchi Ta Tuɓe Rawanin Sanata Kan Sukar Gwamna Bala
  • Rikicin Warware Rawanin Tsohon Wazirin Bauchi Na Ci Gaba Da Daukar Sabon Salo

Sanata Buba ya bayyana martaninsa cikin wata takarda da ya fitar ranar Alhamis 15, ga Augustan 2024 da aka rabawa manema labarai ta kuma yaɗu a shafukan sada zumunta na yanar gizo, Inda ya bayyana cewa; “Ina amfani da wannan dama don bayyana wa jama’a cewa tun lokacin da na shiga harkokin siyasa ba na bin wani tsari na cin zarafin kowa idan ban da suka mai ma’ana ba tare da cin mutunci ko zagin kowa ba, wannan matakin shi ne tsarin da nake bi da nufin samar da ingantacciyar al’umma”.

“A lokacin da na saurari kalaman Gwamna lau Bauchi, Bala Muhammad da ya yi akan Shugaba Tinubu sai na ga hakan ya zama wajibi a kai na da na kare shugaban kasar daga yunkurin da ake yi na ɓata masa suna da zubar kimarsa da ƙoƙarin cusa kiyayyarsa a zukatan al’umma.” Cewar Buba.

Sanata Shehu Buba ya ce wannan shi ne iya abun da ya yi a lokacin yakin neman zaben da APC ta yi da ya halarta a kwanannan.

Labarai Masu Nasaba

ASUU Ta Tsunduma Yajin Aiki A Faɗin Nijeriya

‘Yan Bindiga Sun Hallaka ‘Yan Sa-kai Sama Da 70 A Filato

Sanatan ya ce sai kwatsam ya ji maganganun Gwamna Bala Muhammad akan shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu, wanda kafafen yaɗa labaran ƙasar nan da dama suka rawaito, wan da ya ƙunshi fito da fito da zargi mara tushe da kuma kage, da amfani da kalamai da ka iya kawo barazana ta fuskar tsaro a ƙasa.

Sanatan ya kuma ƙara jaddada cewa zarge-zargen da Gwamna Bala Muhammad ya yi wa Shugaba Tinubu, kalamai ne na siyasa, ba su da tushe kuma ba su da wata cikakkiyar hujja da dalilai da za a dogara da su.

Sannan ya ce cikin kalamansa da ya yi ya musanta zargin da Gwamna Bala ya yi wa Gwamnatin Tinubu na rashin kula da aiki da Kare muradun al’ummar ƙasa. Tabbas ya ce ya zargi Gwamna Bala da aikata hakan.

Sanatan ya ce a jawabinsa da ya yi ya ce Gwamna Bala Muhammad ya karɓi Naira Biliyan144 daga asusun Gwamnatin Tarayya a Shekarar 2023 da kuma fiye da Naira Biliyan 47 daga watan Janairu zuwa yau, wanda ake sa ran a jumla ce za su kai Naira Biliyan 195 zuwa karshen wannan shekarar, na kima nemi bahasi akan cewa me Gwamnatin Bala Muhammad ta yi da wadannan makudan kudade.

Buba ya ce Shugaba Tinubu na yin iya bakin kokarinsa na ganin an samar da tsaro a faɗin Tarayyar Nijeriya da daidaita tattalin arziki da ganin an samu zaman lafiya tsakanin ‘yan ƙasa ba tare da samun rabuwar kai ba.

Buba ya ce shi kalamansa bai yi su da wata niyya ba face da kyayyakwar manufa da kare shugaban Tinubu.

A ƙarshe ya shawarci Majalisar Masarautar Bauchi da ta guji amfani da tunanin wasu, wanda hakan ka iya yi kawo cikasa wajen cimma manufofin masarautar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamna Bala MuhammadMasarautar BauchiSanata Buba Shehu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Jihohi Sun Kashe Naira Biliyan 139.92 Wajen Biyan Bashin Kasashen Ketare A Wata 6

Next Post

Laifukan Zabe Barazana Ne Ga Samun Sahihan Zabuka A Nijeriya – INEC

Related

ASUU Ta Tsunduma Yajin Aiki A Faɗin Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

ASUU Ta Tsunduma Yajin Aiki A Faɗin Nijeriya

2 hours ago
Rikicin Gonar Gado Ya Yi Ajalin Mutum Ɗaya, An Ƙone Gidaje A Filato
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Hallaka ‘Yan Sa-kai Sama Da 70 A Filato

2 hours ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

ADC: Tinubu Na Yunƙurin Raba Kawunan Masu Haɗaka Kafin Zaɓen 2027

3 hours ago
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa
Manyan Labarai

Nijeriya Ba Ta Da Sha’awar Yin Gwajin Makamin Nukiliya — Shettima

4 hours ago
Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC
Labarai

Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC

13 hours ago
NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19
Da ɗumi-ɗuminsa

NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

14 hours ago
Next Post
Inec

Laifukan Zabe Barazana Ne Ga Samun Sahihan Zabuka A Nijeriya – INEC

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Tsunduma Yajin Aiki A Faɗin Nijeriya

ASUU Ta Tsunduma Yajin Aiki A Faɗin Nijeriya

July 8, 2025
Rikicin Gonar Gado Ya Yi Ajalin Mutum Ɗaya, An Ƙone Gidaje A Filato

‘Yan Bindiga Sun Hallaka ‘Yan Sa-kai Sama Da 70 A Filato

July 8, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

ADC: Tinubu Na Yunƙurin Raba Kawunan Masu Haɗaka Kafin Zaɓen 2027

July 8, 2025
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Nijeriya Ba Ta Da Sha’awar Yin Gwajin Makamin Nukiliya — Shettima

July 8, 2025
Da Ɗumi-Ɗumi: Osimhen Ya Amince Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

Da Ɗumi-Ɗumi: Osimhen Ya Amince Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

July 7, 2025
Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

July 7, 2025
Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC

Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC

July 7, 2025
Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki

Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki

July 7, 2025
NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

July 7, 2025
Sin Ta Kafa Kungiyar Masana Masu Binciken Sararin Samaniya Mai Zurfi Ta Farko

Sin Ta Kafa Kungiyar Masana Masu Binciken Sararin Samaniya Mai Zurfi Ta Farko

July 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.